22
Mar
Daga FATUHU MUSTAPHA Gwamnatin Tarayya ta bada tabbacin cewa nan bada daɗewa ba, za ta soma aikin gyran gadar hanyar zuwa filin jirgin sama a birnin Legas wadda ta ƙone a lokutan baya. Babban Sakataren Ma'aikatar Ayyuka a Gidaje ta Tarayya, Alhaji Babangida Hussaini, shi ne ya faɗi haka yayin wani rangadi da ya yi a Legas domin duba wasu ayyukan gidaje da hanyoyi da ke gudana a jihar. Gadar da lamarin ya shafa ta ci wata ne sakamakon haɗarin tankar mai da ya auku a Janairun da ya gabata, kuma a wancan lokaci aka rufe gadar aka hana abubuwan…
