10
Jul
Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Wasu bishiyu uku a kasuwar Jattu dake ƙaramar hukumar Etsako ta yamma a jihar Edo, sun yi sanadiyar mutuwar mutum huɗu bayan da suka faɗo a kan ƴan shan inuwa da masu shaguna. Wani adadi da ba a tantance ba na mutane sun samu raunuka a yayin aukuwar ibtila'in. Blueprint ta ruwaito cewa yayinda ake ruwan sama da misalin ƙarfe takwas na safe, masu saye da sayarwa sun fake a ƙarƙashin rumfunan bishiyun inda aka yi wani tsawa da ya yi sanadiyar faɗuwarsu wanda a sakamakon haka ne aka rasa rayukan. Wani mai suna Sule, ya…
