29
May
Daga IBRAHIM HAMISU, a Kano Kungiyar Marubuta ta Ƙasa reshen jihar Kano, wato Association of Nigeria Author's (ANA) ta zaɓi sabbin shugabanni. Zaɓen ya gudana ne a ɗakin karatu na murtala Muhammad da ke kan Titin Ahmadu Bello da ke Kano. Dr. Maryam Ali Ali ce ta Jagoranci gudanar da zaɓen, waɗanda aka zaɓa sun hada da: Tjjani Muhammad Musa a matsayin shugaba, sai mataimakiyarsa Maimuna Idris Beli, da Mazhun Idris Ya'u a matsayin sakatare. Haka kuma an zaɓi Danladi Z. Haruna a matsayin Ma'aji da sakataren kuɗi Abdullahi Lawan Kangala. Sai jam'in walwala Hausa, da Abdullahi Muhammad a matsayin…
