Babaji

4787 Posts

An samu tsaiko a shari’ar Kwankwaso kan EFCC

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Sakamakon rashin cike ƙa'idojin babbar kotun jihar Kano da hukumar hana yi wa tattalin arziƙi zagon ƙasa, EFCC ta yi, an samu tsaiko kan sauraron ƙarar da aka shigar kan kare ƴancin shugaban jam'iyyar NNPP, Rabi'u Musa Kwankwaso da wasu mutum bakwai. Jaridar 'Daily Trust' ta ruwaito cewa, waɗanda su ka shigar da ƙarar sun haɗa da; NNPP, Dakta Ajuji Ahmed, Dipo Olayanku, Ahmed Balewa, Cif Clement Anele, Ledi Folshade Aliu, Buba Galadima da kuma Rabi'u Musa Kwankwaso kan hukumar EFCC. A yayin da aka tada batun, lauyan da ya karɓi shigar da ƙarar, Robert Hon,…
Read More

DSS ta sake kama wani matashi kan shirya zanga-zanga a Sakkwato

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Rundunar Ƴan sandan farin kaya ta DSS, ta yi nasarar kama wani matashin Nijeriya mai suna Aliyu Sanusi kan shirya zanga-zangar da ke ƙalubalantar raunin shugabanci a faɗin ƙasar. An kama matashin ne a yammacin ranar Litinin, a hanyar Sama da ke Sakkwato, babban birnin jihar. Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa a jam'iyyar AAC, Omoyele Sowere ya bayyana hakan a shafinsa na X, a ranar Talata inda ya buƙaci hukumar ta gaggauta sako matashin, yana mai cewa hakan ya saɓa wa doka. Lamarin ya auku ne bayan da DSS ta sako wani matashin mai suna Bashir…
Read More

Rundunar ‘Yan sanda ta roƙi mazauna Abuja kar su shiga zanga-zanga kan tsadar rayuwa

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Kwamishinan 'Yan sandan birnin tarayya, Abuja, Bennet Igweh ya roƙi al'ummar jihar kar su shiga zanga-zangar da aka shirya za a yi a watan Agusta kan tsadar rayuwa a faɗin Nijeriya. Igweh ya nuna damuwarsa kasancewar ɓata gari ka iya amfani da zanga-zangar wajen tarwatsa sabbin ayyukan cigaba da a ka yi a faɗin jihar. Kwamishinan, ya bayyana hakan ne a yayin hira da manema labarai a ranar Litinin a lokacin da rundunar ta gurfanar da mutane da dama kan zargin fashi a hedkwatar ofisoshinta da ke birnin. Ya ce, suna aiki tuƙuru wajen kamo ƴan…
Read More

‘Yan sandan Kano sun kama fursunan da ya tsere daga kurkukun Kuje, wanda ya kitsa kashe janar na soja

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Rundunar 'Yan sanda ta yi nasarar kama wanda aka zarge shi da kitsa kisan marigayi Burgediya Janar Harold Udokwere, mai suna Hashiru Baku wanda yana ɗaya daga cikin waɗanda suka tsere daga kurkukun Kuje a kwanakin baya. Jaridar 'News Point Nigeria' ta ruwaito yadda ƴan bindiga suka shiga gidan janar Harold tare da kashe shi a unguwar rukunin gidajen Sunshine da ke Abuja a ranar 21 ga watan Yuni, inda Ƴan sanda ƙarƙashin kwamishinan rundunar Abuja, Bennet Igweh su ka kama waɗanda ake zargi kwana biyu bayan aukuwar lamarin. A lokacin da aka gurfanar da ƴan…
Read More

ASUU ta janye yajin aikin Jami’ar Abuja da aka ɗauki kwanaki 82 ana yi

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Jami'ar Abuja ɓangaren ƙungiyar malaman jami'o'i ta sanar da dakatar da yajin aikin da aka ɗauki tsawon kwanaki 82 ana yi inda ta ce nan da nan za a dawo bakin aiki. Shugaban ƙungiyar, Dakta Sylvanus Ugo ya faɗi haka a yayin ganawa da manema labarai bayan kammala wani zama na ƙungiyar a Abuja inda ASUU tare da majalisar zartarwar Jami'ar su ka tattauna yayin da majalisar ta yi alƙawarin yin duba ga buƙatunsu tare da samar musu da mafita a kan su. A ranar biyu ga watan Mayu, 2024 ne aka shiga yajin aikin sakamakon…
Read More

