Editor

9513 Posts
Kuriga: Ɗalibai 137 aka ceto – Ofishin Tsaro

Kuriga: Ɗalibai 137 aka ceto – Ofishin Tsaro

Daga BASHIR ISAH Rundunar sojojin Nijeriya ta bayyana adadin ɗaliban Kuriga da aka ceto daga hannun ‘yan bindiga. An yi garkuwa da ɗaliban ne a makarantar firamare da sakandare na yankin Kuriga da ke cikin Ƙaramar Hakumar Chikun a Jiahar Kaduna. Cikin sanarwa mai ɗauke da sa hannun Manjo-Janar Edward Buba, rundunar ta ce ɗalibai kimanin 137 ne aka yi nasarar cetowa, saɓabin abin da wasu rahotanni suka rawaito. Kimanin ɗalibai 287 ne ’yan bindiga suka yi awon gaba da su ranar 6 ga Maris a yankin Kuriga, lamarin da ya tada hankalin jama’a a ciki da wajen Nijeriya. Sanarwar…
Read More
‘Yan bindiga sun kashe masu Sallar Tarawihi a Katsina

‘Yan bindiga sun kashe masu Sallar Tarawihi a Katsina

Daga UMAR GARBA a Katsina Waɗansu 'yan bindiga dauke da makamai sun yi dirar mikiya a ƙauyen Mai ruwa dake cikin karamar hukumar Faskari ta jihar Katsina, inda suka nufi gidan wani babban ɗan kasuwa kuma ɗan siyasa mai suna Alhaji Lado Mai ruwa, suka harbe shi tare da wani makocinsa har lahira daga bisani suka sace iyalinsa. Lamarin ya faru a ranar Asabar da dare lokacin da marigayan tsaka da Sallar Tarawihi. Ɗaya daga cikin 'ya 'yan marigayin ya tabbatar da kashe mahaifin na su tare da wani maƙwabcinsa Sani Autan Haris. Rahotanni da jaridar Manhaja ta samu sun…
Read More
Gidauniyar Ɗangote ta ƙaddamar da tallafin kayan abinci a Kano

Gidauniyar Ɗangote ta ƙaddamar da tallafin kayan abinci a Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci ƙaddamar da rabon tallafin kayan abinci da Gidauniniyar Dangote za ta raba wa al’ummar Nijeriya domin rage musu raɗaɗin rayuwa da suke fuskanta. Da yake ƙaddamar da rabon tallafin a gidan Gwamnatin Kano a ranar Asabar, Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya yi kira ga kwamitin da za su gudanar da rabon kayan abincin su zamo masu gaskiya da riƙon amana, tare da tabbatar da tallafin ya isa ga mabuƙatan da aka tanadi abincin domin su. Yusuf ya kuma ce tuni tallafin kayan abincin ya isa ga…
Read More
EFCC ta ƙwato wa ’yan fanshon Kano gidajen Kwankwasiyya da tsofaffin gwamnoni suka sayar

EFCC ta ƙwato wa ’yan fanshon Kano gidajen Kwankwasiyya da tsofaffin gwamnoni suka sayar

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arzikin Ƙasa Ta'annati, EFCC, ta shiyyar Abuja, ta miqa takardun gidaje 324 da aka ƙwato na ’yan fansho na Jihar Kano ga waɗanda abin ya shafa. Wannan cigaban dai ya biyo bayan wani bincike da hukumar EFCC ta gudanar kan wani asusun fansho na Naira Biliyan 4.1 da gwamnatocin Jihar Kano da suka shuɗe guda biyu suka hana ’yan fansho. Binciken Hukumar EFCC ya biyo bayan koke da wata qungiya mai suna “Concerned Kano State Workers and Pensioners” ta shigar a kan zargin karkatar da kuɗaɗen ’yan fansho a…
Read More
Ɗaliban Kuriga sun shaƙi iskar ‘yanci

Ɗaliban Kuriga sun shaƙi iskar ‘yanci

Daga BASHIR ISAH Bayanai daga Jihar Kaduna na nuni da cewa, ɗaliban firamaren da aka yi garkuwa da su kwanan baya a yankin Kuriga a jihar, sun shaƙi iskar 'yanci. Gwamnan Jihar, Sanata Uba Sani, shi ne ya ba da sanarwar hakan a shafinsa na Facebook ranar Asabar da tsakar dare Idan za a iya tunawa, MANHAJA ta rawaito a ranar 8 ga Maris wasu 'yan bindiga suka kai hari yankin Kuriga, cikin Ƙaramar Hukumar Chilun a jihar Kaduna, inda suka yi awon gaba da yara sama da 200. Sai dai Gwamnan bai yi wani cikakken bayani kan sako yaran…
Read More
Jihohin Kebbi, Sakkwato, Oyo da Ebonyi na kan gaba a yaran da ke gararamba a titi – Rahoto

