Editor

9513 Posts
Jami’ar Azman Kano za ta fara yin digiri a ɓangaren tuƙin jirgin sama

Jami’ar Azman Kano za ta fara yin digiri a ɓangaren tuƙin jirgin sama

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Jami'ar nan mai zaman kanta mai suna Azman University da ke Kano, za ta fara yin digiri a fannin koyon tuƙin jirgin sama wanda ya ke shi ne na farko a Nijeriya da ma Afirka ta Yamma. A zantawarta da manema labarai da ya gudana a harabar makarantar da ke 'Yargaya da ke kan titin Wudil ranar Talata, Shugabar Jami'ar Farfesa Fatima Batulu Muktar ta bayyana cewa Jami'ar Azman ta samu sahalewar yin kwasa-kwasan tuqin jirgin sama guda biyu da suka haɗa da; Aviation Management da kuma Aviation Security. Ta kuma ce Jami'ar Azman za…
Read More
Sanata ya ɗauki nauyin koyar da matasa da mata sama da 1000 sana’o’i a Kebbi

Sanata ya ɗauki nauyin koyar da matasa da mata sama da 1000 sana’o’i a Kebbi

Daga JAMIL GULMA a Kebbi A cikin wani shiri na haɗin gwiwa tsakanin Sanata Yahaya Abubakar Abdullahi mai wakiltar gundumar mazaɓar Kebbi ta Arewa da kuma Hukumar Yawon Buɗe Ido (National Institute for Hospitality and Tourism da kuma Muhasaf Global Resources Ltd ) ya ɗauki nauyin koyar da matasa da mata sama da dubu ɗaya sana'o'in hannu a faɗin mazaɓarsa. Da ya ke jawabi a wajen ƙaddamar da koyon sana'o'in Alhaji Sama'ila Ɗantagago a madadin Sanata Yahaya Abubakar ya bayyana cewa koyon sana'o'i ya zama wajibi ga kowane mutum don kare mutuncinsa da na iyalansa, da zarar mutum ba ya…
Read More
INEC ta karrama Sa’idu Bappah da mutum biyar a Gombe

INEC ta karrama Sa’idu Bappah da mutum biyar a Gombe

Daga ABUBAKAR A. BOLARI a Gombe Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa INEC a Jihar Gombe ta karrama Shugaban Sashin Injiniyoyi na hukumar Injiniya Sa'idu Bappa Yaya da wasu ma'aikata mutum 5 bisa jajircewar su a aiki a Jihar Gombe. INEC ta karrama ma'aikatan na ta ne bisa hazaƙar a aiki kafin zaɓe da bayan babban zaven shekarar 2023 da ya gabata. A jawabinsa a wajen taron karramawar da ya gudana a helkwatar hukumar Kwamishinan Zaɓen na Jihar Gombe Alhaji Ibrahim Umar, yaba wa ma'aikatan ya yi bisa ƙwazon da suka nuna a aikin su wanda hakan ne sanadiyyar…
Read More
Shugaban ƙaramar Hukumar Koko a Kebbi ya bai wa ‘yan sanda sabbin motoci

Shugaban ƙaramar Hukumar Koko a Kebbi ya bai wa ‘yan sanda sabbin motoci

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Shugaban Ƙaramar Hukumar Mulki ta Koko/Besse da ke Jihar Kebbi Honarabul Yahaya Bello Koko ya bai wa ofishin hukumar 'yan sanda motoci biyu ƙirar Peogeot 406 tare da gyara Hilux da ta lalace a ƙaramar hukumar. Honarabul Bello ya bayyana cewa ya lura da yadda jami'an 'yan sandan ke wahala bisa ga rashin abin hawa sanadiyyar lalacewar motar da su ke amfani da ita ƙirar Hilux da su ke sintiri da aikin ofis da ita duk da irin matsalar tsaro da ke barazana a wannan yankin. Ya ce ya zama wajibi a haɗa hannu da…
Read More
Tallafi: Gwamnan Neja ya bai wa NLC tirelar shinkafa biyu

Tallafi: Gwamnan Neja ya bai wa NLC tirelar shinkafa biyu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Jihar Neja, Umaru Bago ya amince da tireloli biyu na buhunan shinkafa mai nauyin kilogiram 50 ga ƙungiyar ƙwadago ta ƙasa, NLC, a matsayin tallafin rage raɗaɗin cire tallafn man fetur. Mista Bago ya sanar da amincewar ne a lokacin liyafar murnar sabon ginin ofishin mataimakin gwamna, Yakubu Garba da aka gina a Minna. Ya bayyana cewa Naira miliyan 110 da aka amince wa ƙungiyar ta NLC tun da fari, an ba su ne don samar da kayan aiki don sanya ido kan yadda ake raba kayan agajin a mazaɓu 274 na jihar.…
Read More
Rikicin Boko Haram ya yi ajalin mutum 35,000 a Arewa maso Gabas – MƊD

