Rahoto

Haɗin kan Afirka da Sin na tabbatar da tsaron abinci a Nahiyar Afirka

Haɗin kan Afirka da Sin na tabbatar da tsaron abinci a Nahiyar Afirka

Daga BELLO WANG A kwanakin baya an kawo ƙarshen taron ƙolin ƙungiyar AU na 35 a ƙasar Habasha, inda mahalarta taron suka sanya wa shekarar 2022 da muke ciki taken “shekarar tabbatar da samun isashen abinci masu gina jiki”, don jaddada muhimmancin tsaron abinci a nahiyar Afirka. Haƙiƙa a cikin shekarar da ta gabata, annobar COVID-19 ta haifar da mummunar illa ga tattalin arzikin ƙasashen Afirka, lamarin da ya sanya mutanen ƙasashen kimanin miliyan 30 zuwa miliyan 40 fuskantar yunwa. Wannan yanayi ya haɗa da bala’i daga indallahi, sun sa ake fuskantar ƙaruwar matsalolin rashin tsaron abinci da ta kai…
Read More
Ana wata ga wata: NDLEA na neman DCP Abba Kyari wurjanjan bisa zargin safarar miyagun ƙwayoyi

Ana wata ga wata: NDLEA na neman DCP Abba Kyari wurjanjan bisa zargin safarar miyagun ƙwayoyi

*Kyari ya faɗa a komarmu - 'Yan Sanda Daga BASHIR ISAH Kawo yanzu dai DCP Kyari ya faɗa a komar 'yan sanda, 'yan sa'o'i bayan da Hukumar Yaƙi da Sha da Safarar Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA) ta bada sanarwar tana nemansa ruwa a jallo bisa zargin fataucin muguwar ƙwaya. Majiyar MANHAJA ta ce an ga lokacin da aka shigo da Kyari babban ofishin 'yan sanda da ke Abuja da ankwa a hannunsa. Tun farko dai Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA), ta bada sanarwar tana neman dakataccen Mataimakin Kwamishinan ‘yan sandan nan, wato DCP…
Read More
’Yan bindiga sun kashe ladani a Zamfara

’Yan bindiga sun kashe ladani a Zamfara

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Wasu gungun ‘yan bindiga sun kai hari a cikin wani masallaci a Larabar da ta gabata a cikin garin Magazu a Ƙaramar Hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara, inda suka kashe ladani mai suna Abubakar Muhammad wanda aka fi sani da Abu Dogo ɗan shekara 25. Wani mazaunin garin na Magazu mai suna Malam Isma’il Magazu a wata hira ta wayar tarho da Blueprint Manhaja ya ce ‘yan ta’addan sun kai hari masallacin ne da misalin ƙarfe 5:40 na safiyar ranar ta Laraba. "Kamar yadda nake magana da kai yanzu, an yi jana'izar Marigayi Malam Abu…
Read More
Muhammadu Sanusi ya hango wa Nijeriya tarnaƙin ƙura gabanin zaɓen 2023

Muhammadu Sanusi ya hango wa Nijeriya tarnaƙin ƙura gabanin zaɓen 2023

Daga BAKURA K. MUHAMMAD a Bauchi Sarkin Kano mai murabus, Alhaji Muhammadu Sanusi II, ya yi hasashen tarin ƙalubaloli da Nijeriya za ta fuskanta gabanin zaɓen shekara ta 2023, yana mai cewar, akwai buƙatar ‘yan takara su yi kyakkyawan shiri domin tunkarar su. Sanusi ya kuma fahimci cewar, ƙasar ta Nijeriya tana zaman bakin kogi ne da lokacin irin wannan zama ya ƙure. Tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriyar dai yana jawabi ne a garin Abeokuta ta jihar Ogun, a wani taron liyafa na cika shekaru 80 da rayuwar wani babban basarake, Babanla Addini Mai Ƙasar Egba, Chief Tayo Sowunmi. Tsohon…
Read More
Gidauniyar Fasaudat ta tallafa wa ‘yan gudun hijra a Sakkwato

Gidauniyar Fasaudat ta tallafa wa ‘yan gudun hijra a Sakkwato

Daga AMINU AMANAWA a Sakkwato 'Yan gudun hijira dake zaune a Ramen Kura a jihar Sakkwato sun samu tallafin abinci da tufafin sawa daga Gidauniyar tallafa wa marasa ƙarfi daga gidauniyar ta Fasaudat. Baya ga kayan abinci haka ma gidauniyar ta tallafa wa yaran 'yan gudun hijirar da tufafin sawa. Da take ƙaddamar da tallafin shugabar gidauniyar Hajiya Fatima Ahmed Maigari ta yi kira ga matan 'yan gudun hijira da su kula da karatu da kuma tarbiyyar 'ya'yansu. "Ina mai kira a gareku da kada ku dubi halin da kuke cike, ku yi amfani da damar ku wajen sauke nauyin…
Read More
Ranar Hijabi: Ɗalibai suna da ‘yancin sanya hijabi a makarantu – Gwamna Makinde

