Editor

9513 Posts
Gina al’umma: Tsakaninmu da Gwamna Buni sai godiya – Hon. Lawan Bukar

Gina al’umma: Tsakaninmu da Gwamna Buni sai godiya – Hon. Lawan Bukar

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban riƙo na Ƙaramar Hukumar Bursari a Jihar Yobe, Hon. Lawan Bukar ya bayyana cewa ba su da abinda za su ce wa gwamnan jihar Mai Mala Buni sai sam-barka, domin a cewarsa yana iyakacin ƙoƙarinsa na ganin ya sauke nauyin da al'ummar jihar ta ɗora masa. Bukar ya ce Gwamna Buni ya tallafa wa kananan hukumomin jihar wajen ƙarfafa wa da inganta rayuwar jama'a musamman masu ƙaramin ƙarfi da gidajen marayu; samar da aikin yi ga matasa a ƙaramar hukumar Bursari da suka haɗa da: Samar da ingantattun cibiyoyin kiwon lafiya a cikin…
Read More
Kayan miliyoyin Naira sun kone a gobarar kasuwar Legas

Kayan miliyoyin Naira sun kone a gobarar kasuwar Legas

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kayayyaki da darajarsu ta kai na miliyoyin Naira sun kone kurmus a ranar Larabar da ta gabata, yayin da wata gobara ta tashi a wasu shaguna a sashen Nnamdi Azikiwe da Docemo na Kasuwar Idumota a Jihar Legas. Gobarar ta shafi gine-gine guda uku da suka haɗa da benaye biyu da wani gini mai hawa uku a kasuwar waɗanda suka shahara  wajen sayar tufafi da jaka da takalma. Hukumar kashe gobara ta jihar Legas da sauran masu bada agajin gaggawa sun isa wurin, inda suka yi ta koƙarin aikin kashe gobarar. "Hukumomin kashe gobara a Ebute…
Read More
Tinubu zai tsige ministocin da suka gaza kataɓus

Tinubu zai tsige ministocin da suka gaza kataɓus

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban Nijeriya Bola Tinubu yana shirin fara wani tsari mai matakai uku domin tantance ƙoƙarin ministoci, shugabannin ma’aikatu da hukumomin gwamnati. Manufar ita ce samar da wani shafi da zai ba jama'a damar yin bayanai game da koƙarin ministocin da ba da shawarar waɗanda za a riƙe da waxanda za a kora. Wannan yunkuri na zuwa ne yayin da Gwamnatin Tinubu ke tunkarar bikin cika shekara gyda a kan madafun iko a ranar 29 ga Mayu, 2024. Wasu majiyoyi masu ƙarfi a fadar shugaban kasa sun ce Shugaban kasar Tinubu zai ƙaddamar da wannan shafi ne…
Read More
Amusan ta lashe tambarin zinare a gasar tseren Afrika

Amusan ta lashe tambarin zinare a gasar tseren Afrika

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Sarauniyar wasannin guje-guje ta Nijeriya, Tobi Amusan, ta cika burin magoya bayanta bayan da ta lashe tambarin zinare a tseren gudu na mita 100 a gasar kofin Afrika da ke ci gaba da gudana a ƙasar Ghana. Amusan, wadda ita ce ke riƙe da kambun tseren mita 100 na duniya, ta kasance wadda aka fi so a gasar, an nuna mata ƙauna bayan ya doke sauran abokan hamayyarta a karo na farko a tsaren. A karo na biyu bayan an harba bindigar farawa, Amusan ba ta tsaya sanya ba, inda ta yi nasara a cikin sauƙi…
Read More
Adadin waɗanda aka kashe a Gaza ya ƙaru zuwa 31,819 — Abu Shawesh

Adadin waɗanda aka kashe a Gaza ya ƙaru zuwa 31,819 — Abu Shawesh

Daga BASHIR ISAH Ofishin jakadancin Falasɗin a Nijeriya, ya bayyana cewa yazu ran Laraba, 20 ga Maris, 2024 adadin Falasɗinawa da aka kashe Gaza ya kai 31,819, yayin da 73,934 sun jikkata, sannan kimanin mutum 8,500 sun ɓace ba tare da an san inda suke ba. Jakadan Falasɗin a Nijeriya, Abdullah M. Abu Shawesh, shi ne ya bayyana haka a cikin sanarwar manema labarai da ya fitar ranar Alhamis. Jakadan ya ce baya ga kisan kiyashi da yankin Gaza ke fuskanta daga Isra'ila, yankin na kuma fama da matsanancin ƙarancin abinci, wanda a cewarsa wannan shi ne irinsa na farko…
Read More
‘Ban fuskanci wata matsala ba wajen sauya jinsina’ – Bobrisky

