Editor

9513 Posts
Hedikwatar Tsaro na neman su Dogo Gide, Simon Ekpa, Bello Turji da sauransu ruwa a jallo

Hedikwatar Tsaro na neman su Dogo Gide, Simon Ekpa, Bello Turji da sauransu ruwa a jallo

Daga BASHIR ISAH A ƙalla 'yan bindiga, ɓarayin daji da tsageru 97 ne Babban Ofishin Tsaro da ke Abuja ya bayyana a matsayin waɗanda yake nema ruwa a jallo. Ofishin ya ce waɗanda yake neman suna da hannu wajen aikata manyan laifuka da tada zaune tsaye a sassan ƙasa. Har wa yau, waɗanda lamarin ya shafa ya haɗa da shugaban wani ɓangare na tsagerun IPOB, wato Simon Ekpa. Mai magana da yawun rundunar soji, Manjo-Janar Edward Buba, shi ne ya bayyana sunaye da hotun waɗanda rundunar ke farautarsu. MANHAJA ta rawaito a makon jiya cewa, Babban Ofishin tsaro na shirin…
Read More
Gwamnati ta dakatar da karɓar kashi 25 kan motocin da aka shigo da su ba bisa ƙa’ida ba

Gwamnati ta dakatar da karɓar kashi 25 kan motocin da aka shigo da su ba bisa ƙa’ida ba

Daga BASHIR ISAH Ministan Tattalin Arziki kuma mai sanyo ido kan fannin kuɗi, Mr. Wale Edun, ya unarci Hukumar Kwastom da ta dakatar da karɓar kashi 25 daga hannun masu shigo da motoci daga ƙetare ba bisa ƙa'ida ba. Kakakin hukumar na ƙasa, Abdullahi Maiwada, shi ne ya bayyana haka cikin sanarwar da ya fitar a ranar Juma'a. Kwanan nan ne Gwamnatin Tarayya ta ba da sanarwar buɗe dama na tsawon kwana 90 don shigowa da wasu keɓaɓɓun motoci. Da ma dai hukumar kan amshi kashi 25 kan motocin da aka shigo da su ba bisa ƙa'ida ba a matsayin…
Read More
Gyaran masallacin Idi: Sanata Barau zai kashe sama da Naira miliyan 400 a Bichi

Gyaran masallacin Idi: Sanata Barau zai kashe sama da Naira miliyan 400 a Bichi

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Sanatan Kano ta Arewa kuma mataimaki shugaban majalisar datttawa ta ƙasa, Barau Jibrin Maliya, ya bada umarni fara aikin zagaye babban masallaci Idi na Masarautar Bichi tare da saka interlocks. Da yake jawabi lokacin ƙaddamar da aikin jagoran tafiyar gidan Sanata Barau I. Jibrin na ƙaramar hukumar Bichi Sani Muƙaddas Barden Bichi wanda Alh. Garba Ɗandawaki ya wakilta, ya ce Sanatan ya bada umarnin yin aikin ne saboda kishinsa ga addinin Musulunci. Ya ce ba yi mamakin irin wannan aikin Allah da Sanata Barau Jibrin zaiyi ba, domin daman aikin sa ne ya saba a…
Read More
Yanzu-yanzu: An ceto ɗaliban tsangaya da aka yi garkuwa da su a Sakkwato

Yanzu-yanzu: An ceto ɗaliban tsangaya da aka yi garkuwa da su a Sakkwato

Kimanin makonni biyu da suka gabata ne aka 'yan bindiga suka sace yaran su 15 a wata makatrantar tsangaya da ke kauyen Gidan Bakuso a yankin Kaeamae Hukumar Gada. MANHAJA ta kalato cewa, 'yan bindigar da suka yi awon gaba da yaran sun bukaci a a biya su Naira miliyan 20 kafin su sako yaran. Shigaban makaranar, Liman Abubakar, shi ne ya bayyana wa majiyarmu haka a ranar Talata. Ya zuwa hada wannan labari, babu wani cikakken bayani kan ko sai da aka biya kudin fansa kafin aka sako yaran ko kuwa a'a.
Read More
’Yan sanda sun yi karar Jaruma Amal kotu bayan kotu ta wanke ta

’Yan sanda sun yi karar Jaruma Amal kotu bayan kotu ta wanke ta

Daga AISHA ASAS  Rundunar ’Yan Sandan Nijeriya Shiyya ta Ɗaya (wato Zone 1) ta kai ƙarar fitacciyar jaruma a Kannywood, Amal Umar, gaban kotu kan zargin bayar da toshiyar baki ga wani ɗan sanda da ke binciken ta kan zargin aikata wata almundahanar kuɗi da ake zargin da sa hannunta a ciki, duk da cewa, kotu ta wanke jarumar tun a watannin baya. A jiya Alhamis ne aka gurfanar da jarumar a kotun Majistare mai lamba 24 da ke Jihar Kano.  Da yake jawabi a gaban manema labarai, Kakakin Rundunar 'Yan Sanda Na Shiyya Ta Ɗaya, CSP Bashir Muhammad, ya…
Read More
Ramadan: Dubban ‘yan Nijeriya za su rasa Umara sakamakon matakin hana biza da Saudiyya ta ɗauka — Rahoto

