Rahoto

Tsadar abincin kifi zai haddasa rashin sa a Ramadan – PFFAN

Tsadar abincin kifi zai haddasa rashin sa a Ramadan – PFFAN

Daga MUHAMMADU MUJITABA a Kano  Ma su sana'ar kiwon kifi sun koka kan yadda kamfanonin sarrafa abincin kifi ke tsawwala farashin kayan abincin kifi, inda suka bayyana cewa hakan zai iya kawo matsanancin tsadar kifi a watan Ramadan mai zuwa. Wannan koke ya fito ne daga bakin shugabannin ƙungiyar masu sana`ar kiwon kifi a Nijeriya na ƙasa reshen Jihar Kano, wato Piratic Farmers Fish Association Of Nigeria, PFFAN a lokacin taron ƙungiyar da suka gabatar a Kano cikin makon jiya. Hudu Salisu Khalid, shi ne kakakin ƙungiyar ta PFFAN, ya ce suna fuskantar ƙalubale da matsaloli masu yawa a wannan…
Read More
2023: Yadda Mohammed Malagi ya mayar da APC tsintsiya maɗaurinki ɗaya a Jihar Neja

2023: Yadda Mohammed Malagi ya mayar da APC tsintsiya maɗaurinki ɗaya a Jihar Neja

Daga AMINA YUSUF ALI A kwanakin nan ne dai Shugaba kuma Mawallafin rukunin kamfanin jaridun Blueprint da Manhaja, Alhaji Mohammed Idris Malagi (MIM), ya kai wata ziyara zuwa reshen Jam'iyyar APC na Jihar Neja a Minna, Babban Birnin Jihar. Wakilinmu ya rawaito cewa, wannan ziyara ta Kakakin Nufe ta buɗe wani sabon shafi a kan muradinsa na nuna sha'awarsa ga takarar Gwamnan Jihar Neja a kakar zaɓe mai zuwa ta 2023.  Shigowar uban gayya:Da ƙarfe 7 na safiyar ranar Talatar, wato daidai da 22 ga watan Fabrairu shekara ta 2022, ƙofar shiga garin Minnan jihar Neja ta ɗinke da cincirindon 'yan…
Read More
Ƙarancin mai na cigaba da ta’azzara duk da alƙawarin NNPC

Ƙarancin mai na cigaba da ta’azzara duk da alƙawarin NNPC

Daga MAHDI M. MUHAMMAD a Abuja Duk da tabbacin da Kamfanin Man Fetur na Nijeriya (NNPC) ya bayar na cewa za a kawo ƙarshen ƙarancin man fetur a ƙarshen watan Fabrairu, amma har yanzu ’yan Nijeriya na fuskantar wahalar samun man. Shugaban kamfanin mai na NNPC Mele Kyari, ya bayyana a gaban kwamitin majalisar wakilai kan harkokin man fetur a ranar 16 ga watan Fabrairu, inda ya bada tabbacin kawo ƙarshen ƙarancin man nan da mako guda. Ya shaida wa kwamitin cewa tuni kamfanin ya karɓi lita biliyan 2.1 da za a raba domin daidaita al’amura. Ƙaranci yana ƙara muni:Duk…
Read More
Cikakken rahoto: Faruk Lawan bai nemi cin hanci daga Otedola ba, inji Kotun Ɗaukaka Ƙara

Cikakken rahoto: Faruk Lawan bai nemi cin hanci daga Otedola ba, inji Kotun Ɗaukaka Ƙara

Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Kotun Ɗaukaka Ƙarar, wacce ta ke zamanta a Abuja, Babban Birnin Tarayyar Nijeriya, ta tabbatar da cewa, masu gabatar da ƙara ba su iya tabbatar wa kotu da cewa, tsohon fitaccen ɗan Majalaisar Wakilai ta Nijeriya, Hon. Faruk Lawan, ya nemi attajirin nan, Mista Femi Otedola, ya ba shi cin hancin Dala Miliyan Uku, don ya zare sunan kamfaninsa, Zenon Oil and Gas Limited, daga jerin kamfanonin da suka damfari Nijeriya kan kuɗin tallafin mai ba a cikin rahoton Kwamitin Musamman na majalisar, wanda Hon. Lawan din ya jagoranta a 2012. Wannan dalili ya…
Read More
’Yan bindiga sun aurar da ’yan mata 13 daga cikin ɗaliban Yauri

’Yan bindiga sun aurar da ’yan mata 13 daga cikin ɗaliban Yauri

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Watanni 8 bayan da ‘yan bindiga suka yi awon gaba da ɗaliban sakandiren Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta birnin Yauri a jihar Kebbi, har yanzu ‘yan bindigar suna riƙe da fiye da 10 daga cikinsu, duk kuwa da biyan kuɗin fansa da aka yi, da kuma musayar fursunoni da aka yi a lokuta daban-daban. Wani bincike da jaridar ‘Daily Trust ta gudanar na nuni da cewa an aurar da kimanin ɗalibai  mata 13 ga ‘yan bindiga, kuma yanzu haka wasu daga cikinsu na da juna biyu. A ranar 17 ga watan Yunin shekarar da ta…
Read More
Gbajabiamila ya sake taɓa zukatun jama’a a mazaɓarsa

