15
Sep
Daga JAMIL GULMA a Kebbi Gwamna Malam Nasir Idris ya maye kujerar Marigayi Sheikh Abubakar Abddullahi Giro Argungu da ɗansa Malam Hussaini Abubakar Giro a hukumar jin daɗin Alhazai ta jihar Kebbi, inda Sheikh Abubakar Giro kafin rasuwarsa mamba ne a hukumar. Wannan ya biyo bayan wani koke da ƙungiyar Izala ta ƙasa ƙarƙashin jagoranacin Sheikh Bala Lau ta miƙa wa Gwamna Idris ne yayin da suka je ta'aziyya a fadar gwamnatin jihar Kebbi inda suka nemi gwamnati da ta janyo ɗaya daga cikin 'ya'yan Marigayi Giro a jiki saboda cigaba daga inda ya tsaya. Gwamna Malam Nasir Idris ya…
