Editor

9513 Posts
Buhari ya amince da kashe bilyan N18 don gina sabbin jami’o’i huɗu a sassan ƙasa

Buhari ya amince da kashe bilyan N18 don gina sabbin jami’o’i huɗu a sassan ƙasa

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya amince da kashe kuɗi Naira biliyan 18 domin gina jami'o'in ƙwararru guda huɗu a faɗin ƙasa. Gwamnati ta bayyana haka ne a Litinin da ta gabata, inda ta ce jami'o'in da za a gida sun haɗa da ta fasaha da za a gina Jigawa da Akwa Ibom, sai kuma ta kiwon lafiya da nazarin ingancin abinci da magunguna da za a gina a Azare, jihar Bauchi da Ila Orangun, jihar Osun. Da yake yi wa manema labarai bayani a Abuja, Ministan Ilimi, Malam Adamu Adamu, ya ce…
Read More
El-Rufai ya rantsar da wasu manyan jami’an gwamnati

El-Rufai ya rantsar da wasu manyan jami’an gwamnati

Daga ABBA MUHAMMAD, a Kaduna Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmed El-Rufai ya rantsar da Shugaban Hukumar Zaɓe mai Zaman Kanta ta Jihar Kaduna da Shugaban Hukumar Kula da Kwangiloli ta Jihar Kaduna da kuma wasu sababbin manyan sakatarorin ma’aikatun gwamnatin Jihar a gidan gwamnati da ke Kaduna. Ranar Litinin Gwamnan ya rantsar da jami'an da lamarin ya shafa da suka haɗa da: Dakta Saratu Binta Dikko Audu - Shugaban Hukumar Zaɓe mai Zaman Kanta ta Jihar Kaduna.Injiniya Sanusi Aminu Yero - Shugaban Hukumar Kula Kwangiloli ta Jihar Kaduna.Adamu Atama - Babban Sakatare.Abubakar Abba Umar - Babban Sakatare.Balarabe Wakili -…
Read More
‘Yan Nijeriya miliyan 40 masu ciwon sikila sun nemi taimakon Buhari – Ƙungiya

‘Yan Nijeriya miliyan 40 masu ciwon sikila sun nemi taimakon Buhari – Ƙungiya

Daga BAKURA K. MUHAMMAD a Bauchi Wata cibiya ta neman taimako ga masu ciwon sikila daga gwamnati da daukacin al’umma ta gabatar da kokenta ga gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari na kawo ɗauki ga masu fama da wannan ciwo kimanin su miliyan 40 da ke sassa daban-daban na ƙasar. Kamar yadda cibiyar ta ce, masu wannan ciwo su na ta mutuwa, saboda rashin samun ingantaccen abinci, haɗi da rashin samun magunguna da ke rage raɗaɗin ciwon na sikila. Da suke gabatar da koken nasu a daidai lokacin bikin shekara-shekara na tunawa da ciwon na sikila a Bauchi, majinyatan sun bayyana hali…
Read More
Harin Yauri: An ceto ƙarin malami ɗaya, ɗalibai uku

Harin Yauri: An ceto ƙarin malami ɗaya, ɗalibai uku

Daga AISHA ASAS Sojojin Nijeriya ƙarƙashin shirin Operation HADARIN DAJI tare da taimakon sojojin sama, sun yi nasarar ceto ƙarin waɗanda aka yi garkuwa da da su a FGC Birnin Yawuri. Bayanan da Manhaja ta kalato sun nuna waɗanda aka kuɓutar ɗin sun haɗa da malami ɗaya da ɗalibai uku, an kuɓutar da su ne a Makuku. Sanarwar da ta fito daga Daraktan Sashen Hulɗa da Jama'a na Sojojin Nijeriya, Brigadier General Onyema Nwachukwu, ta nuna baya ga kuɓutar da waɗanda lamarin ya shafa, haka nan jami'an sun kashe ɗaya daga cikin ɓarayin sannan sun ƙwato babura guda tara daga…
Read More
Zulum ya amshi umarnin Buhari na dawo da aikin gona  a yankin Mulai-Dalwa

Zulum ya amshi umarnin Buhari na dawo da aikin gona a yankin Mulai-Dalwa

Daga WAKILINMU Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya kai ziyara a ƙauyukan Mulai da Dalwa tare da ganawa da jami'an tsaro don samar da matakan da suka dace wajen farfaɗo da harkar noma a ƙauyukan. A Lahadin da ta gabata Zulum ya yi wannan ziyarar a matsayin wani mataki na cika umarnin Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari wanda ya bayar sa'ilin da ya ziyarci jihar Alhamis da ta gabata, inda ya buƙaci jami'an tsaro su yi aiki tare da gwamnatin jihar wajen samar da tsare-tsaren da za su bai wa jama'ar ƙauyukan damar komawa gona ba tare da wata fargaba…
Read More
Yadda PDP ta lallasa APC a zaɓen cike gurbi a Kaduna

