Editor

9513 Posts
Maikatanga ya lashe gasar ɗaukar hoto ta Wiki Loves Africa

Maikatanga ya lashe gasar ɗaukar hoto ta Wiki Loves Africa

Fitaccen ɗan jarida a fannin ɗaukar hoto a Nijeriya, Sani Maikatanga, ya lashe gasar ɗaukar hoto ta ƙasa da ƙasa ta Wiki Loves Africa 2023. Mutum 13,413 daga ƙasashen Afirka 51 ne suka shiga gasar. Maikatanga ya yi wa takwarorinsa zarra a gasar ne ta dalilin wani hoto da ya ɗauka mai alaƙa da sauyin yanayi a ƙauyen Auyo, Jihar Jigawa. Taken gasar na bana ya maida hankali ne kan sauyin yanayi. Bayanan Hukumar Kiwon Lafiya ta Duniya, (WHO), sun nuna sauyin yanayi matsala ce da kan shafi iskar da ake amfani da ita da ruwan sha da abinci da…
Read More
Ku ba wa iyalanku kariya daga cutar mashaƙo

Ku ba wa iyalanku kariya daga cutar mashaƙo

Daga AISHA ASAS Kamar yadda yake haƙƙi da ya rataya kanka maigida na daga ci da sha ga iyalanka, haka ya kasance haƙƙi gare ka ka ba wa iyalanka kariya daga curutukan da ka iya yiwa iyalanka lahani. Ba ma maigida kawai ba, a matsayinki ta uwa mai kula da sha'anin iyalinta ke ma ya kamata ki kula tare da mayar da hankali wurin ganin curutukan nan na zamani sun tsallake gidanki. Wannan ne ya sa yake da matuƙar muhimmanci samun ilimi kan kowacce irin cuta da ke yaɗuwa, wanda hakan zai ba ku dama, wurin ba wa 'ya'yanku da…
Read More
Ta yaya za a iya magance warin gaba

Ta yaya za a iya magance warin gaba

Daga AISHA ASAS Mai karatu barkanmu da sake kasancewa a shafin Kwalliya na jaridar Manhaja. A satin da ya gabata, mun tavo bayyani kan dalilan da ke haifar da warin gaban mace, wanda muka tabbatar ba halitta ba ce. A wannan makon, da yardar mai dukka, za mu kawo wasu daga cikin ababen da uwar gida za ta yi don kawar da warin gaba, sai dai kamar yadda muka yi bayanin ababen da ke haifar da warin na gaba, zan so uwar gida ta fara da haddace su, ya zamana ta kauce wa dukka hanyoyin na samuwar warin kafin ta…
Read More
UAE ta ɗage haramcin bai wa ‘yan Nijeriya bisar shiga ƙasar

UAE ta ɗage haramcin bai wa ‘yan Nijeriya bisar shiga ƙasar

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da takwaransa na Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE), Mohamed bin Zayed Al Nahyan, sun cimma yarjejeniyar ɗage haramcin bai wa matafiya daga Nijeriya bisa ta shiga ƙasar. A ranar Litinin shugabannin biyu suka cimma wannan matsaya a Abu Dhabi, inda aka amince jiragen Etihad Airlines da na Emirates Airlines su ci gaba da zirga-zirga a Nijeriya nan take. Kuma yarjejeniyar ci gaba da zirga-zirgar jiragen ba ta shafi gwamnatin Nijeriya ta biya wasu kuɗaɗe nan take ba. La'akari da manufar Tinubu ta inganta tattalin arzikin Nijeriya haɗa da sauran tsare-tsaren bunƙasa tattalin arzikin ƙasa da ya…
Read More
Alƙali, tsammani bai yi yadda PDP da LP su ka yi tsammani ba!

Alƙali, tsammani bai yi yadda PDP da LP su ka yi tsammani ba!

