Editor

9513 Posts
Ƙuri’a ɗaya ta kawo ƙarshen mulkin Netanyahu na shekara 12 a Isra’ila

Ƙuri’a ɗaya ta kawo ƙarshen mulkin Netanyahu na shekara 12 a Isra’ila

Daga AMINA YUSUF ALI Firayiminista Benjamin Netanyahu, kuma firayiminista mafi daɗewa a Ƙasar Isra'ila ya yi adabo da kujerarsa. Hakan ta faru ne bayan majalisa ta sutale shi tare kuma da maye gurbinsa da wani sabon Firayiministan wanda aka zaɓo shi ta hanyar haɗin gwiwa da jam'iyyun siyasar da suke a ƙasar. A halin yanzu tuni sabon Firayiminista Mista Bennet ya ɗare kujerar Netanyahu wanda ya shafe tsawon shekaru goma sha biyu a matsayin firayiminista a ƙasar. Mr. Bennet dai ɗan ɓangaren mulkin ra'ayin riƙau ne na 'yan ƙasa. Kuma ana sa ran zai shafe shekaru biyu yana riƙe da…
Read More
Boko Haram na yaudarar mayaƙansu da Naira 5,000 – Zulum

Boko Haram na yaudarar mayaƙansu da Naira 5,000 – Zulum

Daga WAKILINMU Gwamnan Jihar Barno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya bayyana cewa mayaƙan Boko Haram suna amfani da kuɗi suna yaudarar mutane su shigo cikinsu inda sukan raba musu dubu biyar-biyar (N5,000). Kazalika, Zulum ya bayyana yadda gwamnatinsa ta sha gwagwarmaya da yaƙi da Boko Haram a tsakanin shekaru biyun da suka gabata. Gwamnan ya yi waɗannan bayanan ne yayin da yake yi wa talakawansa bayani ta kafar yaɗa labarai game da sha'anin mulkinsa a yayin bikin Ranar Dimukuraɗiyya na bana da aka gudanar a Asabar da ta gabata. Kazalika, bayanin gwamnan ya shafi bikin cikarsa shekara biyu kan mulkin…
Read More
Gona zan koma bayan na yi murabus daga siyasa – Masari

Gona zan koma bayan na yi murabus daga siyasa – Masari

Daga BASHIR ISAH Gwamna Aminu Masari na jihar Katsina, ya ce zai yi murabus daga harkokin siyasa bayan kammala wa'adinsa  a matsayin gwamna. Masari ya bayyana haka ne sa'ilin da yake yi wa taron maneman labarai bayani a Katsina yayin bikin Ranar Dimukuraɗiyya na bana da ya gudana ran Asabar da ta gabata. Gwamnan ya ce bayan kammala mulkinsa zai yi murabus daga siyasa sannan ya koma gonarsa ya ci gaba da noma. A cewarsa, "Na riƙe muƙamai da dama kama daga matsayin kwamishina a jihar Katsina zuwa Majalisar Ƙasa inda na riƙe matsayin Shugaban Majalisar Wakilai. “Ga shi har yanzu…
Read More
Gwamnati ta dakatar da albashin ma’aikata 331 saboda rashin cika umarnin IPPIS

Gwamnati ta dakatar da albashin ma’aikata 331 saboda rashin cika umarnin IPPIS

Daga WAKILINMU Gwamnantin Tarayya ta ce ta dakatar da albashin wasu ma'aikata su 331 saboda rashin ba da cikakken bayanansu a tsarin biyan albashi na IPPIS kamar yadda aka buƙaci kowane ma'aikaci da aikatawa. Babban Sakatare na Ofishin Gudanar da Ayyuka, Mahmuda Mamman, shi ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa ta hannu Daraktan Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama'a na Ofishin Shugaban Ma'aikata na Tarayya, Abdulganiyu Aminu, a ranar Asabar da ta gabata a Abuja. Kamar yadda sanarwar ta nuna, Mamman ya sanya wa takardar sanarwar hannu a madadin Shugaban Ma'aikata, Dr. Folasade Yemi-Esan. Kazalika, sanarwa ta ce an…
Read More
Al Mustapha ya shawarci Yahaya kan matsalar tsaron ƙasa

