Editor

9513 Posts
‘Babu hannu Gumi a lamarin ceto ɗaliban Kuriga’ — Gwamna Sani

‘Babu hannu Gumi a lamarin ceto ɗaliban Kuriga’ — Gwamna Sani

Daga BASHIR ISAH Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani, ya bayyana cewa babu hannun malamin nan na Islama, wato Sheikh Ahmad Gumi a lamarin ceto ɗaliban firamaren da aka yi. Uba Sani ya faɗi hakan ne a wani shirin da Tashar Channels Television ta yi da shi a ranar Lahadi. Yana mai cewa, sojoji ne suka ceto yara 137 da aka kuɓutar da su bayan da 'yan bindiga suna yi garkuwa da su a ranar 7 ga Maris a yankin Ƙaramar Hukumar Chikun a jihar. Ya ƙara da cewa, an kuɓutar da yaran ne inda aka kai su aka ɓoye a…
Read More
An ƙara kuɗin Hajjin bana zuwa N8m

An ƙara kuɗin Hajjin bana zuwa N8m

Daga BASHIR ISAH Hukumar Hajji ta Ƙasa (NAHCON) ta ce an samu ƙari a kuɗin Hajjin bana inda a yanzu maniyyaci zai biya Naira miliyan 8 domin tafiya aikin Hajjin 2024. Sanarwar da NAHCON ta fitar ta bakin Kakakinta, Hajiya Fatima Sanda Usara a ranar Lahadi, ta ce, tsayayyen farashin da maniyyatan bana za su biya shi ne N8, 225, 464.74 ga waɗanda suka fito daga yankin Adamawa/Borno. Fatima ta ce, "sabon biya daga yankin Arewa zai biya N8, 254, 464.74, sannan daga yankin Kudu za su biya N8, 454, 464.74." Ta ƙara da cewa, ana sa ran dukkanin rukunonin…
Read More
Yadda muke ƙoƙarin sauya halayyar ’yan daba a Jos – Ƙungiyar ‘Jos Peace Vanguar’

Yadda muke ƙoƙarin sauya halayyar ’yan daba a Jos – Ƙungiyar ‘Jos Peace Vanguar’

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Garin Jos, babban birnin Jihar Filato na ɗaya daga cikin manyan biranen arewacin ƙasar nan da suke fama da matsalar taɓarɓarewar tsaro, da ya shafi yadda ƙungiyoyin matasa 'yan daba suke ɗaukar makamai suna shiga anguwanni suna sare-saren kan-mai-uwa-da-wabi da ƙwacen wayoyi. Yawaitar wannan masifa ce ta zaburar da mutane irin su MALAM NURA ALHASSAN da masu ra'ayi irin nasa suka tashi tsaye don ganin yaran da suke wannan aika-aika sun dawo kan hanya, da samar da tsaro a cikin al'umma. Wanne ƙalubale irin wannan aikin sa-kai ke fuskanta? Wacce nasara aka samu? Kuma wanne tallafi…
Read More
Turmutsitsin rabon zakka a Bauchi: Adadin waɗanda suka mutu ya ƙaru

Turmutsitsin rabon zakka a Bauchi: Adadin waɗanda suka mutu ya ƙaru

Daga BASHIR ISAH Hukumomi a Jihar Bauchi sun ce, adadin waɗanda suka rasa rayukansu a wajen rububin karɓar zakka a Jihar Bauchi ya ƙaru. A ƙarshen mako ne aka samu turmutsitsi a wajen wani rabon zakka lamarin da ya yi sanadiyar salwantar rayukan wasu da suka je karɓar zakkar. Ya zuwa yanzu, mutum shida ne aka tabbatar da sun mutu bayan da aka ɗebe su zuwa Asibitin Koyarwa na Jami'ar Abubakar Tafawa Balewa. Kakakin rundunar 'yan sanda ta Jihar Bauchi, Ahmed Wakilin ya tabbatar da haka sa'ilin da yake yi wa manema labarai ƙarin haske kan lamarin a ranar Litinin.…
Read More
Ku guji sayar da motocinku ɗauke da lamba – gargaɗin FRSC ’yan Nijeriya

