30
Jun
Daga BASHIR ISAH Uwargidan Gwamnan Jihar Nasarawa, Hajiya Salifat Sule, ta jaddada buƙatar da ke akwai iyaye su zamo masu saka ido matuƙa a kan tarbiyyar 'ya'yansu don amfnin al'umma baki ɗaya. Salifat ta yi wannan kira ne a jawabin da ta yi wa alhazan jihar sa'ilin da ta kai musu ziyara ranar Alhamis a Mina a ƙasar Saudiyya. Ta ce, aikin lura da tarbiyyar 'ya'ya bai kamata ya a bar shi a hannun iyaye mata kaɗai ba, don haka ta buƙaci iyaye maza da su kasance masu mara wa matan baya yadda ya kamata a fagen bai wa yara…
