Babaji

4782 Posts

‘Yan sanda sun tabbatar da garkuwa da ƴan jarida biyu da iyalansu a Kaduna

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI 'Yan sandan jihar Kaduna sun tabbatar da sace wasu ƴan jarida biyu tare da iyalansu da aka yi a ranar Asabar da misalin ƙarfe 10:30 na dare. Mai magana da yawun rundunar Mansir Hassan ya faɗi hakan a yayain wata hira da 'News Agency of Nigeria' inda ya ce jami'ansu na ƙoƙari wajen ganin an ceto su daga waɗanda suka yi garkuwa dasu wanda a yanzu haka an watsa tawagar ƴan sandan a yankunan da ake tsammanin suna nan. Mansir ya ce, ɗaya da cikin su shi ne Abdulgafar Alabelewa, shugaban wakilan 'Chapel' na ƙungiyar ƴan…
Read More

Gwamnan Zamfara ya aika saƙon gaisuwar sabuwar shekara ga al’ummar Musulmi

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya aika saƙon fatan alkhairi ga al'ummar Musulmin jihar bayan shiga shekarar Hijira ta fiyayyen halitta, Annabi Muhammad (SAW), 1446. Gwamnan, ya yi kira ga al'ummar Musulmi a jihar da ma Nijeriya baki ɗaya da su cigaba da yi wa ƙasa addu'a domin samun zaman lafiya a dukkan sassan da ake fama da matsalolin tsaro. Wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ta ce sabuwar shekarar Musuluncin lokaci ne na yin nazari ga abubuwan da suka faru a shekarar da ta gabata. Yau Lahadi ce ranar…
Read More

Kuto ta umarci Sadiya Farouk ta yi bayanin yadda aka sarrafa biliyan N729 ga talakawa

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Babbar kotun jihar Legas ta umarci tsohuwar ministar ma'aikatar jinƙai da ci gaban ƙasa, Sadiya Farouk ta yi bayani dalla-dalla kan yadda ta sarrafa Naira biliyan 729 ga talakawan Nijeriya miliyan 24.3 a cikin wata shida. Cikin bayanan da kotun ta buƙaci tsohuwar ministar ta yi sun haɗa da; adadin waɗanda suka ci moriyar kuɗin, jihohin da aka bai wa kasafi da kuma nawa aka bai wa kowacce. Alƙali Deinde Dipeolu ya yi hukuncin bayan da cibiyar tabbatar adalci da Mulki Nagari (SERAP) ta buƙaci a yi hakan ƙarƙashin dokar ƴancin sanarwa ta FHC/L/CS/853/2021. Mataimakin Daraktan…
Read More

Da ƊUMI-ƊUMI: Tinubu ya yi murabus daga shugabancin ECOWAS

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Wa'adin Shugaba Bola Ahmed Tinubu a matsayinsa na shugaban ƙungiyar raya tattalin arziƙin ƙasashen Afrika ta yamma (ECOWAS), ya ƙare a ranar 7 ga watan Yuli, 2024. Za a gudanar da taron ƙungiyar karo na 65 da aka saba yi, a fadar shugaban Nijeriya da ke Abuja inda a nan Tinubu zai miƙa ragamar shugabancin ECOWAS a hannun wanda zai gaje shi. A watan Yulin 2023 ne aka zaɓi shugaba Tinubu a matsayin shugaban ƙungiyar a zamanta na 63 a Bissau, babban birnin ƙasar Guinea-Bissau.
Read More

An yi auren tsohuwar jarumar Kannywood, Sadiya Gyale

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI A ranar juma'a, 5 ga Yuli, 2024 ne aka ɗaura auren tsohuwar tauraruwar Kannywood, Sadiya Gyale da angonta mai suna Mustafa Umar Kawu bayan sallar juma'a, a masallacin sharaɗa 'Phase 3' da ke jihar Kano. Sadiya Muhammad, wacce aka fi sani da Sadiya Gyale, ta kasance ɗaya daga cikin taurarin da ke da basira wajen yin shiri mai kyau a kowane ɓangare aka saka ta a fim. Tauraruwar ta yi baya da harkar fim ne bayan da aka yi aurenta na farko a shekarar 2015 da wani Barista Abubakar da ke aiki a jihar Kaduna. Sai…
Read More

