Editor

9513 Posts
Ubangiji ya gaya min kotun sama za ta tabbatar wa Abba mulkin Kano, inji limamin coci

Ubangiji ya gaya min kotun sama za ta tabbatar wa Abba mulkin Kano, inji limamin coci

Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Shugaban cocin Wisdom Church of Christ International, Prophet Bisi Olujobi, ya bayyana cewa, Ubangijinsa ya sanar da shi cewa, Gwamnan Jihar Kano mai ci, Abba Kabir Yusuf (Abba Gida-gida), ya samu tagomashi a kotun sama, inda za ta rushe hukuncin baya na Kotun Zaɓen Gwamnan Jihar Kano na 2023, wacce ta sauke shi daga mulki kuma ta ɗora ɗan takarar gwamna na babbar jam’iyyar adawa a jihar, Nasiru Yusuf Gawuna. Prophet Olujobi ya bayyana hakan ne a a jiya Alhamis a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai, yana mai cewa, hukuncin…
Read More
Ruɗani ya mamaye hukuncin kotun zaɓen Gwamnan Kaduna

Ruɗani ya mamaye hukuncin kotun zaɓen Gwamnan Kaduna

*Shugaban Kotun ya kori ƙarar*Alqalai biyu sun nemi yin tutsu?*Gwamna Sani ya yaba wa Ashiru Kudan*PDP ta kasa gamsuwa Daga MAHDI M. MUHAMMAD Daga dukkan alamu hukuncin da kotun sauraron ƙarar zaɓen kujerar Gwamnan Jihar Kaduna ta yanke ya jefa mutane da dama cikin ruɗani, inda da fari aka bayar da rahotannin da ke nuni da cewa, kotun ta ayyana zaɓen a matsayin wanda bai kammala ba (wato inconclusive), to amma jim kaɗan bayan hakan sai kuma sababbin rahotanni suka nuna cewa, hukuncin yana magana ne akan tabbatar da Gwamna Uba Sani na Jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe…
Read More
Yau Tinubu zai yi wa ‘yan ƙasa jawabi

Yau Tinubu zai yi wa ‘yan ƙasa jawabi

Yau Lahadi ake sa ran Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai yi wa 'yan ƙasa jawabi bayan dawowa daga taron da ya halarta a Amurka. Taron shi ne karo na 78 da Majalisar Ɗinkin Duniya ta shirya wanda ya gudana a birnin New York. Bayan kammala taron ne Shugaba Tinubu ya ziyarci Paris da Faransa don taƙaitaccen hutu, in ji wata majiya. Tinubu ya iso gida ne sa'o'i kafin Ranar Samun 'Yancin Kan Nijeriya karo na 63, sannan kawana huɗu gabanin tsunduma yajin aikin da Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya da takwarorinta suka shirya. Da misalin ƙarfe 7:00am na wannan safiya…
Read More
Gwamna Bala ya ƙaddamar da kwamitin farfaɗo da ilimin boko a Bauchi

Gwamna Bala ya ƙaddamar da kwamitin farfaɗo da ilimin boko a Bauchi

Daga BAKURA MUHAMMAD a Bauchi Gwamna Bala Abdulqadir Mohammed na Bauchi ya danganta faɗuwar darajar ilimi a jihar, musamman ma ilimin firamare ga riƙon sakainar kashi da malaman makarantu suka yi wa koyarwa, haɗi da rashin bibiyar ayyukansu, rashin lura da lamurran koyo da koyarwa na yau da kullum, haɗi da rashin kan gado na malamai. Ire-iren waɗannan malamai, inji gwamnan, yakan kasance sun karɓi bashin baburan hawa ne domin yin sana'ar acava, da suke biyan waɗannan basussukan a tsintsinke wata-wata, lamarin da ya tilasta masu yin gararambar acava a kowace rana ta duniya, yayin da suka munafirci sana'ar su…
Read More
RTEAN ta horar da mambobinta kan dabarun shugabanci

