Editor

9513 Posts
Gobe Barno za ta karɓi baƙuncin Buhari

Gobe Barno za ta karɓi baƙuncin Buhari

Daga AMINA YUSUF ALI Ana sa ran Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya kai ziyarar aiki a jihar Barno ran Alhamis idan Allah ya kai mu. Gwamnan jihar, Babagana Umara Zulum, shi ne ya bayyana haka yayin jawabin da ya yi wa 'yan jihar kai tsaye a kafar yaɗa labarai a Maiduguri. Tare da kira ga talakawansa da su fito ƙwansu da ƙwarƙwata domin tarbar babban baƙon nasu. A cewar Zulum Buhari da tawagarsa za su ziryaci Barno ne domin la'akari da sha'anin tsaro na yankin Arewa-maso-gabas, kana ya ƙaddamar da tarin ayyukan da gwamnatin jihar ta aiwatar a tsakanin shekaru…
Read More
Almundahana: Yadda muka cafke ministar da ta sayi gida na Dala milyan 37.5 ta bayan fage – EFCC

Almundahana: Yadda muka cafke ministar da ta sayi gida na Dala milyan 37.5 ta bayan fage – EFCC

Daga UMAR M. GOMBE Shugaban Hukumar Yaƙi da yi wa Tattalin Arziki Zagon Ƙasa da Zambar Kuɗaɗe (EFCC), Abdulrasheed Bawa, ya labarta yadda wata minista ta sayi gida na maƙudan kudi Dala milyan $37.5 daga hannun wani banki sannan ta biya rabin kuɗi Dala milyan $20 kuɗi hannu. Bawa ya ba da wannan labari ne ba tare da ya bayyana sunan ministar da lamarin ya shafa ba, haka ma bai bayyana ko har yanzu ministar na kan kujera ko kuwa a'a ba. Shugaban EFCC ya yi wannan bayanin ne yayin wani shiri da aka yi da shi a tashar talabijin…
Read More
Bayan shekara 25, Nijeriya ta samu ƙarin rumfunan zaɓe 56,872

Bayan shekara 25, Nijeriya ta samu ƙarin rumfunan zaɓe 56,872

Daga AMINA YUSUF ALI Hukumar Zaɓe ta Kasa (INEC) ta ce kawo yanzu adadin rumfunan zaɓe da Nijeriya ke da su ya kai 176,846. Tun 1996 da aka ƙirƙiri ƙarin rumfunan zaɓe, hakan bai sake aukuwa ba sai bayan shekara 25, inda INEC ta sauya wasu cibiyoyin zaɓe guda 56,872 a faɗin ƙasa zuwa cikakkun rumfunan zaɓe. Kafin wannan lokaci, rumfunan zaɓen da INEC ta san da su a faɗin ƙasa guda 119,974 ne. Da yake jawabi a wajen wani taro tare da kwamishinonin hukumar a ranar Laraba, Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, ya ce sun yi nasarar ɗauke rumfunan…
Read More
Nijeriya za ta karɓi rigakafin korona milyan 3.92 a Agusta – Gwamnati

Nijeriya za ta karɓi rigakafin korona milyan 3.92 a Agusta – Gwamnati

Daga AISHA ASAS Ana sa ran Nijeriya ta karɓi ƙarin aullurar rigakafin korona na Oxford/AstraZeneca guda milyan 3.92 ya zuwa farkon Agusta. Shugaban Hukumar Bunƙasa Lafiya a Matakin Farko, Dr Faisal Shuaib ne ya bayyana haka a Talatar da ta gabata a Abuja. Sai dai bai bayyana takamammiyar ranar da maganin zai shiga hannun Nijeriya ba. Ya ce, “Mun samu labarin Nijeriya za ta samu rigakafin korona na Oxford/AstraZeneca guda milyan 3.92 ya zuwa ƙarshen Yuli ko farkon Agusta." Ya ƙara da cewa, "Idan muka samu ƙarin bayanai game da takamammiyar ranar da za a karɓi maganin, za mu bayyana…
Read More
Bello ya koka kan yadda ‘yan siyasa da jami’an gwamnati ke saida wa ‘yan fashi bayanan sirri

Bello ya koka kan yadda ‘yan siyasa da jami’an gwamnati ke saida wa ‘yan fashi bayanan sirri

Daga BASHIR ISAH Gwamnan Jihar Neja, Abubakar Sani Bello, ya ce wasu 'yan siyasa da na kusa da gwamnati sun zaɓi zama 'yan leƙen-asiri ga 'yan bin bindigar da suka addabi jihar saboda kuɗi inda sukan saci bayanan sirri na gwamnati suna kai wa ɓarayin. Gwamna Bello ya bayyana haka ne a Talatar da ta gabata a lokacin da yake ƙaddamar da rundunar tsaro ta musmman mai jami'ai 161 domin yaƙi da rashin ɗa'ar matasa a Minna babban birnin jihar. A cewarsa, "Akwai 'yan siyasa da wasu na kusa da gwamnati da ke satar bayanai suna kai wa ɓarayin. Ko da taro…
Read More
Yulin 2022 zaɓen gwamna zai gudana a Osun – INEC

