Editor

9513 Posts
Baƙin kishi: Anya kuwa ciwon ‘ya macen na ‘ya macen ne?

Baƙin kishi: Anya kuwa ciwon ‘ya macen na ‘ya macen ne?

Daga AMINA YUSUF ALI Assalamu alaikum. Masu karatu sannunku da jimirin karanta wannan fili namu na Zamantakewa. Wanda yake zuwa muku kowanne mako a jaridarku mai farin jini ta Manhaja. A wannan makon za mu tattauna a kan zafin kishin mata da abinda ya je kawo shi, da kuma yadda za a magance shi. A sha karatu lafiya. Kafin na shiga rubutun gadan-gadan. Ya kamata na tuna wa 'yan'uwana mata cewa, mu ne jinsin da muka fi nuna muna da haɗin kai yayin da wata yar uwarmu ta shiga wani hali fiye da maza. Kuma mu ne kullum muke iƙirarin…
Read More
Ranar Keke ta Duniya: FRSC ta shawarci ‘yan Nijeriya su koma amfani da kekuna don rage aukuwar haɗurra

Ranar Keke ta Duniya: FRSC ta shawarci ‘yan Nijeriya su koma amfani da kekuna don rage aukuwar haɗurra

Daga UMAR M. GOMBE Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Ƙasa (FRSC) ta ce amfani da kekuna a matsayin hanyar sufuri zai taimaka wajen rage yawan haɗurra da kuma cinkoson abubuwan hawa a hanyoyi. Shugaban hukumar a jihar Filato, Alphonsus Godwin, shi ne ya bayyana haka a wajen wani gangamin masu tuƙa kekuna da aka shirya a Jos albarkacin Bikin Ranar Keke ta Duniya na 2021. A cewar jami'in, baya ga rage yawan aukuwar haɗurra, haka nan amfani da keke na taimako wajen inganta lafiya da kuma tabbatar da yanayi mai cike da lafiya, don haka ya shawarci al'ummar Filato da kewaye…
Read More
Tun ina ƙarama nake da burin zama malamar makaranta – Hauwa Hussaini

Tun ina ƙarama nake da burin zama malamar makaranta – Hauwa Hussaini

Hajiya Hauwa Husaini Muhammad malamar makaranta da takai babban matsayi na shugabar makarantar mata, wato "Principal" kuma ita ce shugabar ƙungiyar yaƙi da cin zarafin mata. A wannan tattaunar da Manhaja ta yi da ita a Kano, za ku ji yadda wannan ƙungiya tata ke fafutuka wajen yaƙi da cin zarafin mata da ƙananan yara wajen ƙwato masu haƙƙinsu musamman a Arewacin Nijeriya. Daga IBRAHIM HAMISU, a Kano Zamu so ki gabatar mana da kanki ga masu karatunmu? Kamar yadda ka sani sunana Hauwa Hussain Muhammad. An haife ni a Kano, na yi karatuna na allo da firamare da sakandare…
Read More
Nagarta: Zulum ya karɓi baƙuncin limamin Ka’aba

Nagarta: Zulum ya karɓi baƙuncin limamin Ka’aba

Daga AISHA ASAS Sakamakon nagartar da gwamnan jihar Barno, Farfesa Babagana Umara Zulum ke nunawa a harkar jagorancinsa, ya sanya ɗaya daga cikin limaman Masallacin Ka'aba a Ƙasar Saudiyya, Farfesa Hassan Abdulhamid Bukhari, ya ziyarci gwamnan don yabawa da kuma ƙarfafa masa gwiwa. Imam Bukhari, wanda babban malami ne a Jami'ar Ummul Qura da ke Makka, ya ziyarci Barno ne a Larabar da ta gabata inda Gwamna Zulum ya karɓi baƙuncinsa a fadar gwamnatin jihar da ke Maiduguri. Shehun malamin ya yi ziyarar ne bisa gayyatar Dr. Mohammed Kyari Dikwa, wanda shi ne Shugaban Gidauniyar Al-ansar wadda ke kan gina…
Read More
Labari da ɗuminsa: Gwamnatin Neja ta haramta acaɓa

