Editor

9513 Posts
Allah Ya yi wa Jarumar Kannywood, Hajiya Binta Ola asuwa

Allah Ya yi wa Jarumar Kannywood, Hajiya Binta Ola asuwa

Daga UMAR GARBA a Katsina Allah Ya yi wa shahararriyar jarumar fina-finan Hausa, Hajiya Binta Ola rasuwa. Hajiya Binta ta rasu ne da misalin ƙarfe 3 na daren jiya Talata, a gidanta dake Sabuwar unguwa Ƙofar Ƙaura, dake jihar Katsina bayan gajeruwar rashin lafiya. Majiyar mu ta ce za a yi jana'izar marigayiyar a wannan Laraba da misalin ƙarfe 10 na safe a gidanta dake Sabuwar unguwa cikin garin Katsina.
Read More
An tsige Kakakin Majalisar Wakilan Amurka, Kevin McCarthy

An tsige Kakakin Majalisar Wakilan Amurka, Kevin McCarthy

A ranar Talata 'yan Majalisar Wakilan ƙasar Amurka suka tsige Kakakin majalisar, Kevin McCarthy, bayan kaɗa ƙuri'ar jin ra'ayi. Wannan al'amari wanda tarihin siyasar ƙasar ba zai mance da shi ba, ya jefa 'yan Jam'iyyar Republican a majalisar cikin ruɗani. Da wannan mataki da 'yan majalisar suka ɗauka, yanzu ya zama wajibi su zaɓi wanda zai maye gurbin McCarthy. Sai dai ya zuwa haɗa wannan rahoto, babu cikakken bayani kan wanda za a zaɓa a matsayin sabon kakakin Majalisar. Kodayake dai 'yan majalisar sun naɗa Patrick McHenry na Carolina ta Arewa a matsayin muƙaddashin kakakin Majalisar ya zuwa lokacin da…
Read More
Macen da ba ta da abin yi na saurin gundurar namiji – Aisha Adamu Sadiq

Macen da ba ta da abin yi na saurin gundurar namiji – Aisha Adamu Sadiq

"Wasu matan babu ce ke jefa su halin rashin kamun kai" Daga AISHA ASAS Masu azancin zance suna cewa, sana’a goma maganin mai gasa. A wannan makon shafin Gimbiya na jaridar Manhaja ta ɗauko maku matashiya mai sana'ar sarrafa fara, siyar da abayoyi, akwatuna da ma haɗa lefe bakiɗaya. A tattaunawar Manhaja da matashiyar, ta tavo yadda sana'ar siyar da fara ke bayar da abin rufa asiri, saɓanin yadda mutane da dama suke kallonta a matsayin shiririta. Sannan kuma ta yi ƙarin haske kan yadda sana'arta ta haɗa lefe ke gudana. Babban fatanmu dai mata su amfana da wannan shafin,…
Read More
Dalilin da ya sa na tsunduma siyasa duk da kasancewa ta limamin coci – Mawaƙi Banky W 

Dalilin da ya sa na tsunduma siyasa duk da kasancewa ta limamin coci – Mawaƙi Banky W 

Daga AISHA ASAS  Shahararren mawaƙin Nijeriya Olubankole Wellington, wanda aka fi sani da Banky W, ya bayyana dalilin sa na shiga siyasa har ya tsaya takara, duk da cewa, a yanzu shi limami ne na Coci. A cikin wata tattaunawa da ya yi da BBC, mawaƙin wanda a halin yanzu yake jagorantar wata Coci ya bayyana cewa, ya shiga harkar siyasa ne don ya canza ma'anar da mutane da yawa suke yi wa siyasa, inda suke kallon dukka wani ɗan siyasa a matsayin mutumin banza. Mawaƙin ya ce, shigar tasa siyasa har ya tsaya takara, zai zama wata ishara da…
Read More
‘Yan Nijeriya miliyan 62 ne za su amfana da shirin ‘cash transfer’ – Betta Edu

‘Yan Nijeriya miliyan 62 ne za su amfana da shirin ‘cash transfer’ – Betta Edu

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa, 'yan Nijeriya miliyan 62 ne za su amfana daga shirin ba da tallafi na "Conditional Cash Transfer" inda kowanne zai riƙa samun tallafin kuɗi na N25,000 duk wata har na tsawon wata uku. Kazalika, gwamnatin ta yi alkawarin tallafa wa mata 'yan kasuwa su miliyan ɗaya da rabi ta shirin "Iyaloja Fund". Ministar Jinƙai da Yaƙi da Talauci, Dr Betta Edu ce ta bayyana haka sa'ilin da ta kai wa Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris Malagi, ziyara ranar Talata a ofishinsa da ke Abuja. A cewarta, “Za mu aiwatar da…
Read More
Muƙamin Minista: Tinubu ya maye gurbin El-Rufai da Balarabe