Rikicin Boko Haram ya yi ajalin mutum 35,000 a Arewa maso Gabas – MƊD

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hukumar Kula da ’Yan Gudun Hijira ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNHCR) ta ce kimanin mutum 35,000 ne suka mutu tun fara rikicin Boko Haram daga shekara ta 2009 zuwa watan Agustan 2023. Shugaban ofishin hukumar a Jihar Adamawa, Elsie Mills-Tetty ce ta bayyana hakan yayin wani taron horar da sojoji a kan kare haƙƙin bil Adama da kuma kare fararen hula a Yola ranar Laraba. Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya rawaito cewa hukumar ta shirya taron ne domin ba su horo kan hanyoyin kiyaye haqqoqin jama’a yayin ayyukansu. Elsie, wacce wani jami’i…
Read More
Arteta na takarar zama gwarzon koci a Firimiya na watan Agusta

Arteta na takarar zama gwarzon koci a Firimiya na watan Agusta

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Mikel Arteta na takarar gwarzon koci a Firimiya na watan Agusta, bayan da ya ja ragamar Arsenal wasa huɗu ba tare da an doke ƙungiyar ba. Kocin ya doke Nottingham Forest da Crystal Palace da yin 2-2 da Fulham a dai gasar ta firimiya da haɗa maki bakwai a watan na Agusta. Wannan ƙwazon na koci ya sa shi cikin koci biyar da ke takara kocin da ba kamarsa a watan na jiya. Mikel, wanda ya lashe kyauta huɗu ta gwarzon koci a firimiya a bara na takara tare da Pep Guardiola na Manchester City, bayan…
Read More
Nasarorin da matar Gwamnan Kebbi ta samu cikin kwana 100 a ofis 

Nasarorin da matar Gwamnan Kebbi ta samu cikin kwana 100 a ofis 

Daga JAMIL GULMA a Birnin Kebbi  Hajiya Zainab Nasir Idris (Nasare) matar Gwamnan Jihar Kebbi, wacce ake wa kirari da mace mai kamar maza da ke da burin canza rayuwar mabuƙata zuwa mawadata ta hanyar bayar da tallafi a inda ya dace. Kasancewar ta matar gwamna, hakan bai hana ta ayyukan da ta taso tana aiwatarwa ba kafin yanzu.   A cikin kwanaki 100 da ta yi na matar gwaman, Hajiya Nasare ta sami nasarar canza rayuwar mutane da yawa, musamman mabuƙata a faɗin jihar ta Kebbi, inda ta ba wa waɗansu damar kaiwa ga wani bagire da a baya ba…
Read More
Kamfanin Google ya naɗa ɗan Nijeriya muƙamin Mananjan Darakta na Afirka 

Kamfanin Google ya naɗa ɗan Nijeriya muƙamin Mananjan Darakta na Afirka 

Daga AMINA YUSUF ALI A ranar Talatar da ta gabata ne dai kamfanin Google ya ba da sanarwar naɗin wani ɗan Nijeriya, Alex Okosi a matsayin Manajan Darakatan Google na Afirka domin taimaka wa kasuwanci da tattalin arziki su bunƙasa.  Mataimakin Shugaban EMEA na Google, Meir Brand shi ya hayyana hakan a wani jawabi. Sannan ya ce, a yanzu Mista Okosi shi ne zai ja ragamar ayyukan Google a Afirka. Mista Brand ya ƙara da cewa, wannan muƙami kuma zai taimaka wa biliyoyin masu amfani da shafin na Google su samu ƙarin abubuwa daga gare shi.   “Alex shugaba ne na…
Read More
An tsinci gawar ɗaliba cikin rami bayan vatarta

An tsinci gawar ɗaliba cikin rami bayan vatarta

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An tsinci gawar wata ɗalibar Jami’ar Tarayya ta Oye Ekiti (FUOYE), Atanda Modupe Deborah, kwanaki biyu bayan ta ɓata. A cewar rahotanni, Deborah, wacce ɗaliba ce a sashen karatun aikin jinya, stream A, Faculty of Basic Medical Science, ta ɓata bayan ta tafi karatun daren Litinin, 4 ga Satumba, 2023. Abokan zamanta sun bayyana ɓatarta lokacin da ba ta dawo daga karatun dare ba. An tsinci gawar ta binne a wani rami mara zurfi a bayan jami’ar ba tare da idanunta ba a ranar Laraba, 6 ga watan Satumba. Da ya ke mayar da martani kan…
Read More