Rahoto

WHO ta ziyarci Zannan Askar Sarkin Gombe

WHO ta ziyarci Zannan Askar Sarkin Gombe

Daga MOHAMMED ALI a Gombe Zannan Askan mai Martaba Sarkin Gombe, kuma Sarkin Askan Bolari ta Gabas a Jihar Gombe, Dokta Yunusa Adamu, ya nuna matuƙar farin cikin shi akan ziyarar da Hukumar Lafiya ta Duniya, wato World Health Organization (WHO) ta kai mishi a harabar warakar shi kwanan nan, inda jami’an hukumar suka yi bincike da nazari a kan irin ayyukan shi daga bisani kuma suka gamsu da su. Malam Yunusa Adamu wanda ya yi wannan tsokacin a Gombe a makon jiya yayin wata zantawa da ya yi da manema labarai, ya furta cewa, ziyarar da jami’an na WHO…
Read More
`Yan sanda sun cafke ɓarawon da ke amfanin da katin ATM ɗin jama’a a Katsina

`Yan sanda sun cafke ɓarawon da ke amfanin da katin ATM ɗin jama’a a Katsina

Daga UMAR GARBA a Katsina Rundunar 'yan sandan Jihar Katsina ta kama wani matashi ɗan damfara wanda ke zuwa banki da nufin taimakon waɗanda ba su iya amfani da na'urar cirar kuɗi ta ATM ba amma daga bisani ya ɓuge da yi masu canjin katin banki 'ATM Card' na boge, inda bayan ya yi ma su musayar kati sai ya tafi wajen ma su POS ya yashe masu asusun ajiyarsu na banki. Aminu Rabiu dake zaune a Ɗanɗagoro ya shigar da ƙorafi a babban ofishin 'yan sanda dake birnin Katsina, inda Aminu ya bayyana wa 'yan sanda cewar ya je…
Read More
Fatanmu shine yi wa marayu da gajiyayyu gata – Hadiza Rumah

Fatanmu shine yi wa marayu da gajiyayyu gata – Hadiza Rumah

Daga BABANGIDA A. GORA a Katsina A ranar Asabar ɗin makon jiya ce gidaunyar 'Voice of the Voiceless' wato gidauniyar da ke share wa marasa gata hawayen su, ta yi taron taimakon matan sojojin da su ka mutu suka bar iyalan su don kare martar ƙasar su da al'ummar ƙasa. Gidauniyar wadda ke gudanar da ayyukanta a jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Hajiya Hadiza Rumah, ta kuma ba 'yan gudun hijira tallafin kayan abinci da sauran kayan da zai rage ma su raɗaɗin rayuwa. Hajiya Hadiza ta kuma ce wannan gidauniya ta shafe shekaru sama da goma tana gudanar da ayyukanta…
Read More
Matakan da gwamnati ke ɗauka kan tsaro ya taimaka wajen haɓaka kasuwancin kayan gwari – Shugaba

Matakan da gwamnati ke ɗauka kan tsaro ya taimaka wajen haɓaka kasuwancin kayan gwari – Shugaba

Daga AMINU AMANAWA a Sakkwato Shugaban kasuwar kayan gwari ta ƙasa da ƙasa ta Mile 12 da ke Legas, Alh Shehu Usman Jibril, ya bayyana cewa matakan da gwamnati ke ɗauka na inganta lamurran tsaro a Nijeriya ya taimaka wa lamurran kasuwancin kayan gwari, musamman na iya safarar su daga jihohin Arewa dake fama da matsalar tasaro zuwa kasuwar kayan gwari ta Mile 12. Shugaban ya bayyana hakan ne a wajen taron shekara-shekara da jagororin kasuwar ke gudanarwa a duk shekara domin tattauna nasarori da irin ƙalubalen da masu noma da kasuwancin kayan gwarin ke fuskanta, taron da a wannan…
Read More
An ƙaddamar da shugabannin jam’iyyar ’yan citta na Arewa maso Yamma

An ƙaddamar da shugabannin jam’iyyar ’yan citta na Arewa maso Yamma

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Gwamnatin Jihar Kano tana gudanar da ayyuka a fannoni daban-daban don sauƙaƙa wa da bunƙasa harkar kasuwanci a jihar.  Kwamishinan ma'aikatar kasuwanci na jihar Barista Ibrahim Muktar ya bayyana hakan a waje taron ƙaddamar da shugabannin ƙungiyar masu citta na ƙasa  na shiyyar jihohin Arewa maso Yamma. Ya ce jihar Kano cibiya ce ta kasuwanci mai daɗaɗɗen tarihi da kuma take cigaba da jan ragamar kasuwanci duk da halin tattalin arziƙi da ake ciki. Gwamnatin Jihar Kano na gudanar da muhimman ayyuka da suka haɗa da hanyoyi da kuma gina tasha ta tsandauri a garin…
Read More
Da maganin ɓera na N100 na kashe Hanifa, inji Abdulmalik Tanko