Gbajabiamila ya sake taɓa zukatun jama’a a mazaɓarsa

Daga BAKURA MUHAMMAD a Bauchi Kakakin Majalisar Dokoki ta Tarayya, Femi Gbajabiamila, a ranar Asabar da ta gabata ne ya kuma rarraba tallafi wa jama’ar mazaɓar sa ta Surulere 1 da ke birnin Ikko, inda ɗimbin mutane suka amfana. A wani ƙasaitaccen shiri na miƙa hannu wa jama’ar mazaɓar sa, wanda aka gudanar a filin wasa na Teslim Balogun dake birnin Ikko, an bayar da tallafin ƙaro ilimi wa ɗalibai 351dake jami’o’in gwamnati da a halin yanzu suke karatu a sassa daban-daban na ƙasar nan, yayin da shugabannin makarantun sakandare guda 1,020 aka ba su na’urorin kwmfuta domin su sauƙaƙa…
Read More
Kotun Minna ta yanke wa mutane 11 hukuncin kisa ta hanyar rataya

Kotun Minna ta yanke wa mutane 11 hukuncin kisa ta hanyar rataya

Daga BAKURA MUHAMMAD a Bauchi Babbar Kotu mai lamba 6 dake garin Minna a cikin jihar Neja ta yanke wa waɗansu mutane 11 daga ƙaramar hukumar Lavun hukuncin kisa ta hanyar rataya, bayan ta same su da ɗabagogin laifuka guda tara yayin zaman shari’ar. Kotun, ta kuma sallami wasu mutanen 15 waɗanda aka gurfanar tare da waɗanda aka yi wa hukuncin kisa, saboda rashin ƙwazo da rashin gurfanar da su bisa tsari ko ƙa’ida. Waɗanda aka yanke wa hukuncin kisa sune Mohammed Mohammed, Baba Mohammed, Mohammed Isah, (wanda aka fi sani da Madu), Abubakar Saba, Mohammed Adamu Babamini, Ibrahim Mohammed…
Read More
Koyi da Saudiyya: Za a fara fille kan masu ta’ammalli da miyagun ƙwayoyi a Kano

Koyi da Saudiyya: Za a fara fille kan masu ta’ammalli da miyagun ƙwayoyi a Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Ƙudirin dokar yaƙi da ta'ammali da miyagun ƙwayoyi, wanda ya ƙunshi kisa, ya tsallake karatu na biyu a zauren Majalisar Dokoki ta Jihar Kano. Majalisar Dokokin Jihar Kano dai ta ce za ta duba yiwuwar yin wata doka kwatankwacin irin ta Ƙasar Saudiyya da za a riƙa fille kan duk wanda aka same shi da ta'amalli da miyagun ƙwayoyi ko kuma safararsu.  Kakakin Majalisar Dokokin ta Jihar Kano, Rt. Hon. Injiniya Hamisu Ibrahim Chidari, shi ne ya bayyana hakan a lokacin da yake tsokaci kan yadda matasa da 'ya'yan masu faɗa-a-ji suke yawan ta'amilli da…
Read More
Pantami ya buƙaci matasa su mayar da hankali kan fasahar ƙirƙira

Pantami ya buƙaci matasa su mayar da hankali kan fasahar ƙirƙira

Daga UMAR GARBA a Katsina Pantami ya buƙaci matasa da su mayar da hankali akan sana'ar fasahar ƙirƙira a madadin dogaro da takardar shaidar kammala karatu.  Ministan Sadarwa na Nijeya, Isah Aliyu Pantami ya buƙaci gwamnati, matasa da sauran al'ummar ƙasar nan akan su mayar da hankali  wajen koyon sana'ar ƙirƙire-ƙirƙiren fasahar zamani a madadin mayar da hankali a kan takardar shaidar kammala karatu don samun ayyukan dogaro da kai. Pantami ya bayyana haka ne a sakatariyar gwamnatin jihar Katsina a wajen wani taron bada kyaututtuka ga waɗanda suka yi nasara a gasar zaƙulo matasa masu baiwar ƙirƙirar fasahar zamani…
Read More
Harshe na asali yana da daraja matuƙa

Harshe na asali yana da daraja matuƙa

Sharhi daga BELLO WANG Yau rana ce ta harshe na asali, wadda hukumar UNESCO ta keɓe don tunatar da al’ummun duniya muhimmancin kare yarensu na asali. Dalilin da ya sa harshe na asali ke da muhimmanci, shi ne yana da amfani wajen bambanta mu da sauran al’ummomi. Saboda haka, harshenmu na asali tamkar lu’u-lu’u ne da aka gaje su daga magabantanmu. Sai dai wasu daga cikin “lu’u-lu’un” sun riga sun ɓace. Yau na karanta wani labari dake cewa: wata mace mai suna Cristina Calderon ta rasu a kwanakin baya, tana da shekaru 93 a duniya, da rasuwar ta kuma an…
Read More