Yulin 2022 zaɓen gwamna zai gudana a Osun – INEC

Daga WAKILINMU Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ce, ya zuwa 16 ga Yulin 2022 za a gudanar da zaɓen gwamnan na jihar Osun. Bayanin haka na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da INEC ta fitar ta hannun sakatariyarta, Rose Oriarian-Anthony a Talatar da ta gabata. Jadawalin zaɓen mai ɗauke da kwanan wata Yuni 10, 2021, ya nuna tsare-tsaren ayyukan zaɓen wanda za a soma gudanarwa daga 1 ga Fabrairun 2022.
Read More
NUJ ta samu tabarrukin Janar Babangida a Minna

NUJ ta samu tabarrukin Janar Babangida a Minna

Daga BASHIR ISAH Tsohon Shugaban Ƙasa, Ibrahim Badamasi Babangida, ya bai wa Ƙungiyar 'Yan Jarida ta Ƙasa (NUJ) Reshen Jihar Neja, tabbacin mara mata baya don taimaka mata wajen cim ma manufofinta. Babangida ya ba da wannan tabbaci ne a lokacin da tawagar sabbin shugabannin NUJ na jihar Neja ta ziyarce shi a gidansa da ke Minna, a Lahadin da ta gabata. Tsohon shugaban ya ce ya yaba da ziyarar 'yan jaridar ƙarƙarshin jagorancin shugabansu na jiha, Comrade Abu Nmodu. Tare da kira a gare su da su kasance masu aiki da gaskiya a kowane lokaci. Haka nan, ya shawarce…
Read More
Bala ya naɗa Gamawa Shugaban Ma’aikatan Fadar Gwamnatin Bauchi

Bala ya naɗa Gamawa Shugaban Ma’aikatan Fadar Gwamnatin Bauchi

Daga WAKILINMU Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya naɗa Dr Aminu Gamawa a matsayin sabon Shugaban Ma'aikatan Fadar Gwamnatin Jihar da ke Bauchi. Gamawa ya maye gurbin Ladan Salihu ne wanda  aka sauke daga muƙaminsa a ran 9 ga Yuni, tare da Sakataren Gwamnatin Jihar, kwamishinoni da sauran masu riƙe da muƙaman siyasa. Mai bai wa gwamna shawara kan harkokin yaɗa labarai da hulɗa da jama'a, Mukhtar Giɗaɗo, shi ne ya bayyana naɗin Gamawa cikin wata sanarwa da ya fitar a wannan Litinin a Bauchi. Kafin naɗin nasa, Gamawa shi ne Kwamishinan Ma'aikatar Kasafi da Tsarin Tattalin Arziki. Sanarwar ta…
Read More
Jiri ya kwashi Shugaban Ƙasar Zambiya ya yanke jiki ya faɗi a taro

Jiri ya kwashi Shugaban Ƙasar Zambiya ya yanke jiki ya faɗi a taro

Daga AISHA ASAS Shugaban Ƙasar Zambiya, Edgar Lungu, ya yanke jiki ya faɗi a wajen wani babban taro na ƙasar da aka gudanar a Lahadin da ta gabata a Lusaka, babban birnin ƙasar. Jim kaɗan bayan faruwar lamarin, sakataren gwamnatin ƙasar, Dr Simon Miti, ya bayyana wa manema labarai cewa Shugaba Lungu ya wattsake har ma ya ci gaba da harkokinsa. Dr Miti ya ce jiri ne ya kwashi shugaban yayin da yake jawabi a wajen taron bikin Ranar Tunawa da Dakarun Ƙasar karo na 46 inda ya yanke jiki ya faɗi, amma cewa ya wattsake ba tare da jimawa…
Read More
Ranar Jini ta Duniya: ‘Yan Afirka milyan 7 ke buƙatar jini duk shekara – WHO

Ranar Jini ta Duniya: ‘Yan Afirka milyan 7 ke buƙatar jini duk shekara – WHO

Daga UMAR M. GOMBE Hukumar Kiwon Lafiya ta Duniya (WHO), ta ce a shekarar da ta gabata an samu koma baya dangane da gudunmawar jini da ake samu a yankin Afirka saboda cutar korona. WHO ta ce mutane 'yan ƙalilan ne aka samu suna ba da gudunmawar jini sakamakon ɓullar annobar korona. Daraktar Shiyya ta WHO a Afirka, Dr Matshidiso Moeti, ta ce ƙarancin gudunmawar jini da ake fuskanta na da nasaba da hana tafiye-tafiye da aka yi don cutar korona da kuma tsoron harbuwa da cuta su ne suka hana mutane ziyartar cibiyon ba da gudunmawar jini. Ta ce,…
Read More