Editor

9513 Posts
Wolves ta naɗa Gary O’Neil sabon kocinta

Wolves ta naɗa Gary O’Neil sabon kocinta

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wolverhampton ta sanar da naɗa tsohon kocin Bournemouth, Garry O'Neil, a matsayin wanda zai horar da ita. Tuni ya amince da kwantiragin kaka uku, ya kuma maye gurbin Julen Lopetegui. An sanar da raba gari tsakanin ƙungiyar da Lopetegi a Molineu ranar Talata, kwana uku kafin fara kakar firimiya ta 2023/24. O'Neil ya ja ragamar Bournemouth zuwa mataki na 15 a teburin firimiya a bara, daga baya ta kore shi ranar 19 ga watan Yuni. Mai shekara 40, shi ne kocin Wolves na hudu cikin shekara biyu. Zai fara aiki ranar Litinin, lokacin da Wolves za…
Read More
Courtois zai yi jinya mai tsawo a Real Madrid

Courtois zai yi jinya mai tsawo a Real Madrid

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Mai tsaron ragar Real Madrid, Thibaut Courtois zai yi jinya mai tsawo a kakar bana, bayan da ya ji rauni a gwiwar ƙafarsa ta hagu. A ’yan kwanaki masu zuwa likitoci za su yi wa golan tawagar Belgium, mai shekara 31 tiyata, daga baya a fayyace kwanakin jinyar da zai yi. Courtois, wanda aka zava mai tsaron raga mafi fice a duniya a bikin kyautar Ballon d'Or a bara, ya lashe La Liga biyu tun bayan da ya koma Real a 2018. Ya buga wa Real wasa 230, wadda za ta kece raini da Athletic Bilbao…
Read More
Kirifto Karansi: Tsakanin mutanen MTFE da ƙwararru

Kirifto Karansi: Tsakanin mutanen MTFE da ƙwararru

Daga ƊANLADI Z. HARUNA Kasuwanci, musamman na yanar gizo, yana tattare da kasada da ganganci da kuma tarangahuma. Wasu ma sun ce kasuwancin intanet tamkar cinikin biri a sama ne. Don haka masu bincike suke ɗora nazarinsu akan cewa kasuwancin intanet ya sha bambam da na zahiri. Domin shi a mafi yawan lokuta, daji ne da ba shi da ƙyaure. Kowacce irin harkar intanet na ɗauke da wasu alamu da a zahiri ana iya alaƙanta su da damfara ko rashin tabbas. Ta haka idan an samu matsala, ana shan wahala kafin a warware ta. Wannan kenan. Bayyanar MTFE, ya zo…
Read More
Hukumomin Kwastam, NCC, da ma’aikatu 61 na tarayya za su fara tattara haraji ƙarƙashin inuwa guda

Hukumomin Kwastam, NCC, da ma’aikatu 61 na tarayya za su fara tattara haraji ƙarƙashin inuwa guda

Daga AMINA YUSUF ALI 'Yan kwamitin shugaban ƙasa a kan haraji da gyara al'amurran tattalin arziki na Nijeriya sun bayyana cewa, daga yanzu hukumar Kwastam da sauran hukumomi da ma'aikatu guda 62 na gwamnatin Tarayya za su daina amsar haraji kai-tsaye. Shugaban kwamitin mai suna, Taiwo Oyedele, shi ya yi wannan jawabi a wata tattaunawarsa da gidan talabijin ɗin Channels Television a wani shiri da suka saba gudanarwa duk ranar Laraba. Ya ƙara da cewa, hukumar tattara haraji ta tarayya ita ce za ta cigaba da harajin dukkan waɗannan hukumomi da ma'aikatu. Oyedele, ya bayyana cewa, Nijeriya tana daga cikin…
Read More
Matsin tattalin arziki: Masu amfani da intanet a Nijeriya sun ragu ya zuwa miliyan 159.49 – NCC

Matsin tattalin arziki: Masu amfani da intanet a Nijeriya sun ragu ya zuwa miliyan 159.49 – NCC

Daga AMINA YUSUF ALI Hukumar Sadarwa ta Nijeriya ( NCC), ta bayyana cewa, masu amfani da intanet a Nijeriya sun ragu i zuwa miliyan 159.49 daga watan Yunin 2023. Wata majiya ta bayyana cewa, kuma bisa dukkan alamu hakan yana da nasaba da matsin tattalin arzikin da ƙasar ta shiga a dalilin cire tallafin mai. A wani rahoto da hukumar ta NCC ta wallafa a shafinta na intanet, ta bayyana cewa, yanzu masu amfani da intanet ɗin sun ragu zuwa miliyan 159.49 wanda a baya suke adadin miliyan 159.59. Wato an samu raguwar masu amfani na kaso wajen 0.06 a…
Read More
Shin shugaba Bazoum zai koma karaga?

