Editor

9513 Posts
Kotu ta ƙwace kujerar ɗan majalisa daga hannun NNPP ta bai wa APC a Kano

Kotu ta ƙwace kujerar ɗan majalisa daga hannun NNPP ta bai wa APC a Kano

Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe a Jihar Kano ta tsige Yusuf Umar Datti na Jam'iyyar NNPP a matsayin zaɓaɓɓen ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Kura/Madobi/Garun Malam a jihar. Bayan tsige Datti daga kujerar ɗan majalisa tmda ta yi, kotun ta ayya abokin hamayyarsa na jam'iyyar APC, Musa Ilyasu Kwankwaso, a matsayin wanda ya lashe zaɓe. Kotun ta yanke wannan hukuncin ne bayan da ta kama Datti da laifin ƙin ajiye aikin gwamnati a tsakanin kwana 30 kafin shiga zaɓe kamara yadda doka ta tanada. Kafin shiga zaɓen, ɗan siyasar ma'aikaci ne a Jami'ar Bayero ta Kano. Kazalika, Alƙali Azingbe ya ce…
Read More
Minista Malagi a mizani

Minista Malagi a mizani

Ga duk wanda ya fahimci Malagi a natse kuma ya iya fahimtar yadda haƙuri da jajircewa ke zamowa sular ɗaukakar mutum za a iya tabbatar da cewa lallai mun dace da miqa wa Alhaji Muhammed Idris Malagi muƙami na minista a fannin labarai. Kakakin na Nufe na da kyakkyawan hali na haƙuri wanda tun a neman takara ta gwamna a jihar su Neja wanda abokin takarar sa Alh Bago ya samu. Malaji bai koma gefe ya riƙa surutai da soke soke ba wanda hakan wata al'ada ce wacce da dama yan siyasar mu ta zamo ma su jiki duk wanda…
Read More
Dangantaka na ƙara tsami tsakanin Gwamna Obaseki da mataimakin sa

Dangantaka na ƙara tsami tsakanin Gwamna Obaseki da mataimakin sa

Ana yunƙurin fitar da ofishin mataimakin daga fadar gwamnati Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Rikicin da ke tsakanin Gwamnan Jihar Edo, Godwin Obaseki da mataimakinsa, Philip Shaibu na ci gaba da ruruwa yayin da ake shirin mayar da mataimakinsa wani gini da ke wajen gidan gwamnati. Ginin da ke lamba 7, Dennis Osadebey Avenue, kusa da gidan gwamnati, wanda shine ofishin hukumar saye da sayarwa ta jihar Edo, an gyara shi domin ya zama ofishin mataimakin. Tsohon gwamnan jihar, Adams Oshiomhole ne ya qaddamar da ginin a ranar 16 ga watan Disamba, 2014. Sai dai kuma da aka tuntuɓi…
Read More
Bayan kotu ta tabbatar da nasarar zaɓen Tinubu…

Bayan kotu ta tabbatar da nasarar zaɓen Tinubu…

*Atiku da Obi za su cigaba da yaƙin*Tinubu ya yi maraba da hukuncin*Buhari ya tsomo baki*Tinubu ya nuna gwanintar mulki a kwana 100 – Ministan Labarai Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Kotun Sauraron Ƙararrakin Zaɓen Shugaban Ƙasa ta tabbatar da nasarar Zaɓen Shugaba Bola Ahmed Tinubu. Shugaban kotun, Mai shari'a Haruna Tsammani ya ce matakin hukumar Zaɓe na ayyana Bola Tinubu, a matsayin wanda ya lashe zaɓen 25 ga watan Fabrairu, ya dace. Matakin na zuwa ne bayan kotun ta kori ƙarar ɗan takarar shugaban ƙasa na babbar jam'iyyar adawar Nijeriya, Atiku Abubakar da maraicen Laraba. Shi, da Peter…
Read More
Juyin mulkin Burkina Faso: Reshe ya nemi juyawa da mujiya

Juyin mulkin Burkina Faso: Reshe ya nemi juyawa da mujiya

Daga BASHIR ISAH An cafke wasu manyan jami'an soji a ƙasar Burkina Faso bisa yunƙurin yin juyin mulki ga sojojin da suka hamɓarar da mulkin dimokraɗiyya a ƙasar. Mai gabatar da ƙara na mulkin sojin ƙasar, Manjo Alphonse Zorma ne ya bayyana haka a ranar Juma'a. Ya ce a makon da ya gabata masu bincike suka samu rahoto kan shirin da wasu sojoji da tsoffin sojojin ƙasar ke yi na neman kifar da sosjojin da ke riƙe da ƙasar a halin yanzu. Sanarwar ta ce cikin hasfsoshin da lamarin ya shafa har da Kyaftin Ibrahim Traore wanda jigo ne a…
Read More
Girgizar ƙasa ta kashe sama da mutum 296 a Moroko

