Babaji

4784 Posts

Majalisar Dokokin Kano ta amince da ƙudirin ƙirƙirar sarakuna masu daraja ta biyu

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Majalisar dokokin jihar Kano ta amince da ƙudirin ƙirƙirar Majalisar Masarautu da zai bada damar samar da wasu Masarautun bayan da ƙudirin ya tsallake dubiya ta uku a ranar Talata. Ƙudirin, wanda mataimakin kakakin majalisar, Muhammad Bututu Bello da ke wakiltar Rimin Gado/Tofa ya jagoranta ya bayyana samar da Masarautar Kano a matsayin mai daraja ta ɗaya, sai Masarautun ƙananan hukumomin Rano, Gaya da Ƙaraye a matsayin masu darajoji na biyu-biyu. Sarakunan Masarautun masu daraja ta biyu za su ke biyayya ga Sarkin Kano sannan suna da ikon bashi shawara kan kula da zaman lafiyar al'umma…
Read More

Da ƊUMI-ƊUMI: Donald Trump ya ɗauki abokin tafiya a zaɓen Amurka da ke tafe

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Tsohon shugaban Amurka kuma ɗan takarar kujerar shugabancin ƙasar a zaɓen 2024, Donald Trump ya zaɓi Sanata JD Vance, R-Ohio a matsayin wanda zai zame masa mataimaki wanda ake fatan ya zama magajinsa na siyasa yayinda ake cigaba da shirye-shiryen zaɓe. A watan Agusta ne Vance zai cika shekaru 40 da haihuwa wanda ya kasance mai salo irin na Trump mai shekaru 78 da shugaba Joe Biden mai shekaru 81. Trump ya zaɓi matashin ne kwanaki biyu bayan da ya tsallake rijiya da baya inda aka kai masa harbi a yayin wani yawon neman zaɓe. Matuƙar…
Read More

Rundunar ‘Yan sanda ta dakatar da rijistar yanar gizo ga motoci

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Sufeta Janar na 'Yan sanda, Kayode Egbetokun ya dakatar da rijistar yanar gizo ta e-CMR ga motoci a Nijeriya. An bada umarnin hakan ne kwana ɗaya bayan rundunar 'Yan sandan ta bada wa'adin 29 ga Yuli ga masu motoci su yi rijistar e-CMR kan Naira 5,375. Jami'in hulɗa da jama'a na rundunar, ACP Olumuyiwa Adejobi ya fitar da sanarwar bayan ƙorafe-ƙorafe daga ƴan ƙasa na cewa yin rijistar tilastawa ce ga waɗanda suka motoci. Shugaban ƙungiyar lauyoyi kan muradun al'umma da cigaban Shari'a, John Aikpokpo Martins ya ce umarnin yin rijistar abin a ƙi amincewa da…
Read More

Messi ya ji rauni yayin da Argentina ta lashe Copa America karo na 16

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Ƙasar Argentina da ke Kudancin Nahiyar Amurka ta lashe gasar 'Copa America' karo na 16 bayan doke Colombia da ta yi da ci ɗaya da nema a birnin Miami. An dakatar da fara buga wasan na tsawon mintuna 80 bayan hayaniya ya kaure tsakanin magoya bayan ƙasashen biyu a wajen filin wasan. Kyaftin ɗin Argentina, Lionel Messi ya ji rauni yayinda yake ƙoƙarin karɓar ƙwallo a zango na biyu wanda hakan ya sa aka sauya shi da wani ɗan wasan inda ya bar fili yana zubar da ƙwalla. Lautaro Martinez shi ne ɗan wasan da ya…
Read More

Ministan labarai ya marabci ƴan jaridan da aka yi garkuwa da su bayan sako su

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Ministan Labarai da Haɗin kan Ƙasa, Alhaji Mohammed Idris ya marabci ƴan jaridan da ke aiki a Kaduna da aka yi garkuwa da su a gidajensu ƙarshen makon da ya gabata. Sanarwar ta fito ne daga mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Rabi'u Ibrahim a yayin ganawa da manema labarai a Abuja, ranar Lahadi. A lokacin da ya ke magana yayin martabar AbdulGafar Alabelewe na jaridar 'The Nation' da kuma AbdulRaheem Aodu na jaridar 'Blueprint' daga mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkar tsaro (NSA), Malam Nuhu Ribadu, Ministan ya jinjina wa hukumomin tsaro…
Read More

