Editor

9513 Posts
‘Yan sanda sun yi musayar wuta da ɓarayin daji a Zamfara

‘Yan sanda sun yi musayar wuta da ɓarayin daji a Zamfara

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja A qarshen makon da ya gabata ne jami’an ‘yan sanda suka yi artabu da ‘yan bindiga a ƙauyen Gada da ke Ƙaramar Hukumar Bunguɗu a jihar Zamfara, inda aka kashe da dama daga cikin ‘yan bindigar, wasu da dama kuma suka gudu da harbin bindiga. ‘Yan bindigar ɗauke da muggan makamai sun hau babura da dama, inda suka mamaye al’ummar Gada, inda suka kashe mutanen yankin 8 tare da yin awon gaba da shanu da dama. Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara, ASP Yazid Abubakar, ya ce sun samu nasarar fatattakar ‘yan bindigar, kuma…
Read More
Gwamna Dauda da takwarorinsa na Arewa maso Yamma sun nemi tallafin AfDB don bunƙasa sha’anin noma da tsaro

Gwamna Dauda da takwarorinsa na Arewa maso Yamma sun nemi tallafin AfDB don bunƙasa sha’anin noma da tsaro

Daga BASHIR ISAH Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya buƙaci Bankin Bunƙasa Afirka (AfDB) da ya saka Jihar Zamfara cikin shirinsa na taimaka wa shiyyoyin harkokin noma (SAPZ) kashi na biyu. Gwamnan ya yi wannan kira ne a lokacin da yake gabatar da jawabi a wajen taron da gwamnonin shiyyar Arewa maso Yamma suka yi da Shugaban AfDB, Dr. Akinwunmi Adesina a ranar Asabar. SAPZ shiri ne mai manufar daƙile fitar kayan gona zuwa ƙetare, maimakon haka ya zamana ana sarrafa su a cikin gida. Sanarwar da Kakakin Gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta ce, Zamfara ba ta…
Read More
Mutane miliyan 11.2 ne ke ɗauke da ciwon siga a Nijeriya — Ƙungiya

Mutane miliyan 11.2 ne ke ɗauke da ciwon siga a Nijeriya — Ƙungiya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ƙungiyar masu fama da ciwon siga ta Nijeriya ta ce aƙalla 'yan Nijeriya miliyan 11.2 ne ke ɗauke da cutar a halin yanzu. Dr Alƙali Mohammed, shugaban ƙungiyar ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a Abuja a wani taron zagayowar ranar tunawa da cutar siga ta duniya ta 2023, WDD. WDD rana ce da Majalisar Ɗinkin Duniya ta keɓe domin jawo hankalin jama’a kan buƙatar ɗaukar matakan yaƙi da cutar. Taken bikin ranar na bana shine, “Samun kula ga masu ciwon siga.” Mohammed ya bayyana cewa daga cikin ‘yan Nijeriya miliyan 11.2 da…
Read More
Za mu tallafa wa ɗalibai da suka yi karatun lafiya da magunguna – Shugaban Ƙaramar Hukumar Kumbotso

Za mu tallafa wa ɗalibai da suka yi karatun lafiya da magunguna – Shugaban Ƙaramar Hukumar Kumbotso

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Shugaban Ƙaramar Hukumar Kumbotso, Hon. Hassan Garban Ƙauye Farawa ya ɗauki nauyin karatun ɗalibai guda 60 'yan asalin yankin a Jami'ar Ilimi ta Sa'adatu Rimi dake jihar Kano. Ya ce ɗaliban da aka ɗauki nauyin karatun nasu wani sauke nauyi ne da Allah ya ɗora masa da wajibi ne ya yi iya ƙoƙarinsa domin sauke nauyin. Ya taya ɗaliban da suka rabauta murna da jan hankalinsu akan su dage da karatu yanda zai amfanesu su kuma jakadu nagari ga ƙaramar hukumar Kumbotso a jami'ar domin duk abinda suka yi za a kalli 'yan Kumbotso ne…
Read More
Za mu haɗa kai da sarakunan gargajiya domin daƙile matsalar tsaro – Tinubu

Za mu haɗa kai da sarakunan gargajiya domin daƙile matsalar tsaro – Tinubu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, a ƙarshen mako ya ce gwamnatinsa za ta haɗa kai da sarakunan ƙasar nan domin tabbatar da ci gaba da kawo ƙarshen rashin tsaro. Tinubu ya bayyana haka ne a yayin bikin cika shekaru 70 da haihuwar Osemawe na masarautar Ondo, Oba Victor Kiladejo, wanda aka gudanar a Cocin Diocese of Ondo (Anglican Communion) Cathedral Church na St. Stephen a cikin birnin Ondo. Shugaban wanda ya samu wakilcin Ministan Harkokin Cikin Gida, Mista Olubunmi Tunji-Ojo, ya ce haɗin gwiwar ya zama wajibi domin zaman lafiya da kwanciyar hankali su karaɗe…
Read More
Gwamnan Bauchi ya kai bantensa a shari’ar Kotun Ɗaukaka Ƙara