Tare Da NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Babban alƙalin da ya jagaoranci ƙarar ƙalubalantar sakamakon zaɓen shugaban Nijeriya na ranar 25 ga watan Febreru 2023 Haruna Tsammani bai yanke hukunci bisa yadda manyan jam’iyyun adawa biyu PDP da LP da kuma ta uku APM su ka yi tsammanin samun nasara ba. Dama haka shari’a ta ke kuma ba a hasashen me alqali zai yanke hukunci sai an jira ya yanke bisa yadda ya ke a tanadin doka. Hasalima kotu kan iya kama mutum da raini matuƙar ya ambaci wani tunani na abun da ya ke ganin zai faru a kotun. Amma dai…
Read More
Abin da maigidanki ya shuka kika girba, ra’ayin ‘yan Nijeriya kan urwagidan Gwamnan Bauchi

Abin da maigidanki ya shuka kika girba, ra’ayin ‘yan Nijeriya kan urwagidan Gwamnan Bauchi

'Yan Nijeriya na ci gaba da bayyana ra'ayoyinsu a soshiyal midiya dangane da halin da uwargidan Gwamnan Bauchi, Hajiya Aisha Bala Mohammad, da tawagrata suka tsinci kansu a lokacin da ta kai ziyara yankin Jamdan don ƙaddamar da cibiyar kula da lafiya. Hotunan da suka karaɗe kafafen sada zumunta na zamani sun nuna yadda Aisha Bala da tawagarta suka sha fama a hanya saboda rashin kyawun hanyar zuwa garin da suka kai ziyarar. Lamarin da ya kai matar Gwamnan ta sauka a motarta ta taka da ƙafafunta saboda matsalar caɓi a hanyar. Tuni dai wasu 'yan Nijeriya suka yi ra'ayin…
Read More
Talakan Nijeriya bawan Allah

Talakan Nijeriya bawan Allah

Gaskiya duk abin da tsohon Sarkin Kano Sunusi ya faɗa za a cigaba da shan wahala a Nijeriya alamu sun nuna biri ya yi kama mutum sai ko Allah ya kawo mafita da tallafin sa. Saboda tun gwamnatin da Tinubu ya gada vata shekara ba aka ce sai kowa ya ji a jikinsa aka yi wa gwamnati uzuri ana gani kamar wahala mai karewa ce daga ƙarshe za a sha jarmiya, amma alƙawari Bai cikaba. Aka gama shekara huɗu aka sake uzuri aka zave su wahala ta cigaba. Har aka zo kan batun janye tallafin karatu ga ɗalibai da canjin…
Read More
Biden ya jinjina wa Tinubu kan kare martabar dimokuraɗiyya

Biden ya jinjina wa Tinubu kan kare martabar dimokuraɗiyya

Shugaba Joe Biden na ƙasar Amurka, ya yaba da shugabancin da Shugaban Nijeriya, Bola Tinubu, ke yi wa ƙungiyar raya tattalin arzikin ƙasashen Afirka ta Yamma (ECOWAS). Biden ya jinjina wa Tinubun ne la'akari da ƙoƙarin da ke ECOWAS ke yi wajen maido da tsarin mulkin dimokraɗiyya a ƙasar Nijar. Biden ya ce jajircewar da Tinubu ke yi wajen kare tsarin dimokuraɗiyya a Nijar da ma yankin Afirka ta Yamma baki ɗaya abin a yaba ne. Ya byyana haka ne yayin ganawarsu da Tinubu a wajen taron G20 da ya gudana a Delhi, Kasar Indiya. Cikin sanarwar da ta fitar…
Read More
Matsalar tsaro: Wa’adin shekara guda

Matsalar tsaro: Wa’adin shekara guda

A kwanakin baya ne shugaban ƙasa Ahmed Bola Tinubu ya bai wa ministocin tsaro da hafsoshin tsaron Nijeriya wa’adin shekara guda domin kawo ƙarshen duk wani nau’in rashin tsaro a ƙasar. Da yake fuskantar ƙalubalen, Ministan Tsaro, Abubakar Badaru, ya ziyarci wasu manya-manyan hafsoshin soji domin jin yadda za a ɓullo wa bakin zaren. Kafin yanzu dai an fara samun tashin hankali sakamakon yawaitar hare-haren ta'addanci da kashe-kashe a wasu sassan ƙasar inda akasarin 'yan Nijeriya suka lulluɓe cikin yanayi na firgici da damuwa. A baya-bayan nan ne dai rundunar sojin Nijeriya ta rashin kimanin mutane 37 da suka haɗa…
Read More