Editor

9513 Posts
Mai yiwuwa NLC ta dakatar da shirinta na shiga yajin aiki

Mai yiwuwa NLC ta dakatar da shirinta na shiga yajin aiki

Da alama ƙungiyoyin jwadago na NLC da TUC ba za su shiga yajin aikin da suka yi wa shirya domin ba da zarafin ci gaba da tattauna game da batun aiwatar da yarjejeniyon da suka cimma da ɓangaren gwamnati. Bayanin haka na ƙunshe ne cikin sanarwa bayan taron da Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya fitar a ranar Lahadi. Da yammacin Lahadin da ta gabata Gwamnatin Tarayya ta yi zama na musamman da jagororin ƙungiyoyin ƙwadago domin tattauna mafita dangane da yajin aikin da ƙungiyoyin suka ƙuduri aniya. Yayin zaman, gwamnati ta amince a kan za…
Read More
Tinubu ya faɗaɗa shirin ƙarin albashi na N25,000 zuwa ga dukkan ma’aikata

Tinubu ya faɗaɗa shirin ƙarin albashi na N25,000 zuwa ga dukkan ma’aikata

Gwamnatin Tarayya ta faɗaɗa aniyarta ta ƙarin albashi da N25,000 ya shafi dukkan rukunin ma'aikata Shugaban Ma'aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila, shi ne ya bayyana haka yayin taron da suka yi da ƙungiyoyin ƙwadago da yammacin Lahadi. Da fari, ƙarin albashin da gwamnatin ta ce za ta yi ya keɓanta ne ga ƙananan ma'aikata kamar yadda aka ji Shugaba Bola Tinubu ya furta a jawabinsa ga 'yan ƙasa a ranar bikin zagayowar ranar samun 'yancin kan ƙasa. Tinubu ya ɗauki matakin yi wa ma'aikata ƙarin albashin ne domin rage musu raɗaɗin cire tallafin mai da kuma daƙile yunƙurin tafiya…
Read More
Tallafin rage raɗaɗi: SERAP ta maka gwamnoni a kotu kan tallafin N72bn

Tallafin rage raɗaɗi: SERAP ta maka gwamnoni a kotu kan tallafin N72bn

Ƙungiyar nan mai rajin a yi aiki da gaskiya da aka fi sani da SERAP a taƙaice, na zargin gwamnonin jihohi 36 kan rashin bada cikakken bayani game da yadda suka sarrafa Naira biliyan 72 da aka ba su a matsayin tallafin rage raɗaɗin cire tallafn fetur da gwamnati ta yi. Cikin sanarwar da ta fitar a ranar Lahadi ta bakin Daraktanta, Kolawole Oluwadare, ƙungiyar ta ce ta shigar da ƙara a kan gwamnonin, tare da neman cikakken bayani daga gare su game da waɗanda aka tsara su ci gajiyar shirin da kuma kayayyakin da suka saya da kuɗin da…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnatin Tarayya na ganawa da Ƙungiyar Ƙwadago

Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnatin Tarayya na ganawa da Ƙungiyar Ƙwadago

A ƙoƙarin da take yi don hana Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Ƙwadago shiga yajin aikin da ta ƙudiri aniya, Gwamnatin Tarayya na can tana tattaunawa da shugabannin ƙungiyar a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja da yammacin wannan Asabar. Ya zuwa haɗa wannan labarin, majiyarmu ta ce an hango wasu fitattun jagororin ƙungiyar na shiga wurin taron, ciki har da Shugaban NLC na Ƙasa, Joe Ajaero da Sakataren Ƙungiyar na Ƙasa, Emma Ugboaja da Babban Sakataren TUC, Nuhu Toro da sauransu. Wakilan gwamnati a wajen taron sun haɗa da Shugaban Ma'aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajiabiamila, ministocin ƙwadago, Simon Lalong da Nkeiruka…
Read More
Buhari ya taya ‘yan Nijeriya murnar zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

Buhari ya taya ‘yan Nijeriya murnar zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

Daga UMAR GARBA a Katsina Tsohon Shugaban Ƙasar Nijeriya, Muhammadu Buhari, ya taya ɗaukacin 'yan Nijeriya murnar zagayowar Ranar Samun 'Yancin Kai. Kazalika, Buhari ya taya Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu murnar cikar Nijeriya shekara 63 da samun 'yan cin kai. "A dai dai lokacin da ƙasar nan ke bikin samun 'yan kai, ina miƙa jinjinata ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu tare da al'umar Nijeriya," inji shi. Buhari ya bayyana haka ne cikin wata sanarwa da kakakinsa, Malam Garba Shehu, ya fitar. "Tsawon shekaru 63, Nijeriya na ci gaba da zaburar da sauran ƙasashen nahiyar Afrika ta hanyar ƙirƙire-ƙirƙire da…
Read More
Ranar Samun ‘Yancin Kai: Cikakken Jawabin Shugaba Tinubu