Labari da ɗuminsa: Gwamnatin Neja ta haramta acaɓa

A matsayin wani mataki na ci gaba da yaƙi da matsalar tsaro a jihar Neja, gwamnatin jihar ƙarƙashin jagorancin Abubakar Sani Bello ta kafa dokar haramta acaɓa a faɗin Minna, babban birnin jihar. A cewar Gwamnatin wannan doka za ta soma aiki ne daga ranar Alhamis, 3 ga watan Yuni, 2021. Sai dai sabuwar dokar ta sahale wa masu babura na kansu da su riƙa zirga-zirga daga ƙarfe 6 na safe zuwa 9 na dare. Jihar Neja na daga cikin jihohin da ke matsanancin fama da matsalar 'yan bindiga, domin ko a baya-bayan nan sai da wasu 'yan fashin daji…
Read More
Saɓa ƙa’ida: Tiwita ta goge saƙon Shugaba Buhari

Saɓa ƙa’ida: Tiwita ta goge saƙon Shugaba Buhari

Daga BASHIR ISAH Sakamakon abin da ya kira da saɓa wa dokokinsa, kamfanin Twitter ya share wani saƙon da Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya wallafa a shafinsa na Twitter inda ya yi barazanar yin maganin waɗanda suka gagara ɗaukar izina daga yaƙin basasar da aka yi a Nijeriya. Rahotanni sun nuna da alama dai kamfanin ya goge saƙon Buharin ne bisa zargin saɓa dokokinsa. Cikin saƙon da ya wallafa a ranar Talata wanda bai yi wa Twitter daɗi ba, Buhari ya ce, "Galibin waɗanda ke nuna rashin ɗa'a ba su da masaniyar irin ɓanar da hasarar da aka tafka yayin…
Read More
Kisan AIG Dega: Mun kama wasu da ake zargi a Jos – ‘Yan sanda

Kisan AIG Dega: Mun kama wasu da ake zargi a Jos – ‘Yan sanda

Daga AISHA ASAS Rundunar 'Yanan Sandan Nijeriya a Jihar Filato, ta ce ta kama wasu da take zargin suna da hannu a badaƙalar kashe AIG Christopher Dega (mai murabus), kuma mai bai wa Gwamnan Benue, Samuel Ortom, shawara kan sha'anin tsaro. 'Yan bindiga sun kashe tsohon jami'in ɗan sandan ne a Jos babban birnin jihar Filato inda aka yi masa ruwan alburusai a ƙirjinsa wanda nan take rai ya yi halinsa. Kafin ya yi murabus daga aikin ɗan sanda, marigayin ya taɓa riƙe muƙamin kwamishinan 'yan sanda a jihar Barno da Edo. Marigayin ɗan asalin jihar Binuwai ne daga ƙaramar…
Read More
Buhari ya bada odar kuɓutar da ɗaliban Islamiyya 200 da aka sace a Tegina

Buhari ya bada odar kuɓutar da ɗaliban Islamiyya 200 da aka sace a Tegina

Daga UMAR M. GOMBE Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, ya umarci fannin tsaron ƙasa da ya hanzarta ganowa tare da kuɓutar da ɗaliban Islamiyya su 200 da aka sace a Jihar Neja. Shugaba Buhari ya bada odar hakan ne cikin wata sanarwa da mai magna da yawunsa, Malam Garba Shehu, ya fitar a Abuja a Litinin da ta gabata. A cewar Shehu, Buhari ya yi tir da faruwar lamarin bayan da labari ya isa gare shi. Tare da yin kira ga ɗaukacin hukumomin da lamarin ya shafa da su gaggauta yin abin da ya kamata don kuɓutar da ɗaliban. Haka nan,…
Read More
Sau 41 aka kai wa ofisoshin INEC hari cikin shekara 2 — Yakubu

Sau 41 aka kai wa ofisoshin INEC hari cikin shekara 2 — Yakubu

Daga AISHA ASAS Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya bayyana cewa an kai wa kadarorin hukumar hari har sau 41 a sassa daban-daban na ƙasar nan a cikin shekara biyu da ta gabata. Yakubu ya faɗi haka ne a taron gaggawa da hukumar ta yi da hukumomin tsaro ƙarƙashin Kwamitin Tuntuɓa kan Tsaron Harkar Zaɓe, wato 'Inter-agency Consultative Committee on Election Security' (ICCES). Yakubu ya ce ya kamata daga yanzu a ɗau hare-haren da ake kai wa kadarorin hukumar a matsayin babban abin damuwa ga ƙasa baki ɗaya. Ya ce, “Ba shakka, makwannin da su ka gabata sun…
Read More