Babaji

4785 Posts

Kotu ta yi watsi da ƙarar ƙalubalantar rufe layuka marasa rijista

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Babbar kotun tarayya da ke jihar Legas ta kori ƙarar da cibiyar tabbatar da ƴanci da adalci (SERAP), ta shigar wanda ke ƙalubalantar umarnin ofishin shugaban ƙasa na cewa a rufe layukan da ba a sadar da su da lambobin katin ɗan ƙasa ba (NIN). Mai Shari'a Yelim Bogoro ya ce tsarin gwamnatin tarayya da ya buƙaci sadar da layuka da lambobin katin ɗan ƙasa ya tabbatar da cewa maslahar ƙasa amfani ne gare ta, don haka tana sama da dukkan ƴancin kowaye a ƙasar. Waɗanda takardar ƙarar ta zayyano sun haɗa da; shugaban ƙasa, Antoni…
Read More

Ndume ya ƙi amincewa da shugabancin kwamitin majalisa, ya ce yana kan kalamansa

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Daga ƙarshe, Sanata Ali Ndume ya yi jawabi kan cire shi a matsayin Mai Tsawatarwa a majalisar dattijai inda ya ce bayan yin nazari kan abin da ya sa aka gaggauta sauke shi, an kuma fahimci hakan bai bada damar korar sa ba. Majalisa ta tuɓe Ndume daga muƙaminsa ne bayan da ya caccaki tsarin shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu kan yadda ya ke tafiyar da harkokin gwamnati. Haka kuma, bayan kwana biyu da faruwar haka ne Ndume ya ƙi karɓar muƙamin shugaban kwamitin walwala na majalisar inda ya ce bashi da kwarewa da muradin shugabantar…
Read More

Hukumar Almajirai za ta saka ɗalibai 10,000 a makaranta kafin Satumba

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Hukumar almajirai da ilimin yaran da ba sa zuwa makaranta (NCAOOSCE) tare da haɗin gwiwar kwamishinonin ilimin a wasu jihohin Arewa sun ƙudiri aniyar shiga lungu da saƙon ƙananan hukumomi shida na Abuja don zaƙulo yara 10,000 da ba sa zuwa makaranta domin sanya su a makarantu kafin watan Satumba. Sakataren hukumar, Mohammed Idris ya faɗi haka a ranar Juma'a, yayin gudanar da taron ƙaddamar da aikin zaƙulo yaran a babban ofishinta da ke Abuja. Idris, ya yaba wa shugaba Bola Tinubu kan goyon baya da ya ke basu a ƙoƙarinsa na magance matsalolin almajiranci da…
Read More

Nan ba kulob ba ne, sai an ba ki dama kafin ki yi magana – Akpabio ya gargaɗi Natasha

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Shugaban majalisar dattijai, Godswill Akpabio ya faɗa wa Sanatar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan cewa zauren majalisar ba kulob ba ne, don haka sai an gabatar da ita kafin ta yi magana a zaman majalisar. Hakan ya faru ne a lokacin da majalisar ke tafka muhawara game da ƙudirin ƙirƙirar dokar majalisar sufurin motoci da dangoginsu wanda Sanatan Kwara ta Kudu, Oyelola Ashiru na jam'iyyar APC ya ɗauki nauyinsa. Ƙudirin mai suna 'National Road Transportation Council (Establishment) bill, 2024' ya ƙunshi kula da harkokin sufurin da aikin yin sufurin da abubuwan da suka shafe su a…
Read More

Gwamnati ta fitar da hotuna da sunayen waɗanda su ka tsere daga gidan yarin Suleja

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Hukumar gyaran hali ta ƙasa (NCoS), ta fitar da hotuna da sunaye da sauran bayanan waɗansu mutane da su ka tsere daga kurkukun Suleja, reshen Abuja, sakamakon ruftawar ginin da su ke ciki bayan wani mamakon ruwan sama da aka yi a ranar Laraba, 24 ga watan Afrilu, 2024. Wata sanarwa da jami'in hulɗa da jama'a na hukumar, Abubakar Umar ya fitar a ranar Alhamis, ta ce matakin yana da muhimmanci wajen sake kamo su tare da mayar da su komar hukumar. Ya ce, sun miƙa bayanan waɗanda suka tseren ga sauran hukumomin tsaro da kuma…
Read More