Ranar Hijabi: Ɗalibai suna da ‘yancin sanya hijabi a makarantu – Gwamna Makinde

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamna Seyi Makinde na Jihar Oyo a ranar Talata ta makon jiya ya tabbatar wa mazauna jihar cewa gwamnatinsa ba za ta take musu haƙƙinsu na addini ba. Makinde ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da mai taimaka masa na musamman kan harkokin addinin Musulunci, Abdulrasheed Abdulazeez, ya fitar domin bikin ranar Hijabi ta duniya ta 2022. “Hijabi sutura ce da ba wai kawai tana ƙawata mai sakawa ba, har ma tana taimakawa wajen ci gaban ɗa’a a cikin al’umma,” inji Makinde. Gwamnan ya taya al’ummar musulmin jihar murna musamman mata, ya…
Read More
WHO ta ziyarci Zannan Askar Sarkin Gombe

WHO ta ziyarci Zannan Askar Sarkin Gombe

Daga MOHAMMED ALI a Gombe Zannan Askan mai Martaba Sarkin Gombe, kuma Sarkin Askan Bolari ta Gabas a Jihar Gombe, Dokta Yunusa Adamu, ya nuna matuƙar farin cikin shi akan ziyarar da Hukumar Lafiya ta Duniya, wato World Health Organization (WHO) ta kai mishi a harabar warakar shi kwanan nan, inda jami’an hukumar suka yi bincike da nazari a kan irin ayyukan shi daga bisani kuma suka gamsu da su. Malam Yunusa Adamu wanda ya yi wannan tsokacin a Gombe a makon jiya yayin wata zantawa da ya yi da manema labarai, ya furta cewa, ziyarar da jami’an na WHO…
Read More
`Yan sanda sun cafke ɓarawon da ke amfanin da katin ATM ɗin jama’a a Katsina

`Yan sanda sun cafke ɓarawon da ke amfanin da katin ATM ɗin jama’a a Katsina

Daga UMAR GARBA a Katsina Rundunar 'yan sandan Jihar Katsina ta kama wani matashi ɗan damfara wanda ke zuwa banki da nufin taimakon waɗanda ba su iya amfani da na'urar cirar kuɗi ta ATM ba amma daga bisani ya ɓuge da yi masu canjin katin banki 'ATM Card' na boge, inda bayan ya yi ma su musayar kati sai ya tafi wajen ma su POS ya yashe masu asusun ajiyarsu na banki. Aminu Rabiu dake zaune a Ɗanɗagoro ya shigar da ƙorafi a babban ofishin 'yan sanda dake birnin Katsina, inda Aminu ya bayyana wa 'yan sanda cewar ya je…
Read More
Fatanmu shine yi wa marayu da gajiyayyu gata – Hadiza Rumah

Fatanmu shine yi wa marayu da gajiyayyu gata – Hadiza Rumah

Daga BABANGIDA A. GORA a Katsina A ranar Asabar ɗin makon jiya ce gidaunyar 'Voice of the Voiceless' wato gidauniyar da ke share wa marasa gata hawayen su, ta yi taron taimakon matan sojojin da su ka mutu suka bar iyalan su don kare martar ƙasar su da al'ummar ƙasa. Gidauniyar wadda ke gudanar da ayyukanta a jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Hajiya Hadiza Rumah, ta kuma ba 'yan gudun hijira tallafin kayan abinci da sauran kayan da zai rage ma su raɗaɗin rayuwa. Hajiya Hadiza ta kuma ce wannan gidauniya ta shafe shekaru sama da goma tana gudanar da ayyukanta…
Read More
Matakan da gwamnati ke ɗauka kan tsaro ya taimaka wajen haɓaka kasuwancin kayan gwari – Shugaba

Matakan da gwamnati ke ɗauka kan tsaro ya taimaka wajen haɓaka kasuwancin kayan gwari – Shugaba

Daga AMINU AMANAWA a Sakkwato Shugaban kasuwar kayan gwari ta ƙasa da ƙasa ta Mile 12 da ke Legas, Alh Shehu Usman Jibril, ya bayyana cewa matakan da gwamnati ke ɗauka na inganta lamurran tsaro a Nijeriya ya taimaka wa lamurran kasuwancin kayan gwari, musamman na iya safarar su daga jihohin Arewa dake fama da matsalar tasaro zuwa kasuwar kayan gwari ta Mile 12. Shugaban ya bayyana hakan ne a wajen taron shekara-shekara da jagororin kasuwar ke gudanarwa a duk shekara domin tattauna nasarori da irin ƙalubalen da masu noma da kasuwancin kayan gwarin ke fuskanta, taron da a wannan…
Read More