20
Mar
Daga BASHIR ISAH Majalisar Dattawa ta Nijeriya ta amince da Dokar bai wa ɗalibai rancen karatu ta 2024 wanda ɗalibai a manyan makarantu za su ci gajiya. Majalisar ta amince da hakan ne bayan da ta karɓi rahoton Kwamitin Majalisar kan Manyan Makarantu da asusunTETFUND. Shugaban Kwamitin, Sanata Muntari Dandutse (APC – Katsina ta Kudu), shi ne ya gabatar da rahoton yayin zaman malajisar a ranar Laraba. Idan za a iya tunawa, a makon da ya gabata Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya aike wa majalisar dattawa da ta wakilai buƙatar neman soke dokar bai wa ɗalibai rancen karatu (ga…