Rundunar ‘Yan Sanda ta kama jami’inta kan zargin yi wa yarinya fyaɗe

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Rundunar 'Yan sanda ta kama wani jami'inta mai muƙamin mataimakin sufuritanda kan zargin yin fyaɗe wa wata ƴar shekara 17 a Legas. Ana zargin ɗan sandan mai suna Owolabi da samun damar afkawa yarinyar a ofishinsa da ke reshen rundunar a Ojota. An kama shi ne bayan da hukumar yaƙi da cin zarafi ta jihar ta shigar da wata takarda ofishin kwamishinan 'Yan sandan jihar, Adegoke Fayoade wanda hakan ya sa kwamishinan ya bada umarnin gudanar da bincike kan lamarin. Mai magana da yawun rundunar, Benjamin Hundeyin ya tabbatar da kama jami'in nasu inda ya ce…
Read More

Shugabannin duniya sun bayyana kaɗuwarsu bisa kai wa Trump harbi

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Shugabannin ƙasashe da dama sun nuna damuwarsu kan ji wa tsohon shugaban ƙasa Amurka, Donald Trump ciwo a wani harin kisan kai da aka kai masa a lokacin yawon yaƙin neman zaɓe. Shugabanni da Firaministoci sun yi tsokaci kan tare da sukan tashin-tashinar siyasa gami da nuna goyon bayansu ga waɗanda ibtila'in ya afka musu a ranar Asabar wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutum ɗaya da kuma raunata wasu biyu a taron. Shugabar hukumar Turai, Ursula Von der Leyen ta ce ta yi matuƙar girgiza da harin inda ta ce babu gurbin tashin-tashinar siyasa a demokraɗiyya.…
Read More

Tinubu ya naɗa sabbin shugabannin wasu hukumomi

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar da naɗa Baffa Ɗan Agundi a matsayin sabon Darakta Janar na cibiyar bunƙasa ƙwazon aiki ta ƙasa (NPC). Mai taimaka wa Tinubu kan harkokin yaɗa labarai, Ajuri Ngelale ya ce, Ɗan Agundi shi ne tsohon shugaban masu rinjaye na Majalisar Dokokin jihar Kano kuma tsohon rijistira a babban kotun Shari'a na jihar. Tinubu ya kuma naɗa tsohon mataimakin gwamnan jihar Nassarawa, Silas Agara a matsayin Darakta Janar na cibiyar samar da ayyuka (NDE). Agara, ɗan kasuwa ne kuma jigo a harkar wasanni. Haka kuma, "a hukumar kula da albarkatun ruwa…
Read More

Ministar al’adu ta taya Wole Soyinka murnar cika shekaru 90

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Ministar al'adu, Barista Hannatu Musa Musawa ta shiga sahun al'umma da dama wajen taya ɗaya daga cikin jigo a fagen ilimi, Farfesa Wole Soyinka murnar cikarsa shekaru 90 a duniya. Wata sanarwa da mai bata shawara kan harkokin yaɗa labarai, Nneka Ikem Anibeze ta fitar, ta ce ministar ta taya Farfesan murnar cimma nasarar kai wa matakin nasara irin haka gami da jinjina masa bisa ga halin juriya da ya siffanta da shi. Musawa ta kuma yi farin cikin sauya sunan cibiyar al'adu ta ƙasa zuwa cibiyar al'adu ta Wole Soyinka wanda shugaba Bola Ahmed Tinubu…
Read More

An cinna gobara a fadar Sarki Sanusi

Daga FAROUK ABBAS Wani rahoto daga jihar Kano ya ce gobara ta kama a fadar Sarki Sanusi da ke Gidan Rumfa wanda ake zargin waɗansu da ba'a san ko su waye ba ne suka cinna ta, inda a nan ne Sarkin ya ke. Lamarin ya auku ne da misalin ƙarfe 11 na daren Juma'a, a Ƙofar Kudu wanda a nan ne Sarkin ya ke zaman kotu duk ranar Litinin. Wani mutum da ya buƙaci a sakaya sunansa, ya ce suna zargin an buɗe mukullin ƙofar ne da ƙarfi sai kuma aka shiga ciki aka cinna wuta kana sai aka sake…
Read More