Editor

9513 Posts
Kansilan Guringawa, Muslihu Yusuf Ali ya ƙaddamar da shirin bada ilimi kyauta ga marayu

Kansilan Guringawa, Muslihu Yusuf Ali ya ƙaddamar da shirin bada ilimi kyauta ga marayu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja A ƙarshen makon jiya ne kansilan Kano, Honorabul Muslihu Yusuf Ali ya ƙaddamar da raba tallafi ga marayu 10 da aka samar wa gurbin karatu da ɗaukar nauyin su a 'Ihya'us Sunna Science and Commercial College' tare da bada tallafin N20,000 don ɗinka masu kayan makaranta. Shirin wanda ke ƙarkashin kwamitin Hajiya Bilkisu Yusuf Ali da ake wa laƙabi da 'Guringawa Education Promotion Committee' a turance zai duba makarantun kuɗi da ke cikin mazaɓar don samun gurbi na malamai da ɗalibai, sai kuma gidauniyar kansila ta bayar da tallafi. Haka kuma Muslihu Yusuf Ali,…
Read More
Za a rataye ɗan shekara 22 saboda fashi da makami a Ekiti

Za a rataye ɗan shekara 22 saboda fashi da makami a Ekiti

Daga WAKILINMU Babbar Kotun jihar Ekiti mai zamanta a Ado-Ekiti, ta yanke wa wani matashi ɗan shekara 22 mai suna Kehinde Olajide hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda aikata laifin fashi da makami. Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa kotun ta saki wasu 'yan gida ɗaya da aka alaƙanta su da fashin, wato Kareem Azeez mai shekara 24 da Bamisile Lateef ɗan shekara 28 da kuma Adebayo Basiru ɗan shekara 25. Yayin da yake yanke hukuncin ran Alhamis da ta gabata, Mai Shari'a Lekan Ogunmoye, ya ce masu gabatar fa ƙara sun gabatar da gamsassun hujjojin aikata fashi da makami…
Read More
Bincike kafin aure a Ƙasar Hausa: Ga ƙoshi ga kwanan yunwa

Bincike kafin aure a Ƙasar Hausa: Ga ƙoshi ga kwanan yunwa

Daga AMINA YUSUF ALI Assalamu alaikum. Masu karatu sannunku da bibiyar filinmu na zamantakewa wanda kuke karantawa kowanne mako a wannann jarida taku mai farin jini, Manhaja. A wannan mako za mu yi bayani a kan bincike kafin aure a ƙasar Hausa. Menene bincike kafin aure? Bincike wani abu ne da magabatan yaro ko yarinya da suka shirya yin aure suke yi kafin a kai ga amincewa da auren nasu. Iyaye kan himmatu wajen bincike don tabbatar da wanda yake zuwa wajen yarinyarsu nagartacce ne ko akasin haka. Yayin da su ma iyayen yaro ba a bar su a baya…
Read More
Ko Boko Haram ta yi sabon shugaba ne?

Ko Boko Haram ta yi sabon shugaba ne?

Daga BARISTA BULAMA BUKARTI A jiya ne dai wani sabon bidiyo da ya ke cire dukkan shakku game da mutuwar Shekau ya bayyana. Wannan gajeren bidiyon ya ɗauko hoton mayaƙan ƙungiyar Boko Haram na ɓangaren tsohon shugabanta Abubakar Shekau. Inda suke ƙara tabbatar da mutuwar tsohon shugaban nasu. Kakakin nasu mai suna Bakura Shalaba, ya bayyana tare da mayaƙa fiye da goma suna rufa masa baya. Inda ya yi addu'ar neman rahmar Allah ga Marigayi Shekau. Tare da kira ga 'yan'uwan sa masu riƙe da makamai da kada su bari abinda ya faru ya kashe musu gwiwa. Haka zalika, ya yi…
Read More
Ba duk shugaba zai kasadar Zulum ba – Buhari

Ba duk shugaba zai kasadar Zulum ba – Buhari

*Shugaba Buhari ya gode wa ’yan Nijeriya da suke mara masa baya har yanzu Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya bayyana cewa, ba kowanne mai mulki ne zai iya yin irin kasadar da Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ke yi ba a cikin yanayi na matsalar tsaron da ke addabar jiharsa. Shugaba Buhari, wanda ya ke jawabi a lokacin da ya ziyarci Fadar Shehun Borno jiya a ziyarar aikin da ya kai jihar ta Borno, ya yaba wa Gwamna Zulum bisa yadda ya ke wucewa gaba ba dare ba rana kuma cikin rashin…
Read More
Ranar Dimukraɗiyya: Gwamnati na murna wasu na zanga-zanga