Ramadan: Dubban ‘yan Nijeriya za su rasa Umara sakamakon matakin hana biza da Saudiyya ta ɗauka — Rahoto

Daga BASHIR ISAH Akwai yiwuwar bana 'yan Nijeriya da dama ba za su samu yin Hajjin Umar ba a wannan wata na Ramadana. Hakan ba ya rasa nasaba da matakin da Ƙasar Saudiyya ta ɗauka na dakatarwa ko taƙaita da bayar da bizar zuwa yin Umara a ƙasar. Wannan al'amari ya tada hankalin jama'a musamman masu niyyar zuwa Umara domin ninka ibadarsu a watan Azumin Ramdan. Haka su ma kamfanonin shirya tafiye-tafiye zuwa Hajji da Umara sun nuna damuwarsu kan matakin wanda tuni ya haifar musu da asara sakamakon sauke musu bukin na masaukan da suka kama a biranen Makka…
Read More
Falastinawa a Gaza na fama da matsananciyar yunwa – Ofishin jakadancinsu a Nijeriya

Falastinawa a Gaza na fama da matsananciyar yunwa – Ofishin jakadancinsu a Nijeriya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ofishin Jakadancin Falastinu a Nijeriya ya bayyana cewa, a rana ta 167 na yaƙin kisan ƙare dangi da ake yi wa al'ummar Falastinu, mutanen Gaza mata da qananan yara na fama da matsananciyar yunwa, rashin ingantaccen kiwon lafiya da sauran wahalhalu. Jakadan Falastinu a Nijeriya, Abu Shawesh ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwar da ya fitar a ranar Alhamis.  Sanarwar ta ce, "Sakatare Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya, Antonio Guterres da Babban jami'in kare haqqin bil'adama na Majalisar Ɗinkin Duniya Volker Turk sun bayyana irin matsananciyar wahalar da ake fama da ita a garin…
Read More
Makamashi: A dawo daga rakiyar talakan Nijeriya

Makamashi: A dawo daga rakiyar talakan Nijeriya

Tare da BASHIR MUDI YAKASAI Masana tarihi sun tabbatar da dalilai uku waɗanda sune tushen hulɗa a tsakanin nahiyoyin duniya. Dalilin farko shine ƙaurace-ƙauren mafarauta dana makiyaya da kuma masunta. Na biyu tafiye-tafiyen fatake na ruwa dana hamadar sahara da kuma dazuka. Na uku shine gudun hijira don gujewa wasu masifu kamar girgizar ƙasa ko aman duwatsu na wuta ko ambaliyar ruwa ko gobarar daji ko kuma yaƙi da kuma yunwa a dalilin fari. Amma dalilin zuwan Turawan yamma, wato ƙasashen Birtaniya da Faransa da Italiya da Potugal da Sapaniya da Jamus wannan nahiya ta Afrika shine fashi na al’ummarta…
Read More
An sace fasinjoji a hanyar Ƙanƙara dake Katsina 

An sace fasinjoji a hanyar Ƙanƙara dake Katsina 

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Wasu ’yan bindiga sun yi sace fasinjoji da dama a wani harin da suka kai a Ƙaramar Hukumar Ƙanƙara da ke Jihar Katsina. Lamarin ya faru ne a jiya Alhamis bayan da ’yan bindigar dajin suka tare wata mota ƙirar bas mai cin mutane 18 mai lamba 14B-300-KT cike maƙil da fasinjoji mallakar hukumar kula da sufuri ta Jihar Katsina (KSTA). Wani ganau ya shaida wa majiyarmu ta wayar tarho cewa, galibin fasinjojin da ke cikin motar sun fito ne daga Ƙaramar Hukumar Funtuwa a kan hanyarsu ta zuwa Katsina, Babban Birnin Jihar Katsina.…
Read More
Minista ya tono yadda aka riƙe wa gwamnati kuɗin samar da mitar lantarki tsawon shekara 21

Minista ya tono yadda aka riƙe wa gwamnati kuɗin samar da mitar lantarki tsawon shekara 21

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ministan Kula da Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu, ya bayyana cewa wani kamfani mai zaman kansa, Messrs Ziklagsis ya riƙe har Naira biliyan 32 da aka biya a asusunsa a shekarar 2003 domin samar da mitoci miliyan uku da aka riga aka biya. Ministan, a cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin sadarwa da hulɗa da manema labarai, Bolaji Tunji, ya fitar, ya ce gwamnatin tarayya ta ƙulla yarjejeniya da Messrs Ziklagsis Network Limited da Unistar International a shekarar 2003 kan samar da mitoci miliyan uku don rabon wutar lantarki…
Read More