Da ƊUMI-ƊUMI: Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar da Naira 70,000 a matsayin sabon mafi ƙarancin albashi ga ma'aikatan Nijeriya yayin da ya alƙawuranta sabonta dokar albashi duk bayan shekaru uku. Ministan yaɗa labarai Mohammed Idris ya faɗi hakan a Fadar shugaban ƙasa da ke Abuja, a ranar Alhamis. Ministan ya ce, shugaba Tinubu ya bayyana haka ne a yayin ganawa da shugabannin haɗaɗɗiyar ƙungiyar ƙwadago. Waɗanda su ka halarci zaman sun haɗa da shugaban ƙungiyar ƙwadago (NLC), Joe Ajaero da na ƙungiyar kasuwanci (TUC), Festus Usifo tare da wasu mambobin ƙungiyoyin. Kafin zaman, ƙungiyar ƙwadago ta…
Read More

Ƙudirin zangon shekara shida ga shugaban ƙasa da gwamnoni ya tsallake karatun farko a majalisa

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Majalisar wakilai ta gudanar da karatun farko ga ƙudirin da ke neman kwaskwarima ga kundin 1999 wanda zai mayar da yin shekara shida a kowane zango na ofishin shugaban ƙasa da gwamnoni da shugabannin ƙananan hukumomi. Ofishin shugaban ƙasa da na gwamnoni ya tsallake karatun ne a yayin zaman majalisar na ranar Laraba wanda Ikenga Ugochinyere da ke wakiltar mazaɓar Ideato ta Kudu da ta Arewa ta jihar Imo ya gabatar tare da wasu ƴan majalisa 50. Haka nan, ƙudirin na neman goyon bayan sakin layuka na 7, 135, 137, 180 da kuma na 182 kamar…
Read More

Tinubu ya nemi majalisa ta amince da ƙarin tiriliyan N6.2 a kasafin 2024

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya buƙaci majalisar dattijai ta yi kwaskwarima kan dokar kasafin kuɗin shekarar 2024 ta hanyar ƙara tiriliyan N6.2 kan na shekarar da ta gabata. Jawabin hakan na ƙunshe a cikin wata takarda da Tinubu ya aika wa shugaban majalisar, Goodwill Akpabio wacce aka bayyana ta a zaman majalisar na ranar Laraba. Tinubu ya buƙaci hakan ne la'akari da samun goyon bayan sakin layi na 58 wanda reshe ne na sakin layi na biyu na kudin dokar ƙasa kwaskwarimar 1999 inda ya nemi majalisar ta amince da ƙudirin. Ƙundirin gyaran dokar ta 2024,…
Read More

Majalisar Dattijai ta sauke Ndume a matsayin Mai Tsawatarwa, APC ta nemi ya bar ta

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Majalisar Dattijai ta sanar da cire Sanata Mohammed Ali Ndume da ke wakiltar Borno ta Kudu a matsayin mai tsawatarwa inda ta maye gurbinsa da Tahir Mungono da ke wakiltar Borno ta Arewa. An samu hukuncin hakan ne a wani jawabi da kakakin majalisar, Goodwill Akpabio ya yi ta wata ɗaukar murya wanda jiga-jigan mambobin APC da ke majalisar suka amince da hakan. Majalisar ta yi hukuncin ne la'akari da sukan gwamnatin shugaba Tinubu da Ndume ya ke yi a ƴan kwanakin nan wanda hakan ya sa APC ƙarƙashin shugabancin Abdullahi Umar Ganduje, ta aika da…
Read More

Kotu ta dawo da Shuaibu a matsayin Mataimakin Gwamnan Edo

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Mai Shari'a James Omotosho na babban kotun tarayya a Abuja ya dawo da Philip Shuaibu a matsayin mataimakin gwamnan jihar Edo bayan Majalisar Dokoki ta tsige shi watannin da suka gabata. Mai Shari'a Omotosho ya ce cire Philip daga muƙaminsa da majalisar ta yi bai halatta ba kuma ya saɓa wa dokar ƙasa. Mai Shari'ar ya umarci da a biya Philip albashi da alawus ɗinsa tun daga watan Afrilu wanda a lokacin aka tsige shi. Sai dai majalisar dokokin ta ƙi amincewa da hukuncin kotun inda ta shirya takardar ɗaukaka ƙara domin sake yin hukunci game…
Read More