Gwamnan Bauchi ya kai bantensa a shari’ar Kotun Ɗaukaka Ƙara

Daga BASHIR ISAH Kotun Ɗaukaka Ƙara mai zamanta a Abuja ta tabbatar da nasarar Bala Abdulkadir Mohammed a matsayin Gwamnan Jihar Bauchi. Hukumar INEC ce ta bayyana Mohammed a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan da ya gudana ran 18 ga Maris, inda daga bisani babban abokin hamayyarsa na Jam'iyyar APC, AVM Sadique Abubakar (rtd), ya ƙi amicewa da sakamakon zaɓen ya garzaya Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe. Duk da dai Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen ta yanke hukuncin Mohammed ne halastaccen zaɓaɓɓen gwamnan Bauchi, amma hakan bai hana Abubakar garazayawa Kotun Ɗaukaka Ƙara ba. A zaman da Kotun ta yi a…
Read More
Hukuncin Kotun Ɗaukaka Ƙara: Za mu haɗu a Kotun ƙoli – Abba

Hukuncin Kotun Ɗaukaka Ƙara: Za mu haɗu a Kotun ƙoli – Abba

Daga BASHIR ISAH A matsayin ɓangare na fafutukar da yake yi na ganin ya kare kujerarsa a matsayin Gwamnan Kano, Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya ce zai garzaya Kotun Ƙoli domin kuwa bai gamsu da hukuncin da Kotun Ɗaukaka Ƙara ta yanke na korar shi daga kan kujerarsa ba. A ranar Juma'a ce Kotun Ɗaukaka Ƙara ta bi sawun Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe wajen soke nasarar da Abba Kabir na jam’iyyar NNPP ya samu zaɓen gwamnan Kano da ya gudana a watan Maris da ya gabata, sannan ta ayyana ɗan takarar APC, Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin halastaccen zaɓaɓɓen Gwamnan…
Read More
Abin takaici ne yadda wasu alaramomi ke harkokin addini, inji Sarkin Misau 

Abin takaici ne yadda wasu alaramomi ke harkokin addini, inji Sarkin Misau 

Daga BAKURA MUHAMMAD a Bauchi Mai Martaba Sarkin Misau, Alhaji Ahmed Suleiman, ya bayyana takaicinsa bisa yadda ake kiran malamin tsangawa ko Islamiyya da alaramma, amma idan aka yi bibiyar iliminsa, sai a iske bai ma iya gudanar da ayyukansa na ibada da aka halatta masa, domin gudanar da su ba. Sarkin ya ce, "Abu ne na ban takaici matuƙa gaya, ka ga mutum ana ce da shi Alaramma, amma sai a iske yadda yake yin alwala ma akwai gyara ko kura-kurai a ciki, lamarin da ya kasance koma-baya wa sahihin ibadojin mutum da rayuwar sa." Sarkin na Misau sai…
Read More
‘Yan sanda sun halaka ƙasurgumin ɗan bindiga a Katsina

‘Yan sanda sun halaka ƙasurgumin ɗan bindiga a Katsina

Daga UMAR GARBA a Katsina Rundunar 'yan sanda a Jihar Katsina ta bayyana cewar ta samu nasarar hallaka wani ƙasurgumin varawon daji mai suna Nazifi Ibrahim. Rundunar ta kuma ƙwato tarin alburusai da wasu makamai a yayin fafatawa da ta wakana tsakanin su da wata tawagar masu garkuwa da mutane, a Ƙaramar Hukumar Faskari dake jihar ta Katsina. Kakakin rundunar, ASP Abubakar Aliyu ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar game da yaƙi da 'yan ta'addan daji a jihar. A cewar sanarwar, a ranar 11 ga watan Nuwamba, 2023 rundunar ta samu bayanai da ke nuni…
Read More
Majalisar Wakilai ta fusata da shugabannin tsaro kan bijire wa gayyatarta

Majalisar Wakilai ta fusata da shugabannin tsaro kan bijire wa gayyatarta

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Majalisar Wakilai ta fusata kan rashin halartar hafsoshin tsaro da Sufeto Janar na ‘yan sanda, Kayode Egbetokun, a wani zama na mu’amala da aka shirya gudanarwa a jiya Alhamis yayin zaman majalisar. A maimakon haka dai shugabannin tsaro sun tura wakilai. A makon da ya gabata ne dai majalisar ta shirya muhawara a sassa daban-daban da shugabannin tsaro yayin da take shirin yi da sauran sassan ƙasar. Biyo bayan wani tanadi da kundin tsarin mulki ya bayar na mataimakin shugaban majalisar, Benjamin Kalu, majalisar ta ƙi amincewa da wakilcin shugabannin tsaro, maimakon haka ta…
Read More