Gwamnatin Tarayya ta jagoranci ganawa kan taƙaddamar matatar Ɗangote da NMDPRA

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Gwamnatin Tarayya ta shiga tattaunawa kan taƙaddamar da ke tsakanin hukumar man fetur ta NMDPRA da sabon matatar Ɗangote wanda ƙaramin ministan albarkatun man fetur, Heineken Lokpobiri ya jagoranta wanda Alhaji Aliko Ɗangote da shugabannin NMDPRA suka halarta. An shirya zaman ne da nufin wanzar da haɗin kan ɓangarorin biyu da kuma warware ɓoyayyun matsalolin da ka iya shafar ayyukan matatar wanda ake tsammanin hakan zai taimaka wajen kawo ƙarshen dogaro da dangogin mai daga ƙasashen waje da Nijeriya ke yi. Wata takarda da mai bai wa ƙaramin ministan shawara kan yaɗa labaru, Nneamaka Okafor, ya…
Read More

Zanga-zangar tsadar rayuwa: Ya kamata gwamnati ta yi abin da ya dace – Gamayyar Ƙungiyoyin Arewa

Daga SANI AHMAD GIWA Shugaban gamayyar ƙungiyoyin Arewa (CNG), Kwamared Jamilu Aliyu Charanci, ya yi kira ga gwamnatin Nijeriya da Shugaba Bola Ahmed Tinubu da su tashi tsaye su yi duk mai yiwuwa domin hana abin da ke shirin faruwa a ƙasar. Kwamared Aliyu ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai da ƙungiyar ta kira a cikin makon nan, a lokacin da ake tsaka da batun gudanar da zanga-zanga a faɗin ƙasar kan tsadar rayuwa da taɓarɓarewar harkar tsaro da ake fama da su musamman a Arewacin ƙasar. Shugaban ƙungiyar ya ce, sanin kowa ne al'umma tana cikin…
Read More

Rikicin APC a Zamfara: Marafa ya naɗa kwamitin jagorancin jam’iyyar na ɓangarensa

Daga SANUSI MUHAMMAD A. GUSAU A ranar Asabar ne Sanata Kabiru Garba Mafara ya kafa kwamitin mutum 21 na jam'iyyar APC mai kula da ɓangarensa a jihar Zamfara. Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala taron sirri da mambobin kwamitin, shugaban kwamitin, Hon. Surajo Maikatako ya bayyana cewa rashin adalci da kyakkyawan shugabancin jam’iyyar da shugaban Jam'iyar ke yi a jihar ne ya jawo rabuwar ɓangaren Sanata Kabiru Garba Marafa. A cewarsa, kwamitin zai bai wa haɗin kai da cigaban jam’iyyar muhimmanci a jihar, yana mai jaddada cewa kwamitin zai yi bakin ƙoƙarinsa wajen ganin an yi…
Read More

An umarci bankuna su tura ƙuɗaɗen asusun da aka daina amfani da su ga CBN

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI An umarci bankunan Nijeriya da cibiyoyin harkokin kuɗi su mayar da ƙuɗaɗen asusun da aka daina amfani da su da waɗanda ba a bayyana mallakar su ba da wasu kadarori ga babban bankin Nijeriya, CBN. Jawabin ya fito ne cikin wani saƙon umarni da ke ɗauke da sanya hannun Daraktan sashen tsarin kuɗaɗe da gudanar da bankuna, John Onojah inda ya ce duk asusun da ƙuɗaɗen da ba a bayyana mallakar su ba da suka kai shakara goma, za a gadar da su ga asusu mai suna; 'Unclaimed Balances Trust Fund Pool Account' (UBTF). Bankin ya…
Read More

TCN ya yi barazanar sauke kamfanin lantarki na Abuja daga tashar wuta ta ƙasa

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Kamfanin raba wutar lantarki na ƙasa, TCN, ya aika saƙon dakatarwa ga kamfanin lantarkin Abuja, AEDC kan zargin ƙin biyayya ga dokokin kasuwa. TCN ya ce, AEDC ya gaza samar da tsarin gudanar da kasuwa da isasshen tabbacin shaidar banki kamar yadda sakin layi na 15.3.3 na dokar kasuwanci ya nuna. Haka nan, an sanar da AEDC batun matsalar kuma an bashi kwanakin aiki biyar ya gyara ko kuma a sauke shi daga tashar. Jawabin ya ƙara da cewa, wa'adin zai ƙare ne a ranar 28 ga watan Yuli, da tsakiyar dare. Kazalika, AEDC ya sha…
Read More