Al Mustapha ya shawarci Yahaya kan matsalar tsaron ƙasa

Daga AISHA ASAS Manjo Hamza Al Mustapha (Mai murabus) ya shawarci sabon Babban Hafsan Hafsoshi, Manjo Janar Faruk Yahaya, da ya kawo ƙarshen Boko Haram cikin taƙaitaccen lokaci. Al Mustapha, wanda shi ne tsohon shugaban tsaro ga tsohon shugaban ƙasa marigayi Janar Sani Abacha, ya bayyana hakan ne ga Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) a ranar Lahadi a Abuja. Ya ce wajibi ne Yahaya ya gaggauta kawo ƙarshen ta'addancin da ya yi sanadiyyar hasarar rayuka da dukiyoyi a faɗin ƙasa. A cewarsa, "Jinkiri wajen kawar da Boko Haram wani babban koma baya ne ga Nijeriya. Mafi alheri ga ƙasa,…
Read More
NAHCON ga maniyyatan Nijeriya: Mu rungumi ƙaddara da matakin da Saudiyya ta ɗauka

NAHCON ga maniyyatan Nijeriya: Mu rungumi ƙaddara da matakin da Saudiyya ta ɗauka

Daga UMAR M. GOMBE Hukumar Hajji ta Nijeriya (NAHCON), ta ce ta samu labarin hana 'yan wajen ƙasar Saudiyya zuwa hajjin bana da Masarautar Saudiyya ta ɗauka. Hukumar ta ce jami'anta da ke Saudiyyar sun tabbatar mata da wannan mataki da Saudiyya ta ɗauka dangane da hajjin 2021. Da wannan ne NAHCON ta ce, duk da tana sane da cewa matakin ba zai yi wa 'yan Nijeriya da sauran maniyyata na sassan duniya daɗi ba, amma cewa sun ɗauki matakin a matsayin ƙaddarar Ubangiji mai ikon sa a yi da hanawa. Tare da kira da a koma a nemi tuba…
Read More
Hajjin bana sai mazauna Saudiyya – Gwamnatin Saudiyya

Hajjin bana sai mazauna Saudiyya – Gwamnatin Saudiyya

Daga BASHIR ISAH Game da hajjin bana, Ƙasar Saudiyya ta ce za a rage yawan maniyyata da adadin bai wuce mutum 60,000, kuma duka maniyyatan za su zamana mazauna ƙasar ne ban da na waje saboda annobar korona. Saudiyya ta ba da sanarwar hakan ne a wannan Asabar ta wani kamfaninta na dilancin labarai. Da wannan, ya tabbata cewa hajjin 2021 na mazauna Saudiyya ne kawai amma ban da sauran ƙasashen duniya. Ko a shekarar da ta gabata mazauna Saudiyya da ba su wuce 1,000 ne aka zaɓe su suka gabatar da hajji. Kashi biyu bisa uku na mahajjatan baƙi…
Read More
Ranar Dimukuraɗiyya: Mun cire ‘yan Nijeriya milyan 10 daga ƙangin talauci cikin shekara biyu – Buhari

Ranar Dimukuraɗiyya: Mun cire ‘yan Nijeriya milyan 10 daga ƙangin talauci cikin shekara biyu – Buhari

Daga AISHA ASAS Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, ya ce gwamnatinsa ta yi nasarar cire 'yan Nijeriya su milyan 10.5 daga ƙangin talauci a tsakanin shekaru biyu da suka gabata. Buhari ya bayyana haka ne a jawabinsa na Ranar Dimukuraɗiyya ta bana da ya gabatar wa 'yan Nijeriya a ranar Asabar. Bayanan Bankin Duniya sunan Nijeriya na daga cikin ƙasashen da suke da mutane masu fama da matsanancin talauci. Idan dai za a iya tunawa, a 2019 Buhari ya yi alƙawarin raba 'yan Nijeriya milyan 100 da talauci a cikin shekaru goma. Yayin jawabinsa na ran Asabar shugaban ya ce, "Duk…
Read More
Ƙanin mahaifin Farfesa Abdalla ya kwanta dama

Ƙanin mahaifin Farfesa Abdalla ya kwanta dama

Daga Ibrahim Hamisu, Kano Allah Ya yi wa kwaun Farfesa Abdalla Uba Adamu, Alhaji Muhammad Ɗanbala Adamu Daneji (wanda aka fi sani da Kawu Dambala) rasuwa a jiya Juma'a, 12 ga Yuni, 2021 jim kaɗan bayan Sallar Magabriba bayan gajeriyar rashin lafiya. Ya rasu yana da shekaru 83. Shi dai marigayin ƙani ne ga Dr. Muhammad Uba Adamu Daneji, watau Kantoma, wanda Allah Ya yi wa rasuwa bara. Ya rasu ya bar matarsa, Hajiya Duduwa da 'ya'ya shida. Ɗaya daga cikin mutanen da marigayin ya riƙe sun haɗa da Farfesa Abdalla Uba Adamu, wanda ya yi shugabancin Buɗaɗɗiyar Jami'ar Nijeriya,…
Read More