Shin shugaba Bazoum zai koma karaga?

Tare Da NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Idan mu ka shiga nazarin yadda lamura su ke a jamhuriyar Nijar za mu gane sojojin nan ba su da niyyar sauka daga mulki don dawo da gwamnatin dimokraɗiyya ta shugaba Muhammad Bazoum. Kazalika amfani da karfin soja na bukatar gwanaye da za su iya yin hakan ta yaƙi da dabarun kifar da jutin mulki ba yaƙi da ƙasar Nijar ba. Kafin ma na yi nisa zan ce a wajen Allah Maɗaukakin Sarki mai ba da mulki wannan abu ne mai sauƙi. Mu duba misalin yadda a ka kare dimokraɗiyya a Gambia bayan da tsohon…
Read More
Kawar da bautar da ƙananan yara

Kawar da bautar da ƙananan yara

Akwai wani al'amari mai matuƙar tayar da hankali da ban tausayi kan yadda ake amfani da yara masu ƙananan shekaru maza da mata don yin aiki ko bauta a gidaje da sauran wurare da suka haɗa da shaguna, otel-otel, wuraren kwana na manyan makarantu ko ɗakunan kwanan ɗalibai a jami’o’i. Akasarin yaran ’yan ƙasa da shekaru 15 ne kuma ana ɗaukarsu ne da nufin yin aikace-aikacen da suka haɗa da shara, wanke-wanke, wanki, goge-goge, ɗebo ruwa da rainon jarirai da kula da yayayyun yara da makamantansu. Mafi yawan yaran ana kawo su cikin birni daga ƙauyuka lokaci zuwa lokaci, ta…
Read More
Barcelona da Chelsea na rububin ƙulla yarjejeniya da Neymar

Barcelona da Chelsea na rububin ƙulla yarjejeniya da Neymar

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Makomar Neymar idan har ya rabu da PSG na cigaba da kasancewa cikin rashin tabbas a daidai lokacin da ɗan wasan tare da ƙungiyar ta sa suka amince da Shirin rabuwar nan ba da jimawa ba. Sai dai mai yiwuwa burin ƙungiyoyin Barcelona da Chelsea waɗanda ke son ƙulla yarjejeniya da ɗan wasan ya gaza cika, saboda ƙalubalen da kowannensu ke fuskanta. A ɓangaren Chelsea, a yayin da ta kasance ƙungiyar da za fi dacewa da samun sauƙin sayen Neymar, ba lallai bane ɗan wasan ya amince da tayin komawa gare ta, la’akari da cewar ba…
Read More
Gwamna Raɗɗa ya yi wa jami’an tsaro rakiya don kai samame maɓoyar ‘yan ta’adda

Gwamna Raɗɗa ya yi wa jami’an tsaro rakiya don kai samame maɓoyar ‘yan ta’adda

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Raɗɗa a ranar Talata da dare ya bi sahun jami’an tsaro daban-daban na jihar domin kai samame mavoyar ‘yan ta’addan da ke ta’addancin zaman lafiya da kwanciyar hankali a cikin birnin Katsina. A wata sanarwa da Babban Sakataren Yaɗa Labarai na CPS, Ibrahim Kaula Mohammed ya fitar ga Gwamnan Katsina, ya ce Raɗɗa da kansa ya jagoranci jami’an tsaro suka kai samame maɓoyar ‘yan ta’addan, a daren ranar Talata da misalin ƙarfe 10 zuwa 11:30 na dare. Kamar yadda sanarwar ta bayyana, maboyar da Gwamnan da tawagarsa ta…
Read More
Sojojin juyin mulki a Nijar sun naɗa ministoci duk da gargaɗin ECOWAS

Sojojin juyin mulki a Nijar sun naɗa ministoci duk da gargaɗin ECOWAS

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Masu juyin mulkin jamhuriyar Nijar sun kafa sabuwar gwamnati duk da umarnin Ƙungiyar Ƙaya Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS). Shugabannin sojojin sun sanar da sabbin ministoci 21 a wata doka da aka karanta a gidan talabijin na ƙasar. Wannan dai na zuwa ne gabanin wani taron gaggawa da shugabannin ƙungiyar ECOWAS ta Yammacin Afirka suka yi kan juyin mulkin da aka yi a Nijar, bayan da hafsoshin sojin ƙasar suka bijirewa wa'adin da aka ba su na dawo da zavavven shugaban ƙasar. Janar Abdourahamane Tchiani ne ya sanar da sabuwar gwamnatin Nijar, wanda…
Read More