Ranar Dimukraɗiyya: Gwamnati na murna wasu na zanga-zanga

A ranar Asabar ɗin da ta gabata ne Nijeriya ta yi bikin cika shekara 22 da komawar ƙasar kan turbar dimokuraɗiyya, inda mahukunta da `yan ƙasa suke ƙididdigar nasarori da kuma tarin ƙalubalen da ƙasar ta fuskanta da kuma wanda take kan fuskanta. Wannan shi ne karon farko da ake bikin a wannan rana tun bayan sauya ranar bikin daga 29 ga watan Mayu zuwa 12 ga watan Yuni da hukumomin ƙasar suka yi a shekarar da ta gabata, don tunawa da zaɓen MKO Abiola; Zaɓen da aka gudanar a ranar 12 ga watan Yunin 1993 wanda a lokacin mutane…
Read More
Bai kamata mu yi saurin mantawa da gudunmawar Kaunda ba – Buhari

Bai kamata mu yi saurin mantawa da gudunmawar Kaunda ba – Buhari

Daga AISHA ASAS Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya bayyana tsohon Shugaban Ƙasar Zambiya, Kenneth Kaunda, a matsayin "Ɗaya daga cikin manyan shugabannin Afirka da na duniya baki ɗaya da ke ƙaunar ƙasarsa da mutanensa sosai. Buhari ya ce labarin rasuwar Kaunda ya kaɗa shi matuƙa saboda sanin irin gudunmawar da ya bai wa ƙasarsa Zambiya da ma Afirka baki ɗaya a halin rayuwarsa. A sanarwar da ta tafito ta hannun mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Malam Garba Shehu, "Ba za mu yi saurin manta gwagwarmayar Kaunda ba wajen ƙwato wa Zambjya 'yanci daga Afirka ta Kudu da kuma tsohuwar…
Read More
INEC ta sa ranakun zaɓen gwamnonin Ekiti da Osun

INEC ta sa ranakun zaɓen gwamnonin Ekiti da Osun

Daga WAKILINMU Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa za ta gudanar da zaɓen gwamnan Jihar Ekiti a ranar 18 ga Yuni, 2022 yayin da kuma za ta yi na gwamnan Jihar Osun a ranar 16 ga Yuli, 2022. Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, shi ne ya bayyana haka a wurin taron da ya yi da kwamishinonin zaɓe na jihohi a ranar Laraba a hedikwatar INEC da ke Abuja. Yakubu ya ce an wallafa ranakun da aka aje na fara yaƙin neman zaɓe da sauran cikakkun bayanai kan jadawalin ranakun zaɓen da sauran ayyuka dangane da zaɓuɓɓukan biyu a gidan…
Read More
APC ta dakatar ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Birnin Kano

APC ta dakatar ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Birnin Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Jam'iyyar APC ta jihar Kano ta ce ta dakatar da ɗan Majalisar Wakilai, Hon. Sha'aban Ibrahim Sharaɗa daga jam'iyya na tsawon shekara guda. Jam'iyyar ta ce daga wannan lokaci, ta haramta wa ɗan Majalisar shiga harkokinta a dukkanin matakai na tsawon lokacin dakatarwar. Cikin sanarwar da ta sami sa hannun Shugaban APC na gundumar Sharaɗa, Aljahi Abdullahi Umar da sakatarensa Auwalu Saidu Muhammad, mai ɗauke da kwanan wata 16/06/2021, APC ta ce ta ɗauki matakin dakatar da Hon Sha'aban ne bayan da aka same shi da aikata laifin cin mutuncin Mai Girma Gwamnan Kano da…
Read More
Gwamnatin Tarayya ta ba Kanawa 320 aikin duba shiri tare da na’urori

Gwamnatin Tarayya ta ba Kanawa 320 aikin duba shiri tare da na’urori

Daga AISHA ASAS Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ta ƙaddamar da shirin raba takardun kama aiki tare da na'urorin duba aiki ga waɗanda aka horas domin sanya ido kan ayyukan ma'aikatar a jihar. An gabatar da taron a ɗakin taro na 'Coronation' da ke cikin gidan gwamnati Hall a Kano a ranar 15 ga Yuni, 2021. Ministar, wadda Babban Sakatare a ma'aikatar, Bashir Nura Alƙali ya wakilta a taron, ta bayyana cewa Shugaba Muhammadu Buhari ya ƙirƙiro Shirin Inganta Rayuwar Jama'a, wato 'National Social Investment Programme' (NSIP) ne a cikin 2016 domin a fidda…
Read More