Yadda PDP ta lallasa APC a zaɓen cike gurbi a Kaduna

Daga ABBA MUHAMMAD a Kaduna A jiya Asabar, 19 ga Yuni, 2021 aka gudanar da zaɓen cike gurbi a Ƙaramar Hukumar Sabon Gari ta Jihar Kaduna. Jam’iyyar APC mai mulkin Jihar Kaduna ta sha kaye a zaɓen maye gurbi na ɗan Majalisar Dokokin Jiha mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Sabon Gari ta Jihar. Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta bayyana Alhaji Usman Baba na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaɓen cike gurbin. Shugaban hukumar zaɓen yankin mai suna Malam Mohammed Nuruddin Musa, shi ne ya faɗi sakamakon zaɓen ranar Asabar a sakatariyar Ƙaramar Hukumar da ke Zariya. Malam Mohammed…
Read More
APC ta lashe zaɓen maye gurbi a Jigawa

APC ta lashe zaɓen maye gurbi a Jigawa

Daga UMAR AƘILU MAJERI a Dutse Jam'iyyar PDP da sauran jam'iyyu sun sha ƙasa a zaɓen maye gurbi na ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Gwaram da aka gudanar a jihar Jigawa ran Asabar da ta gabata. Ɗan takarar jam'iyyar APC, Yusif Shitu Galanbi, ya samu nasarar lashe zaɓen ne inda ya yi nasarar a kan abokan hamayyarsa na PDP, Sharif Kamilu Maicalbi da sauransu. Wannan shi ne karo na uku da Galanbi zai wakilci al'ummar yankinsu a Majalisar Wakilai ta Ƙasa. Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana Galanbi a matsayin wanda ya yi nasara a zaɓen. Jami'in Hukumar…
Read More
Ogun: Haɗari ya ci ran mutum biyu, an ƙona motar da ta yi kisan

Ogun: Haɗari ya ci ran mutum biyu, an ƙona motar da ta yi kisan

Daga WAKILINMU Wasu fusatattun mutane sun banka wa wata babbar motar ɗaukar kaya wuta biyo bayan haɗarin da ya auku wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutum biyu a jihar Ogun. Haɗarin ya auku ne a hanyar Ibeshe da ke yankin ƙaramar hukumar Yewa ta Arewa a Asabar da ta gabata. Bayanan da Manhaja ta kalato sun nuna motar ta saki hannunta ne ta koma ɗaya hannun inda ta sami wasu mutum biyu a kan babur ta murƙushe su har lahira. Mai magana da yawun rundunar kula da bin dokoki na jihar, Babatunde Akinbiyi, ya tabbatar da faruwar lamarin ga manema…
Read More
Harin Yauri: An kuɓutar da malamai 2, ɗalibai 6

Harin Yauri: An kuɓutar da malamai 2, ɗalibai 6

Daga AMINA YUSUF ALI Alamu sun nuna malamai biyu da kuma ɗalibai shida na Federal Government College (FGC) Yauri da aka yi garkuwa da su, sun kuɓuta. Bayanai sun tabbatar da cewa an samu nasarar kuɓutar da waɗanda lamarin ya shafa ne sakamakon kwanton ɓaunan da da jami'an tsaro suka yi wa 'yan bindigar da suka kai wa makarantar hari. Tun bayan aukuwar harin da aka kai FGC Yauri sama da sa'o'i 24 da suka gabata, har yanzu babu wani bayani da aka fitar a hukumance kan batun, walau daga gwamnatin jihar Kebbi ko 'yan sanda. Ɗalibai kimanin su talatin…
Read More
Jam’iyyu 18 ke fafutikar neman kujerar gwamnan Anambra – INEC

Jam’iyyu 18 ke fafutikar neman kujerar gwamnan Anambra – INEC

Daga UMAR M. GOMBE Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ce jam'iyyun siyasa 18 ne su ka nuna sha'awar su ta shiga zaɓen gwamnan Jihar Anambara da za a yi a ranar 6 ga Nuwamba mai zuwa. Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, shi ne ya bayyana haka a wajen taron kwata ta biyu na hukumar da jam'iyyun siyasa wanda aka yi a ranar Alhamis a Abuja. Yakubu ya ce dukkan jam'iyyun 18 sun tsara gudanar da zaɓuɓɓukan su na fidda gwani a bisa jadawalin kwanaki da hukumar ta fitar. Ya ce, “A kan batun zaɓuɓɓukan ƙananan hukumomin Yankin Birnin Tarayya, jam'iyyun siyasa…
Read More