Jihohin Kebbi, Sakkwato, Oyo da Ebonyi na kan gaba a yaran da ke gararamba a titi – Rahoto

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Nijeriya na fuskantar mawuyacin hali na rashin ilimi, inda miliyoyin yara ke rasa ‘yancinsu na samun ilimi. Manhaja ta lura da cewa duk da karatun firamare a hukumance na ‘kyauta’ kuma wajibi ne, yara da yawa ba sa zuwa makaranta a faɗin jihohi. Wannan rashin samun ilimi yana kawo cikas ga ci gaban mutum da ci gaban ƙasa baki ɗaya. Idan dai ba a manta ba, batun yaran da ba sa zuwa makaranta ba ya watsu a duk faɗin Nijeriya, domin kuwa rahotanni da bayanai sun nuna an sha bayar da gagarumin bambanci tsakanin…
Read More
Mai yiwuwa Tinubu ya sanar da albashi mafi ƙaranci a Ranar Ma’aikata ta Duniya

Mai yiwuwa Tinubu ya sanar da albashi mafi ƙaranci a Ranar Ma’aikata ta Duniya

Daga BASHIR ISAH Alamu bayyanannu na nuni da cewa, akwai yiwuwar Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya sanar da sabon albashi mafi ƙaranci a ranar 1 ga watan Mayu mai zuwa. Kuma zai yi hakan ne albarkacin bikin Ranar Ma'aikata ta Duniya wanda akan gudanar a ranar farko ga watan Mayu duk shekara. Majiyarmu ta ce, Kwamitin Albashin na Ƙasa na aiki tukuru don tabbatar da an cimma dukkan sharuɗɗan da aka shimfiɗa dangane da sabon albashi mafi ƙarancin. Majiya ta kusa da kwamitin ta ce, "Kwamitin Albashi zai sake zama ya zuwa makon gobe. Zama ne wanda kwamitin zai karɓi…
Read More
Na fi tunanin sojojin haya ne suka kashe sojoji 17 a Delta – Akpabio

Na fi tunanin sojojin haya ne suka kashe sojoji 17 a Delta – Akpabio

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Godswill Akpabio ya bayyana cewa mutanen da suka yi wa sojojin qasar 17 kisan gilla a jihar Delta na iya zama sojojin haya ba wai mutanen yankin Neja Delta ba. Ya bayyana haka ne a zaman majalisar na ranar Talata, kwana biyar kenan bayan faruwar mummunan harin. Akpabio ya yi tsokacin ne lokacin da majalisar ta yanke shawarar kafa kwamiti domin gano abin ya janyo kashe sojojin. Ya ce "Ba na son na yanke hukunci cewa waɗannan mutanen daga yankin Neja Delta suka fito saboda muna mutunta mata da zama…
Read More
Sojoji sun kashe ‘yan bindiga 106 a mako guda — DHQ

Sojoji sun kashe ‘yan bindiga 106 a mako guda — DHQ

*Ana ci gaba da farautar waɗanda suka kashe sojoji 18 a Delta Daga BASHIR ISAH Babban Ofishin Tsaro (DHQ) da ke Abuja ya ce ba zai yi ƙasa a gwiwa ba wajen farauto ɓata-garin da suka kashe sojoji a Jihar Delta. Mai magana da yawun rundunar, Manjo-Janar Edward Buba ne ya bayyana haka a ranar Juma'a. Ya ce faɗi-tashin da sojoji ke ci gaba da yi na yaƙi da ta'addancin, suna yi ne don amfanin ƙasa. A cewarsa, ”A ci gaba da ayyukan yaƙi da matsalolin tsaro sojoji sun ceto mutane da dama waɗanda aka yi garkuwa da su tare…
Read More
Sakamakon cire tallafin mai: Adadin fetur da ake amfani da shi a Nijeriya ya ragu da lita biliyan guda – Idris

Sakamakon cire tallafin mai: Adadin fetur da ake amfani da shi a Nijeriya ya ragu da lita biliyan guda – Idris

Daga BASHIR ISAH Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan 'Yan Ƙasa, Muhammad Idris, ya bayyana cewa, adadin man fetur da ake amfani da shi a Nijeriya ya ragu da lita biliyan ɗaya, kwatankwacin kashi 53 na adadin man da ake amfani da shi gabanin cire tallafin mai. A cewarsa, hakan ya faru ne sakamakon tallafin fetur da gwamanti ta cire a watan Mayun Bara. Ya bayyana haka ne a wajen buɗe-baki tare da 'yan jarida da aka shirya kwanan nan a Kano. Idris ya ce, la'akari da yawan raguwar amfani da fetur da aka gani, hakan na nuni da…
Read More