Ku guji sayar da motocinku ɗauke da lamba – gargaɗin FRSC ’yan Nijeriya

Daga BASHIR ISAH Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Ƙasa (FRSC) ta gargaɗi ’yan Nijeriya da su guji sayar da motocinsu ɗauke da lamba. Sabuwar shugabar hukumar a Jihar Ribas, Elizabeth Akinlade ce ta yi wannan gargaɗi yayin ziyarar da ta kai cibiyar ‘yan jarida reshen Jihar Ribas da ke Calabar, babban birnin jihar. Elizabeth ta ce an yi wannan gargaɗi ne domin kare mutane daga sayar da abuwan hawansu ga mutanen da ba su dace ba ko ɓata-gari. Ta ci gaba da cewa, mai asalin motar za a kama a duk lokacin da aka yi amfani da motar da ya saida…
Read More
Saƙo zuwa ga iyayen gida

Saƙo zuwa ga iyayen gida

Daga FATIMA GARBA DANBORNO Saƙona zuwa ga mata shi ne, su rage dogon buri. Su gane auren mai kuɗi ba shi ba ne ƙarshen auren ba. Idan har suka ce sun dage sai mai kuɗi, ƙarshe sai kin ga an zo ana danasani. Su yi iya yinsu su dage da addu'a babu dare babu rana, akan Allah ya yi masu zaɓi da mafi alkhairi. Sau tari auren wani mai kudin ba alkhairi ba ne. Amma daga lokacin da mace ta kai goshinta ƙasa ta yi addua akan Allah ya yi mata zaɓi da miji na gari mai tsoron Allah, mai…
Read More
Tinubu ya yi murna da ceto ɗaliban Kuriga

Tinubu ya yi murna da ceto ɗaliban Kuriga

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya yi farin ciki da ceto wasu ɗaliban Kuriga a Jihar Kasuna da jami'an tsaro suka yi, tare bai wa 'yan Nijeriya tabbacin cewar gwamnatinsa za ta tabbatar da tsaro a makarantu. Hakan na ƙunshe ne cikin sanarwar da ya mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Ajuri Ngelale, ya fitar ranar Lahadi a Abuja. “Shugaban Ƙasa ya bai wa 'yan Nijeriya tabbacin gwamnatinsa na amfani da ingantattun dabaru wajen ganin an samu tsaro mai inganci a makarantunmu," in ji sanarwar. Kimanin ɗalibai 287 ne 'yan bindiga suna yi awon gaba da su a…
Read More
Tsaro: Gwamnatin Kano ta yi alƙawarin taimaka wa Gwamnatin Tarayya kan yaƙi da ta’addanci da satar mutane

Tsaro: Gwamnatin Kano ta yi alƙawarin taimaka wa Gwamnatin Tarayya kan yaƙi da ta’addanci da satar mutane

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Gwamnatin jihar Kano ta lashi takobin mara wa shirin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu baya na daƙile illolin rashin tsaro da ke dagula zaman lafiya a kasar nan. Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi wannan alƙawarin ne a ranar Juma’a a lokacin da ya karɓi baƙuncin Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan 'Yan Ƙasa, Alhaji Muhammad Idris a ziyarar ban girma da ya kai gidan gwamnati. A wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, gwamnan ya ce ya dace a hada kai da gwamnatin tsakiya domin daƙile…
Read More
Mutum huɗu sun mutu wajen turmutsitsin rabon zakka a Bauchi

Mutum huɗu sun mutu wajen turmutsitsin rabon zakka a Bauchi

Wasu mutum huɗu sun riga mu gidan gaskiya sakamakon turmutsitsin da ya auku a wajen raba wa jama'a zakka a jihar Bauchi. Lamarin ya faru ne ranar Lahadi da misalin ƙarfe 12 na rana a harabar hedikwatar kamfankn Shafa Holdings Company plc da ke hanyar Jos a jihar. MANHAJA ta kalato cewa, wani matashi da ya jikkata a wajen turmutsitsin na kwance a Asibitin Koyarwa na Jami'ar Abubakar Tafawa Balewa da ke Bauchi ana yi masa magani. Kakakin rundunar 'yan sandan jihar, Ahmed Wakili, ya tabbatar da aukuwar haka ga jaridar News Point Nigeria.
Read More