Da maganin ɓera na N100 na kashe Hanifa, inji Abdulmalik Tanko

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano A ranar Asabar, 4 ga watan Disamban 2021 ne aka sace Hanifa 'yar shekara biyar a unguwar Kawaji da ke birnin Kano. Mutanen sun ɗauke Hanifa Abubakar ne da misalin ƙarfe 5:00 na yamma bayan sun isa wurin a cikin babur mai ƙafa uku da aka fi sani da a-daidaita-sahu, inda ta kwana 47 a wajensu. Iyayen Hanifa sun ce mutanen sun sace ta ne jim kaɗan bayan ta dawo daga makarantar Islamiyya tare da sauran yaran maƙota. Marigayiya Hanifa "Babu nisa tsakanin makarantar da gidansu (Hanifa), saboda haka yaran sun saba zuwa da ƙafarsu,"…
Read More
Bauchi da Gombe sun buƙaci Gwamnatin Tarayya da NNPC su duƙufa haƙo man fetur a jihohin

Bauchi da Gombe sun buƙaci Gwamnatin Tarayya da NNPC su duƙufa haƙo man fetur a jihohin

Daga BAKURA K. MUHAMMAD a Bauchi Maƙotan jihohin nan na Bauchi da Gombe da ke shiyyar Arewa maso gabashin Nijeriya sun haɗa bakunansu suna masu kira wa Gwamnatin Tarayya da ta yi wa Allah da Annabin Sa, ta shawo kan Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPC) domin ya duƙufa tono ɗimbin man fetur da na gas da ke danƙare a sassan jihohin su. Man fetur da na gas dai, waɗanda aka gano a sassa da gangajiyar abokan jihohin biyu a lokatai masu tsawo da suka gabata, kuma Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPC) ya tabbatar da ɗimbin yawan su a…
Read More
Manyan abin kunyar iyali shida da suka girgiza 2021 a Nijeriya

Manyan abin kunyar iyali shida da suka girgiza 2021 a Nijeriya

Wasu fitattun iyalai a Nijeriya sun tsunduma cikin cece-kuce da ya sa aka shiga kace-nace a Nijeriya kan halin da su ke ciki a wani lokaci a bara, 2021. Kafofin yaɗa labarai, musamman kafafen sada zumunta sun yi ta magana kan rigingimun. Wasu daga cikinsu batun na su bai daɗe ba aka watsar, inda wasu kuwa har yanzu ana ɗaga batun. Tsohon Sufeto Janar Idris Kpotun da amaryarsa Asta:Tsohon Sufeto Janar na ’yan sandan Nijeriya, Ibrahim Idris Kpotun ya shiga cikin rikicin aure da matarsa ne tun a shekarar 2017, lokacin da ya auri Amina Asta, mataimakiyar Sufurtandan ’yan sanda…
Read More
Yadda aka gudanar da bikin aure da ƙaddamar da littafin Editan Blueprint Manhaja a Kano

Yadda aka gudanar da bikin aure da ƙaddamar da littafin Editan Blueprint Manhaja a Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano  A Asabar ɗin da ta  gabata, 25 ga Disamba, 2021, ne aka ɗaura aure tare da ƙaddamar da littafi mai suna Ruwan Jakara, wanda marubuci kuma Editan jaridar Blueprint Manhaja, wato Nasir Sa'ad Gwamgwazo, ya rubuta. An dai ɗaura auren ne a Masallacin Wudilawa da ke kusa da gidan Sarkin Kano, daura da Gidan Makama, yayin da aka yi walima da ƙaddamar da littafin a babban ɗakin taro na Kannywood TV da ke unguwar Tudun Yola kusa da Ƙofar Kabuga akan hanyar zuwa Jami’ar Yusuf Maitama Sule da ke cikin birnin Kano. Tun da farko a…
Read More
Haramta amfani da gawayi a Jihar Nasarawa ya fara janyo guna-guni

Haramta amfani da gawayi a Jihar Nasarawa ya fara janyo guna-guni

Daga IBRAHIM HAMZA MUHAMMAD a Lafia A kwanakin baya ne Gwamnatin Jihar Nasarawa ta haramta yin tu'ammali ko kuma sarrafawa, saye, sayarwa ko yin amfani da gawayi a matsayin makamashi a jihar bakiɗaya. Babban Sakatare a Ma'aikatar Muhalli da Albarkatun Ƙasa, Alhaji Aliyu Agwai, ne ya bayyana haka garin Lafiya, babban birnin jihar, inda ya ce daga yanzu haramun ne sarrafawa da saye da sayarwa da kuma yin amfani da gawayi a jihar. A cewarsa, yadda ake samar da gawayi yana tattare da illoli da dama ga muhalli, gurɓata yanayi da kuma ƙara zafafa yanayi. Babban Sakataren ya ƙara da…
Read More