15
Feb
Daga BELLO WANG A kwanakin baya an kawo ƙarshen taron ƙolin ƙungiyar AU na 35 a ƙasar Habasha, inda mahalarta taron suka sanya wa shekarar 2022 da muke ciki taken “shekarar tabbatar da samun isashen abinci masu gina jiki”, don jaddada muhimmancin tsaron abinci a nahiyar Afirka. Haƙiƙa a cikin shekarar da ta gabata, annobar COVID-19 ta haifar da mummunar illa ga tattalin arzikin ƙasashen Afirka, lamarin da ya sanya mutanen ƙasashen kimanin miliyan 30 zuwa miliyan 40 fuskantar yunwa. Wannan yanayi ya haɗa da bala’i daga indallahi, sun sa ake fuskantar ƙaruwar matsalolin rashin tsaron abinci da ta kai…