RTEAN ta horar da mambobinta kan dabarun shugabanci

Ƙungiyar masu motocin safa ta Nijeriya (RTEAN) ta sha alwashin inganta fannin sufuri ta hanyar daƙile duk wani nau'in dabanci da ake fuskanta a tashoshin mota a sassan ƙasa. Shugaban RTEAN na ƙasa, Musa Maitakobi ne ya bayyana haka jim kaɗan bayan miƙa shahadar kammala samun horo na musamman game da shugabanci ga mambobin ƙungiyar su 17 a Jos, babban birnin Jihar Filato. Yayin taron, shi ma shugaban RTEAN ɗin, an karrama shi da lambar yabo ta bajinta, wato "Nigeria Silent Heroes Award (NSHA)". Shugaban ya ce kundin tsarin mulkin RTEAN ba yarda da dabanci a harkokin ƙungiyar ba, don…
Read More
Sarkin Borin Kabi ya zama Garkuwan masu maganin gargajiya na ƙasa

Sarkin Borin Kabi ya zama Garkuwan masu maganin gargajiya na ƙasa

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Haɗaɗɗiyar ƙungiyar masu bayar da maganin gargajiya ta ƙasa ta zaɓi Yusuf Abubakar a matsayin Garkuwan masu maganin gargajiya na ƙasa. Tawagar ta masu maganin gargajiya ta ƙasa da ta reshen jihar Kebbi ta iso fadar Mai Martaba Sarkin Kabin Argungu Alhaji Sama'ila Muhammadu Mera a ƙarƙashin jagoranacin Malam Bala Hassan inda suka tabbatar wa Masarautar Sarkin Kabin Argungu da cewa wannan zaɓen Allah ne, sun zaɓe shi ne tun daga mataki na ƙasa ba tare da wata jayayya ba saboda la'akari da irin rawar da ya ke takawa a wannan ɓangaren. Da ya ke…
Read More
Masu zanga-zanga sun garƙame Ministan Ayyuka a ofishinsa

Masu zanga-zanga sun garƙame Ministan Ayyuka a ofishinsa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wasu ma’aikatan da suka yi zanga-zanga sun kulle Ministan Ayyuka da Gidaje na Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, Mista Dave Umahi, a cikin ofishinsa da ke Abuja. An ce ministan ya hana ma’aikatan da suka zo aiki a makare samun damar shiga ma’aikatar. ’Yan ƙungiyar da suka hada da ma’aikatar gidaje da ayyuka sun yanke shawarar kulle ma’aikatar, tare da hana shiga da fita da kuma hana ministan fita daga ofishin. Sun kuma yi ikirarin cewa ya hana injiniyoyi da daraktoci yin aikinsu, kuma tun bayan naɗa shi ya ke karya ƙa’idojin aikin gwamnati, ta hanyar…
Read More
Sanatocin Kebbi sun gana da shugabannin sojoji

Sanatocin Kebbi sun gana da shugabannin sojoji

Daga JAMIL GULMA a Kebbi  Sanatoci daga jihar Kebbi da suka haɗa da Sanata Yahaya Abubakar Abddullahi na gundumar mazaɓar Kebbi ta Arewa da Sanata Garba Musa Maidoki na mazaɓar Kebbi ta Kudu sun gana da shugabannin sojoji dangane da matsalar tsaro da ke addabar waɗansu sassan jihar. Sanata mai wakiltar mazaɓar Kebbi ta Arewa Dr Yahaya Abdullahi ya jagoranci sanatocin jihar Kebbi a ofishin shugaban samar da tsaro na ƙasa Manjo Janar Christopher. Sanata Yahaya Abdullahi ya ce wannan ziyarar tana da alaƙa da rashin tsaro da ke addabar jihar Kebbi musamman yankin gundumar mazaɓar Kebbi ta Kudu don…
Read More
Nijeriya ta rasa damar karɓar baƙoncin gasar kofin Afrika ta 2027

Nijeriya ta rasa damar karɓar baƙoncin gasar kofin Afrika ta 2027

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Nijeriya ta rasa damar karɓar baƙoncin gasar kofin Afrika, bayan da aka bayyana sunan ƙasashen Kenya da Uganda da kuma Tanzania a matsayin ƙasashe uku da za su yi tarayya wajen karɓar baƙoncin gasar ta 2027. Gasar ta 2027 za ta zama karon farko da za ta gudana a gabashin Afrika tun bayan shekarar 1976 lokacin da Habasha ta karɓi baƙoncinta. A ɓangare guda makamanciyar gasar da za ta gudana a shekarar 2025 an mika damar ɗaukar nauyinta ga a Moroko bayan da Algeria da Zambia suka janye. Tun farko Nijeriya da Benin suka nemi yin…
Read More