16
Sep
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan 'Yan Ƙasa, Alhaji Muhammed Idris Malagi, ya bayyana cewa, dimokuraɗiyya ba ta da wani amfani muddin ba za ta haifar da cigaba da haɗin kan al'umma ba. Mataimakin Daraktan Yaɗa Labarai a Ma'aikatar, Suleiman Haruna, ya ce Ministan ya bayyana haka ne yayin da mambobin jam'iyyar APC na shiyar Arewa ta Tsakiya suka ziyarce shi a ofishinsa da ke Abuja a ranar Juma'a. “Wannan ne ma ya sa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bai wa batun haɗin kai da bunƙasa tattalin arziki muhimmanci ga jama'armu, ni ma wannan shi ne saƙon da nake…