Girgizar ƙasa ta kashe sama da mutum 296 a Moroko

Daga BASHIR ISAH Rahotanni daga ƙasar Moroko sun ce, sama da mutum 296 sun mutu sakamakon girgizar ƙasa mai karfin maginitud 6.8 da ya auku a ƙasar. Jami'ai sun ce galibin waɗanda suka mutu mutanen da suka maƙale ne a ɓuraguzan gine-gine wanda kai wa gare ya yi wahala balle a cece su a yankunan Kudancin Marrakech. Iftilain girgizar ƙasar ya auku ne da sanyin safiyar wannan Asabar ɗin, lamarin da ya haifar da zubewar gine-gine a wasu manyan biranen ƙasar. A ƙalla mutum 153 aka rawaito sun jikkata kuma ana yi musu magani a asibiti. An ga jami'ai a…
Read More
Gwamnatin Buhari ta ɗaiɗaita tattalin arzikin Nijeriya – Khalifa Sanusi

Gwamnatin Buhari ta ɗaiɗaita tattalin arzikin Nijeriya – Khalifa Sanusi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Sarkin Kano na 14, Muhammadu Sanusi II, ya ce tsohuwar gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta gurgunta tattalin arziki ba tare da neman shawarar ƙwararru ba. Sarki Sanusi wanda kuma shi ne tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), ya bayyana hakan a wani saƙon bidiyo da ya aike wa ‘yan Nijeriya ta yanar gizo. Ya bayyana cewa wasu sun ribaci riƙon sakainar kashi da aka yi wa tattalin arzikin da har aka samu “wani yaro mara ilimi” ya mallaki jirgin sama a ƙarƙashin gwamnatin da ta shuɗe. Ya buqaci ‘yan Nijeriya da su yi haƙuri…
Read More
Ballon d’Or 2022/23: Messi da Haaland sun shiga jerin ’yan takara 30

Ballon d’Or 2022/23: Messi da Haaland sun shiga jerin ’yan takara 30

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Mujallar Faransa ta fitar da sunan 'yan wasa 30 da ke takarar gwarzon ɗan ƙwallon ƙafa, wato Ballon d'Or na duniya na 2022/23. Cikin 'yan wasan har da Lionel Messi da Erling Haaland, waɗanda ake hasashen wani daga ciki ka iya lashe kyautar. Wasu 'yan wasan da suka taka rawar gani da ake ganin za su iya lashe kyautar sun haɗa da Vinicius da Rodri ko kuma Kevin de Bruyne. Tsohon ɗan wasan Real Madrid, wanda ya koma taka leda a babbar gasar tamaula ta Saudiyya, Karim Benzema, shi ne gwarzon Ballon d'Or na bara. Wannan…
Read More
Tallafin man fetur na kowane ɗan ƙasa ne, cewar Gwamna Sule

Tallafin man fetur na kowane ɗan ƙasa ne, cewar Gwamna Sule

Daga JOHN D. WADA a Lafiya Gwamnan Jihar Nasarawa Injiniya Abdullahi Sule ya gargaɗi waɗanda ke rabon kayayyakin tallafin man fetur da gwamnatin tarayya ta bai wa jihar ta Nasarawa su tabbatar suna nuna gaskiya da riƙon amana su kuma guji son kai da sauran su ayayin da suke raba tallafin ga al’ummar jihar baki daya ko su fuskanci fushin gwamnatinsa. Gwamnan ya yi gargaɗin ne a lokacin da ake bikin ƙaddamar da rabon kayayyakin abinci na tallafin man a ƙaramar hukumar Karu a jihar ranar Laraba na mako da ake ciki 6 ga watan Satumbar shekarar 2023. Ya ce…
Read More
Dalilin da ya sa na zaɓi Yar’Adua a matsayin magajina – Obasanjo

Dalilin da ya sa na zaɓi Yar’Adua a matsayin magajina – Obasanjo

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Shugaban Ƙasar Tarayyar Nijeriya Olusegun Obasanjo ya bayyana dalilin da ya sa ya zaɓi tsohon shugaban qasa, Marigayi Alhaji Umar Musa ‘Yar’Adua a matsayin magajinsa duk da ya san cewa ba shi da lafiya. Tsohon shugaban ƙasar a wata hira da ya yi da jaridar Yanar Gizo mai suna “TheCable” ya musanta zargin da ake masa na cewa da gangan ya sanya ’yan takara masu rauni don son kai. A cewarsa, ya ɗauki matakin ne saboda shawarwarin likitoci sun nuna cewa ‘Yar’Adua, wanda aka yi masa dashen ƙoda, ya cancanci zama Shugaban Ƙasa.…
Read More