Editor

9513 Posts
Ana xaukar nauyin ta’addanci da kuxin garkuwa da mutane a Nijeriya – Gwamnati

Ana xaukar nauyin ta’addanci da kuxin garkuwa da mutane a Nijeriya – Gwamnati

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Tsohon sojin ruwan Nijeriya, Rear Admiral Yaminu Musa (mai ritaya), Shugaban Gudanarwa na Cibiyar Yaqi da Ta’addanci a ofishin mai baiwa shugaban qasa shawara kan harkokin tsaro (NCTC-ONSA) ya ce ana amfani da kuxaxen da ake samu na garkuwa da mutane ne wajen samar da kuxaxen ta’addanci. Musa ya bayyana haka ne a ranar Laraba a Abuja yayin taron ‘Anti-Kidnap Multi-Agency Fusion Cell Media and Communication Workhop’ wanda ONSA tare da haxin gwiwar babbar hukumar Birtaniya ta shirya. “An kuma bayyana satar mutane don neman kuxin fansa a matsayin xaya daga cikin hanyoyin samar da kuxaxen…
Read More
A karon farko an yi tozali da abokin karatun Tinubu

A karon farko an yi tozali da abokin karatun Tinubu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wani mai sharhi kan al’amuran jama’a, Durojaiye Ogunsanya, ya bayyana shugaba Bola Ahmed Tinubu a matsayin abokin karatunsa a Jami’ar Jihar Chicago da ke Ƙasar Amurka (CSU). A yayin da ya ke magana a wani shiri na TVC, Ogunsanya ya ce shi da shugaban Nijeriya sun kammala karatun digiri a sashin kula da harkokin kuɗi da kasuwanci a shekarar 1979. Idan za a iya tunawa, taƙaddama kan karatun shugaba Tinubu ya kasance abin cece-kuce kamar yadda wasu abokan hamayyarsa na siyasa suka ce Tinubu bai  halarci jami'ar CSU ba. Tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar, yana…
Read More
Yadda babban layin lantarki ya jefa Nijeriya duhu

Yadda babban layin lantarki ya jefa Nijeriya duhu

*Minista ya yi ƙarin haske*Wannan ne duhun-duhununa na farko a mulkin Tinubu Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ministan Wutar Lantarki na Tarayyar Nijeriya, Adebayo Adelabu ya ce an samu fashewar wani abu da ya kai ga ɓarkewar gobara a tashar wuta ta Kainji/Jebba da ke yankin Arewa ta Tsakiyar Nijeriya. Adelabu a cikin jerin saƙon a dandalin sadarwa na X a jiya Alhamis ya ce, da ƙarfe 04:35 na asubahin Alhamis an ji tashin gobara tare da ƙarar fashewar abubuwa a layin Kainji/Jebba mai qarfin 330KV Line 2 (Cct K2J) Blue Phase CVT da Blue Phase Line Isolator na…
Read More
NNPP ta buƙaci INEC ta dakatar da shirin Kwankwasiyya na yi wa jam’iyyar kwaskwarima

NNPP ta buƙaci INEC ta dakatar da shirin Kwankwasiyya na yi wa jam’iyyar kwaskwarima

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Jam’iyyar NNPP ta rubutawa Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), inda ta buƙaci hukumar ta dakatar da shirin da wasu ƙungiyoyi ke yi na sauya tambarin jam’iyyar. Jam’iyyar ta kuma rubuta wa Sanata Rabiu Kwankwaso, ɗan takararta na shugaban ƙasa a 2023, domin ya kawo ƙarshen yarjejeniyar da ta shigar da ƙungiyar Kwankwasiyya cikin al'amuran jam'iyyar a zaɓen 2023. Wasiqun da Peter Ogah, lauyan jam’iyyar ne ya rubuta wa INEC da Kwankwaso ya sanya wa hannu kuma aka miƙa wa manema labarai ranar Laraba a Legas. Wasiƙar zuwa ga INEC tana ɗauke da taken:…
Read More
Jami’ar Legas na shirin tilasta wa ɗalibai ɗaukar darasin Yarabanci

Jami’ar Legas na shirin tilasta wa ɗalibai ɗaukar darasin Yarabanci

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Jami’ar Jihar Legas (LASU) a wani yunƙuri na kare martabar al’adun gargajiyar Nijeriya, ta sanar da shigar da harshen Yarabanci a matsayin kwas na tilas ga ɗaukacin ɗalibanta. Sabon kwas da aka ƙara a cikin manhajar makarantar daga zaman karatun 2023/2024 mai suna GNS 104 (Nazarin Harshen Yarabanci). Shawarar da LASU ta yi na gabatar da wannan kwas ɗin ya yi daidai da ƙoƙarin da ake yi na ƙasa baki ɗaya na kiyaye al'adun gargajiya da al'adu daban-daban na Nijeriya. Kwas ɗin, Nazarin Harshen Yarbanci, an tsara shi ne don baiwa ɗalibai cikakkiyar fahimtar harshen Yarbanci,…
Read More
Tinubu ya yi sababbin naɗe-naɗe