Muƙamin Minista: Tinubu ya maye gurbin El-Rufai da Balarabe

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya zaɓi Abbas Balarabe don maye gurbin tsohon Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai, a matsayin minista. Hakan na ƙunshe ne cikin wasiƙar da Tinubu ya aike wa Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, a ranar Talata Haka nan, Dr Jamila Ibrahim da Ayodele Olawande na daga cikin sunayen da wasiƙar ta ƙunsa wanda Tinunu ke neman majalisar ta tabbatar da su a matsayin ministocin matasa. Idan ba a manta ba, a watan Agustan da ya gabata Majalisar Dattawa ta tantance tare da tabbatar da ministoci 45, amma ta ƙi tabbatar da wasu uku, ciki har da toshon Gwamnan…
Read More
Hon. Hassan El Ben Jaz ya raba wa mutum 3210 tallafin abinci a Yobe

Hon. Hassan El Ben Jaz ya raba wa mutum 3210 tallafin abinci a Yobe

Daga MUHAMMAD AL-AMEEN a Damaturu A yunƙurin sa wajen rage wa al'ummar mazaɓarsa wahalhalun da cire tallafin man fetur ya jefa jama'a, ɗan majalisa a Mazaɓar Bade/Jakusko a jihar Yobe, a zauren majalisar wakilai ta ƙasa, a ƙarƙashin jam'iyyar PDP, Hon. Hassan Jakduwa KaiKaku (El Ben Jaz) ya ƙaddamar da rabon kayan abinci, tare da takin zamani ga manoma a mazaɓarsa dake jihar Yobe. A jawabinsa wajen ƙaddamar da rabon kayan a Gashuwa, Hon. Hassan El Ben Jaz, wanda Malam Salisu Jawi ya wakilta a taron, ya ce aƙalla mutum 3210 ne a mazaɓarsa za su ci gajiyar tallafin a…
Read More
Jaruma Anita ta yi allawadai da masu neman a yi gwajin DNA ga ɗan Mawaƙi Mohbad

Jaruma Anita ta yi allawadai da masu neman a yi gwajin DNA ga ɗan Mawaƙi Mohbad

Daga AISHA ASAS  Biyo bayan mutuwar mawaƙi Mohbad mai shekaru 27 da haihuwa, mutuwar da ta taɓa mutane da dama, wanda ta sa aka tada ƙura, da ta yi sanadin samun shahara ga mawaƙin fiye da lokacin da yake raye. Mutuwar wadda take ɗauke da ruɗani da neman sanin ababe da dama dangane da silar mituwar matashin mawaƙin. Da yawa sun zargi ubangidan mawaƙin, wato fitaccen mawaƙi Naira Marley, wanda aka ruwaito cewa, mawaƙi Mohbad ya jima yana kai kuken cin zafarin da yake masa a matsayin sa na ubangidansa, wanda har a wasu waƙoƙinsa yana ƙoƙarin bayyana halin da…
Read More
Ba duk finafinan Nollywood ne ake iya hasashen ƙarshensu ba – Tana Adelana

Ba duk finafinan Nollywood ne ake iya hasashen ƙarshensu ba – Tana Adelana

Daga AISHA ASAS  Jaruma a masana'artar finafinai ta Kudu, Tana Adelana ta musanta faɗar mutane da suke cewa, dukka finafinan da masana'antar Nollywood ke fitarwa mai kallo zai iya hasashen yadda zaren labarin zai ci gaba har ya zuwa ƙarshe.  Jarumar ta mayar da martani da cewa, ba fa kowanne fim daga cikin finafinan Nollywood ne mai kallo zai iya hasashen yadda labarin zai ci gaba, domin akwai waɗanda sai dai mai karatu ya tsumayi zuwan ci gaba, wanda zai zo masa a ba yadda ya yi tunanin sa ba. A cikin tattaunawar ta a shirin Saturday Beats, jaruma Tana,…
Read More
Rushewar ginin coci ta yi ajalin Fasto a Binuwai

Rushewar ginin coci ta yi ajalin Fasto a Binuwai

Bayanin da muka samu yanzu-yanzu ya ce, sashen ginin Cocin Dunamis da ke daura da Mission Ward North Bank a Makurɗi, babban birnin Jihar Binuwa, ya rushe. Blueprint Manhaja ta kalato cewar, rushewar ginin wadda ta auku da safiyar wannan Talatar ta yi ajalin wani fasto tare da jikkata wasu masu ibada a mujami'ar. Bayanai sun ce, Faston tare da wasu mutum uku na tsaka da gabatar da addu'a ne a lokacin da wani ɓangaren ginin ya rikito a kansu. Ya zuwa haɗa wannan labari babu cikakken bayani kan dalilin aukuwar iftila'in. Da aka nemi jin ta bakinta, Kakakin 'yan…
Read More