An mayar da wutar lantarkin Jami’ar Ɗangote bayan katse ta da KEDCO ya yi

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Kamfanin raba wutar lantarki na jihar Kano, KEDCO ta sake haɗa wa Jami'ar kimiyya da fasaha ta Ɗangote da ke Wudil wutar lantarkinta bayan da aka biya Naira miliyan 100. Mataimakin Shugaban makarantar (VC), Farfesa Musa Yakasai ya tabbatar da haka a wata hira ta waya da gidan 'News Agency Nigeria' a ranar juma'a inda ya ce KEDCO ta mayar da wutar ne da misalin ƙarfe 4 na yamma bayan da aka biya kuɗin. KEDCO ta katse wutar ne bayan ikirarin cewa akwai bashin Naira miliyan 248 a kan jami'ar. Sannan, a watan, duk da an…
Read More

Buɗaɗɗiyar wasiƙa kan halifofin sharholiya

Daga NASIR ABDULLAHI GAYAWA Zuwa ga Dakta Lawi Abubakar AtikuUnguwar Sanka, Kano1 ga Yuli, 2024 Assalamu Alaikum, Wataƙila Maulana ya yi mamakin samun wannan buɗaɗɗiyar wasiƙa. Sunana Nasir Abdullahi Gayawa, ɗan asalin Ƙaramar Hukumar Nasarawa, Jihar Kano; ɗalibi mai neman digiri na biyu a Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Houari Boumedeine, Bab Zouer, a Algiers, Algeria. Na ziyarce ku a birnin Algiers, lokacin bikin tunawa da Shaykh Abdulkarim Al-Maghili, a Disamban 2022 inda muka tattauna abubuwa da dama ciki har da matsalolin da ƴan uwa ke takaicin afkuwar su a ɗariƙarmu ta Tijjaniyya. Kasa samun ku a waya da rashin…
Read More

Majalisar dokokin Ribas ɓangaren Fubara za su ƙalubalanci hukuncin kotu kan nasarar Amaewhule

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Wani ɓangare na majalisar dokokin jihar Ribas ƙarƙashin jagoranci Vickto Oko-Jumbo ya ce ba su amince da hukuncin kotun ɗaukaka kara ba biyo bayan sanar da Martins Amaewhule a matsayin halstaccen kakakin majalisar. Oko-Jumbo wanda shi ɗan bangaren gwamnan jihar, Siminalayi Fubara ne ya faɗi hakan a yayin wani zaman majalisar a Fatakwal, babban birnin jihar. A ranar Alhamis ne kotun ta yi watsi da hukuncin babbar kotun jihar wacce ta sanar cewa Amaewhule da wasu ƴan majalisu 24 ba sa cikin mambobin majalisar dokokin jihar. Kotun ɗaukaka ƙarar, ta ce babbar kotun jihar ba ta…
Read More

Da ƊUMI-ƊUMI: Ronaldo da Pepe sun yi adabo da gasar Turai bayan doke Portugal da Faransa ta yi

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Yayinda shahararren ɗan ƙwallon ƙafan duniya Christiano Ronaldo da takwaransa na ƙasar Portugal, Pepe ke shirin bankwana da buga wasa, ƴan wasan sun yi rashin nasara a hannun Faransa a wasan daf da na kusa da na ƙarshe a gasar kofin Nahiyar Turai na 2024. Portugal ta sha kaye ne a bugun daga-kai-sai-mai-tsaron-gida bayan shafe mintuna 120 ba a samu wanda ya zura ƙwallo ba, inda daga baya Faransa ta doke ta da ci 5 da 3. Wannan ita ce gasar kofin ƙasashe ta ƙarshe da ƴan wasan biyu su ka sha alwashin ajiye aikinsu da…
Read More

Babu auren jinsi: Dokokin Nijeriya sun fi ƙarfin Yarjejeniyar Samoa, inji Ministan Labarai

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Gwamnatin tarayya ta bayyana matsayarta game da batun yarjejeniyar ƙasar Samoa inda ta ce dokokin Nijeriya kan auren jinsi sun fi ƙarfin a tanƙwara su. Yarjejeniyar, ta ƙunshi dokar sanya ƙasashen da ba su ci gaba ba da masu tasowa su amince da auren jinsi (LGBT), wanda yin hakan shi zai bada lasisin samun agajin kuɗi da wasu nau'uka na taimako daga ƙasashen da su ka ci gaba. Takardar yarjejeniyar Samoa ta na samun karɓuwa a wasu ƙasashe, sai dai ƙasashe da dama sun ƙi amincewa da ita kasancewar auren jinsi abu ne da ya ci…
Read More