Editor

9513 Posts
DSS sun cafke budurwar da ta yi wa Shettima da Gawuna barazanar ƙunar baƙin-wake

DSS sun cafke budurwar da ta yi wa Shettima da Gawuna barazanar ƙunar baƙin-wake

Jami'an DSS a Kano sun cafke Fiddausi Ahmadu, 'yar shekara 23, bayan da ta yi barazanar ƙunar baƙin-wake a kan waɗanda ta ce suna da hannu a nasarar da Jam'iyyar APC ta samu a shari'ar zaɓen gwamnan Kano a Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe. Majiya mai tsushe ta tabbatar wa jaridar News Point Nigeria da batun kama budurwar da DSS ta yi da safiyar Talata. Majiyar ta ce Fiddausi na iƙirarin taya Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusu da jam'iyyarsa ta NNPP faɗa ne kamar yadda aka gani a cikin wani faifan bidiyon da aka yaɗa. An ji Fiddausi a cikin bidiyon…
Read More
Tarihin juyin mulkin soja na farko a Nijeriya

Tarihin juyin mulkin soja na farko a Nijeriya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Daga ranar 15 zuwa 16 ga watan Janairun shekarar 1966, wasu ƙananan hafsoshin soja masu muƙaman manjo sun aiwatar da juyin mulkin soja na farko wanda suka fara kitsawa tun a watan Agustar shekarar 1965. Waɗannan ƙananan hafsoshin soja, sun yi ikirarin cewa sun shirya juyin mulkin ne a saboda a cewarsu, shugabannin da ke jagorancin ƙasar sun nuna zarmiya, inda suka ce ministocin gwamnati suna sace kuɗaɗen baitul-mali domin amfaninsu. Sai dai kuma a wani ɓangare, akwai masu ikirarin cewa wannan juyin mulki na ƙabilanci ne a saboda daga cikin sojoji 8 da suka ƙulla…
Read More
Ƙungiyoyin ƙwadago sun jinginar da aniyar shiga yajin aiki, yayin da ƙarin albashi na N35,000 zai fara aiki daga Satumba

Ƙungiyoyin ƙwadago sun jinginar da aniyar shiga yajin aiki, yayin da ƙarin albashi na N35,000 zai fara aiki daga Satumba

Ƙungiyar ƙwadago NLC da takwararta TUC, sun jinginar da aniyarsu ta shiga yajin aikin sai-baba-ta-gani na tsawon wata guda. Hakan na ƙunshe ne cikin takardar yarjejeniyar da aka cimma tsakanin ɓangaren gwamnatin tarayya da ƙungiyoyin a taron da suka yi ranar Litinin. Yayin zaman nasu, Gwamnatin Tarayya ta yi tayin ƙarin albashi na N35,000 amma ga ma'aikatanta kaɗai wanda zai fara aiki daga watan Satumba zuwa lokacin da za a rataɓɓa hannu kan sabon mafi ƙarancin albashi. Tuni dai sugabannin ƙungiyar Maritime Workers Union of Nigeria (MWUN) suka umarci mambobinsu da su koma bakin a tashoshin jirgin ruwan da ke…
Read More
Dangut ya zama Shugaban WAEC na ƙasa

Dangut ya zama Shugaban WAEC na ƙasa

An naɗa Dokta Amos Dangut a matsayin sabon Shugaban Hukumar Shirya Jarrabawar Kammala Sakandare a Afrika ta Yamma (WAEC) a Nijeriya. Kafin naɗin nasa, Dangut shi ne Mataimakin Rijistara na WAEC na ƙasa. Naɗin nasa ya biyo bayan ƙarewar wa'adin aikin Mr Patrick Areghan a matsayin shugaban hukumar na ƙasa. Bayanin naɗi na ƙunshe ne cikin sanarwar da WAEC ta fitar ranar Litinin ta bakin Mrs Moyosola Adesina wadda ta kasance Muƙaddashin Shugaban Sashen Hulɗa da Jama'a hukumar a Legas. Adesina ta bayyana cewa, Dangut ya fara aiki da hukumar ne a shekarar 1998 ne a matsayin "Assistant Registrar (AR)…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta ƙwace kujerar Gwamnan Nasarawa daga hannun APC ta miƙa wa PDP

Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta ƙwace kujerar Gwamnan Nasarawa daga hannun APC ta miƙa wa PDP