‘Ban fuskanci wata matsala ba wajen sauya jinsina’ – Bobrisky

Daga BASHIR ISAH Matashin ɗan Nijeriyar nan da ya sauya jinsinsa zuwa mace, wato Bobrisky, ya ce komai ya tafi daidai na aikin sauya masa jinsi da aka yi daga namiji zuwa mace. A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Instagram, Bobrisky ya bayyana farin cikinsa kan yadda aka yi masa aiki cikin nasara, yana mai cewa babu wata matsala da ya fuskanta a yayin aikin. A cikin saƙon nasa, ya bayyana godiyarsa ga likitocinsa na gida da ƙetare bisa ƙoƙarin da suka yi wajen sauya masa jinsi zuwa mace. Majiyarmu ta rawaito Bobrisky na cewa, “Komai na…
Read More
Matsalolin Nijeriya za su gushe ba da daɗewa ba – Idris

Matsalolin Nijeriya za su gushe ba da daɗewa ba – Idris

Daga BASHIR ISAH Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan 'Yan Ƙasa, Mohammed Idris, ya yi kira ga 'yan Nijeriya da su ƙara haƙuri sannan samu yaƙini game da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu saboda ƙoƙarin da take yi wajen magance matsalolin da suka addabi ƙasa. Idris ya ce gwamnati na aiki ba dare ba rana wajen daidaita lamurran ƙasa, tare da cewa za a shawo kan ƙalubalenbda suka addabi ƙasa nan ba da daɗewa ba. Ministan ya yi wannan kira ne a wajen taron buɗe-baki tare da 'yan jarida wanda Ma'aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kan 'Yan Ƙasa ta…
Read More
Gwamnati ta lissafa Mamu da wasu mutum 14 a matsayin masu ɗaukar nauyin ta’addanci

Gwamnati ta lissafa Mamu da wasu mutum 14 a matsayin masu ɗaukar nauyin ta’addanci

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ta lissafa Tukur Mamu tare da wasu mutum 14 a matsayin masu ɗaukar nauyi ayyukan ta’addanci a ƙasa. Sashen tattara bayansn sirri kan hada-hadar kuɗi (NFIU) ya bayyana sunayen  mutum 15 da lamarin ya shafa, da suka haɗa da wasu mutum tara da cibiyoyin canji (BDC) shida da uma wani kamfani ɗaya. Bayanan NFIU sun nuna cewar Kwamitin Kafa Takunkumi na Ƙasa ya yi zama a ranar 18 ga Maris, inda a Ƙarshen zaman nasa ya bada shawarar kafa wa wasu takunkumi saboda samun da aka yi da hannu a ɗaukar nauyin ta’addanci. Ɗaya daga…
Read More
Rubutu ya sauya min rayuwata da duniyata – Ramlat Manga Maidambu

Rubutu ya sauya min rayuwata da duniyata – Ramlat Manga Maidambu

"Na sha wahalar rubuta littafina na farko" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Ramlat Abdulrahman Manga, wacce aka fi sani da Maidambu, na daga cikin jajirtattun marubuta onlayin da aka sha gwagwarmaya da su a duniyar marubuta, tun ba a san ko ita wacce ce ba. Ta yi rubuce rubuce da dama, waɗanda suka samu karvuwa a wajen jama'a har kuma ita ma ta yarda cewa ta samu alheri sosai. Tana daga cikin marubutan adabi da suka fito daga Jihar Bauci kuma take bai wa mara ɗa kunya wajen ɗaga sunan jihar a harkar batun rubuce-rubucen Hausa. A zantawarta da Abba Abubakar…
Read More
Ilimi ne ƙashin bayan cigaban Zamfara – Lawal

Ilimi ne ƙashin bayan cigaban Zamfara – Lawal

Daga BASHIR ISAH Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya ayyana ilimi a matsayin ƙashin bayan cigaban Jihar Zamfara. Lawal ya bayyana haka ne a lokacin da ya karɓi baƙincin ɗaliban makarantar Leadsprings International School a Fadar Gwamnatin Jihar da ke Gusau a ranar Laraba. Kakakin Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya ce yayin ziyarar, ɗaliban sun miƙa wa Lawal muhimman ƙudurori guda bakwai don amfanin gaba. Suleiman ya ce ƙudurorin sun haɗa da raya babban birnin jihar, wato Gusau, inganta fannin tsaro, samar da kamfanin jirgin sama mallakar Zamfara, bunƙasa fasaha, bunƙasa fannin noma, ɓangaren kasuwanci da sauransu. Sa'ilin da…
Read More