Tinubu ya yi sababbin naɗe-naɗe

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A Juma'ar da ta gabata Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya sanar da wasu sababbin naɗe-naɗe da ya yi a wasu muhimman hukumomin Gwamnatin Tarayya, domin su jagorance su. An naɗa sabon shugaban hukumar tara haraji (FIRS): Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya amince da naɗin Honarabul Zacch Adedeji a matsayin sabon shugaban riqo na Hukumar Tara Kuɗaɗen Haraji ta Tarayyar Nijeriya (FIRS) da gaggawa. Shugaban ƙasar ya umarci tsohon shugaban FIRS, Muhammad Nami, da ya ci gaba da hutun watanni uku kafin ya yi ritaya kamar yadda dokar ma’aikatan gwamnati (PSR) 120243 ta tanada nan take.…
Read More
ASUU ta ƙi amincewa Tinubu ya bai wa jami’o’i cin gashin kansu

ASUU ta ƙi amincewa Tinubu ya bai wa jami’o’i cin gashin kansu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyar Malaman Jami’o’in Nijeriya (ASUU) ta yi watsi da shirin gwamnatin shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu na bai wa jami’o’in cikakken ’yancin cin gashin kai, tana mai cewa ba zai yiwu gwamnati ta tsame hannunta daga bayar da tallafin karatu ga manyan jami’o’i ba. Shugaban ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke ya bayyana haka ne a ranar Alhamis, 15 ga Satumba, 2023, yayin wata hira da gidan talabijin na Channels Television na Sunrise Daily. Ya na mayar da martani ne kan wani rahoto da Ministan Ilimi Farfesa Tahir Mamman ya bayyana cewa gwamnati za ta ɓullo da sabbin…
Read More
Za a iya yin mummunar ambaliya a jihohi 13, inji NEMA

Za a iya yin mummunar ambaliya a jihohi 13, inji NEMA

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (wato NEMA) ta ce, jihohi 13 da al’ummomi 50, musamman a Arewa, akwai yiwuwar ganin an samu ruwan sama mai ƙarfin gaske, wanda zai haifar da ambaliya tsakanin 13 da 17 ga watan Satumba, 2023. Mista Ibrahim Farinloye, ko’odinetan hukumar NEMA na yankin Legas ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba a Legas. Farinloye ya lissafa jihohin da al’ummomin da suka haɗa da jihar Kano, inda al’ummomi irin su Sumaila da Ƙunchi za su iya shafa. Ya kuma ce, Jihar Kebbi mai…
Read More
Tabar wiwi: ‘Yan sandan Kebbi sun yi kamu mafi girma a tarihi

Tabar wiwi: ‘Yan sandan Kebbi sun yi kamu mafi girma a tarihi

Daga JAMIL GULMA a Kebbi  Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kebbi ta kama manyan motoci guda biyu maƙare da tabar wiwi da ba a taɓa kama irinsa ba a tarihin tsaro a jihar ta Kebbi. A motar ta farko mai lamba IT 21520 LA, Lagos, ’yan sanda sun kama surken ƙullin wiwi guda 4,927 da aka ƙiyasta kuɗinsa ya kai fiye da Naira miliyan 300.  'Yan sanda sun kama mutane uku masu suna Emmanuel Chukwuma ɗan asalin Ƙaramar Hukumar Banden a Jihar Abiya, da Kanta Bisa ɗan Ƙaramar Hukumar Asaka a Ƙasar Ghana, tare da Ishola Adeyemi, ɗan Unguwar Alufon a Ƙaramar…
Read More
Tabbas Rasha za ta yi nasara a kan Ukraine – Kim Jong Un

Tabbas Rasha za ta yi nasara a kan Ukraine – Kim Jong Un

Shugaban Korea ta Arewa Kim Jong Un, ya ce Rasha na samun gagarumar nasara a faɗan da ta ke yi da maƙiya, kalaman da ke zuwa a ziyarar da shugaban ke ci gaba da gudanarwa a Moscow, a wani yunƙurin samar da kyakkyawar alaƙa ciki har da ta aikin soji tsakanin ƙasashen biyu. Duk da cewa kawo yanzu babu wasu bayanai da ke tabbatar da cewa akwai wata yarjejeniya da ke bai wa Rasha damar samun makamai da kuma kayan aikin soji daga Korea ta Arewa, amma Amurka ta yi zargin cewa akwai yiyuwar ƙasar na shirin taimaka wa Moscow…
Read More