Kotun Sauraren Ƙorafe-ƙorafen Zaɓen Gwamnan Jihar Nasarawa, ta tsige Injiniya Abdullahi Sule a matsayin Gwamnan Jihar Nasarawa. Biyu daga cikin alƙalan kotun su uku ƙarƙashin jagorancin Mai Shari'a Ezekiel Ajayi, sun bayyana ɗan takarar Jam'iyyar PDP, David Umbugadu a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan da ya gudana a wannan shekarar da ake ciki. Ya zuwa haɗa wannan labarin alƙali na, Jastis Ibrahim Mashi, bai kai ga bayyana nasa hukuncin ba.
Read More
MURIC ta yaba wa sojojin Nijeriya bisa gano masana’antar bindiga a kudancin Kaduna

MURIC ta yaba wa sojojin Nijeriya bisa gano masana’antar bindiga a kudancin Kaduna

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyar Kare Haƙƙin Musulmi (MURIC), ta yaba wa sojojin da suka gano wata masana’anta da ke haɗa bindigogi a Jihar Kaduna. Farfesa Ishaq Akintola, Babban Darakta na MURIC ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin a Abuja. Akintola ya bayyana wannan farmakin na sojoji a matsayin wani babban ci gaba da kuma buɗe ido ga kokarin da hukumomin tsaro da gwamnatin jihar Kaduna ke yi na bankaɗo masu hannu a rikicin jihar. “An gano wata masana’antar ƙera bindigogi a Kafanchan, Ƙaramar Hukumar Jemaah ta jihar Kaduna a ranar Juma’a, 22 ga…
Read More
Me ake cewa ciwon sanyi na mata?

Me ake cewa ciwon sanyi na mata?

Daga AISHA ASAS Idan aka ce ciwon sanyi, akan samu bambancin fassara daga mutane da dama, wanda ke kawo ruɗani, har matan su kasa bambance wane ne haƙiƙanin ma'ana ta wannan ciwo da ake wa laƙabi da na sanyi. Wasu da dama suna kiran ciwon sanyi a matsayin cuta da ake kamuwa da ita ta hanyar kwanciyar aure, inda suke bayanin ta a matsayin cuta da ake saka wa mata. Wasu kuwa suna fassara ciwon da cutar da ake samu sakamakon rashin tsaftace al'aura, kama daga rashin wanke kamfai akai-akai, rashin amfani da shi, rashin tsaftace wurin da abin da…
Read More
Dandalin shawara: Matata ba ta taɓa gode wa ƙoƙarina ba

Dandalin shawara: Matata ba ta taɓa gode wa ƙoƙarina ba

Daga AISHA ASAS TAMBAYA: Malama Aisha, sannu da ƙoƙari. Ya iyali? Allah ya yi jagora. Don Allah Ina so ki ja hankalin mata a shafinku na iyali akan mata masu ƙin gode wa mazajensu, wallahi wasu matan ba su da imani, ko kaɗan ba su aminta da matsalar rayuwa da ake ciki a yanzu ba. Matata shekara 10 muna tare, amma ban taɓa barinta da yunwa ba, ba a taɓa ranar da ban kawo ba, sai dai wata rana da daɗi wata rana ba daɗi. Ba ta taɓa gode ƙoƙarina ba, sai dai duk ranar da na kasa kawo irin…
Read More
Shin waye bai taɓa sauya sheƙa ba?

Shin waye bai taɓa sauya sheƙa ba?

Tare da NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Sheƙa dai da duk wanda ya fahimci sunan na nufin ‘Gidan Tsustsu” da ya kan gina ko sassarƙafa da kan sa cikin baiwar da Allah ya yi ma sa. Haƙiƙa tsuntsaye na da basirar gasken gaske don yadda su kan saka sheƙar nan su kaɗai. Za ka ga wasu tsuntsayen na tafiya wani waje su na ɗauko kayan haɗa sheƙa ɗaya bayan ɗaya su na sagalawa har su gama. Kwanan nan naga wani hoto mai ban tausayi da ke nuna ’ya’yan wata tsuntsuwa sun mutu a cikin sheƙa sai a ka rubuta ba mamaki an…
Read More
Gangamin bukukuwan Maulidi

Gangamin bukukuwan Maulidi

Al'ummar Musulmi da dama a Nijeirya sun bi sahun sauran ’yan uwansu a faɗin duniya wajen murna da zagayowar ranar haihuwar Annabi Muhammad (Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi.) Musulmai da dama sun yi amannar cewa a watan Rabiu'l Awwal, aka haifi Annabi Muhammad (SAW). A irin wannan rana ce Allah (SAW), ya yi wa halittarsa kyautar da ta fi kowacce irin kyauta daraja, wato Manzon Allah SAW, kamar yadda Musulunci ya bayyana. Al'ummar Musulmai dai kan yi hidima a wannan lokaci, kamar a Nijeriya musamman a jihohin arewacin ƙasar, makarantun allo ko na Islamiyya kan shirya…
Read More