Ranar Samun ‘Yancin Kai: Cikakken Jawabin Shugaba Tinubu

Jawabin mai girma, Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, GCRFR, kuma Babban Kwamandan Askarawan Nijeriya a cikar Jamhuriyar Tarayyar Nijeriya shekaru 63 da samun ‘yancin kai, ranar Lahadi, 1 ga Oktoba, 2023 ‘Yan uwana ‘yan Najeriya, Ina farin cikin yi muku jawabi a yau, ranar cikar ƙasarmu shekaru 63 da samun ‘yancin kai, a matsayina na shugaban ƙasarmu mai albarka, kuma zallar ɗan uwanku ɗan Nijeriya. A wannan rana mai muhimmanci mai cike da fatan alheri, muna jinjina ga iyayenmu da suka kafa Nijeriya, mazansu da matansu. Ba don su ba, da ba a samu ƙasar Nijeriya ba. Gwagwarmayarsu, sadaukarwarsu, da…
Read More
An kashe ɗalibin jami’a saboda budurwa a Katsina

An kashe ɗalibin jami’a saboda budurwa a Katsina

Daga UMAR GARBA a Katsina Wasu da ake zargin ɗalibai ne sun kashe abokin karatunsu, Abubakar Nasir Barda, a jami'ar Gwamnatin Tarayya dake Dutsinma ta jihar Katsina. Ɗalibin ya gamu da ajalinsa a hannun 'yan uwansa ɗalibai bayan da suka lakaɗa masa duka, a dalilin yi wa wata ɗaliba mace magana a jami'ar wadda ake kyautata zaton budurwar ɗaya daga cikin ɗaliban da suka yi aika aikar ne. Kakakin rundunar 'yan sanda ta jihar Katsina, ASP Sadiq Abubakar, ya tabbatar da faruwar lamarin cikin wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai. Jami'in ya bayyana cewar, an kama mutane 6…
Read More
Ranar Samun ‘Yancin Kan Ƙasa: Tinubu ya yi wa ma’aikata ƙarin albashi na wucin-gadi

Ranar Samun ‘Yancin Kan Ƙasa: Tinubu ya yi wa ma’aikata ƙarin albashi na wucin-gadi

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana ƙarin albashi ga ma'aikatan gwamnati don rage musu raɗaɗin cire tallafin mai. Ya sanar da hakan ne a jawabinsa da ya yi wa 'yan ƙasa da safiyar Lahadi albarkacin Ranar Samun 'Yancin Kan Ƙasa, 1 ga Oktoba, 2023. Game da ƙarin, Tinubu ya ce ƙaramin ma'aikaci zai samu ƙarin N25,000 a albashinsa har na tsawon wata shida. Wannan na nufin ma'aikacin gwamnatin tarayya da ke karɓar albashi N30,000, yanzu N55,000 zai riƙa karɓa har na tsawon wata shida. Da alama dai ƙarin albashin na wucin gadi ne, kuma Shugaban bai yi ƙarin haske…
Read More
Cutar Mashaƙo: Kano ta samu tallafin alluran rigakafi miliyan huɗu daga UNICEF

Cutar Mashaƙo: Kano ta samu tallafin alluran rigakafi miliyan huɗu daga UNICEF

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Asusun Kula da Ƙananan Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF) ya ba wa Kano da sauran jihohi alluran riga-kafin cutar Mashaƙo wadda aka fi sani da Diphtheria guda miliyan 9.3. Daga cikin adadin da hukumar ta ba wa jihohin da aka samu vullar, UNICEF ta tura wa Jihar Kano alluran riga-kafin guda miliyan huɗu, a matsayin Kano na jihar da cutar ta fi ƙamari. Wakilin UNICEF, Dokta Rownak Khan, Sauran jihohin da za su amfana da tallafin alluran riga-kafin na UNICEF su ne Bauchi, Borno, Yobe, Katsina, Kaduna da kuma Jigawa. Hukumar ta ƙara…
Read More
Ana zargin Barcelona da bai wa alƙalan wasa cin hanci

Ana zargin Barcelona da bai wa alƙalan wasa cin hanci

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ana zargin Barcelona ta biyan alƙalan wasa Yuro miliyan 8.4 don a riqa yi mata alfarma a wasanni ’Yan sandan Sifaniya sun kai samame hedikwatar alƙalan wasan ƙasar a wani ɓangare na binciken zargin cin hanci da ake yi wa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barcelona. Barcelona na fuskantar zargin cin hanci kan wasu kuɗaɗe da ta tura wa Jose Maria Enriquez Negreira, wani tsohon mataimakin shugaban kwamitin alƙalan wasan, don a riƙa yi musu alfarma a wasanninsu. Barcelona ta musanta zargin kuma ba a kama kowa ba a lokacin samamen a birnin Madrid. Ba a kai…
Read More