Kasashen Waje

Shugaban ƙasar Sin ya gabatar da jawabi ga taron tattalin arzikin duniya na St. Petersburg

Shugaban ƙasar Sin ya gabatar da jawabi ga taron tattalin arzikin duniya na St. Petersburg

Daga CMG HAUSA Shugaban ƙasar Sin Xi Jinping, ya halarta tare da gabatar da jawabi ga taron tattalin arzikin duniya karo na 25 da aka yi a St. Petersburg. Xi Jinping, wanda ya halarci taron ta kafar bidiyo bisa gayyatar da aka yi, ya ce duniya na fuskantar muhimman sauye-sauye da annoba da ba a taba gani ba cikin karni, kana dunƙulewar tattalin arzikin duniya ya gamu da tsaiko, baya ga ƙalubalen da ake fuskanta wajen aiwatar da muradun ci gaba masu ɗorewa da MƊD ke son cimma wa zuwa shekarar 2030. Ya ce a lokacin da duniya ke da…
Read More
Shirin bidiyo da ya nuna yadda Sin ta fatattaki talauci ya ƙarfafawa ‘yan Nijeriya gwiwa

Shirin bidiyo da ya nuna yadda Sin ta fatattaki talauci ya ƙarfafawa ‘yan Nijeriya gwiwa

Daga CMG HAUSA Gomman mutane daga dukkan bangarorin rayuwa ne suka samu damar kallon yadda ƙasar Sin ta yi nasarar fatattakar talauci, a lokacin da aka nuna wani shirin bidiyo na documentary, wanda ya gabatar da baki ɗayan aikin yaƙar talaucin a Abuja, babban birnin Nijeriya. Bayan kammala kallon shirin, mutanen sun bayyana cewa, ya ƙarfafa musu gwiwa, inda suka yi kira da a aiwatar da aikin yaƙi da talauci a Nijeriya. Gidan talabijin na ƙasar Sin CGTN tare da haɗin gwiwar gidauniyar Kuhn ta Amurka ne suka gabatar da shirin mai taken “Voices From The Frontline: China's War On…
Read More
Shugaban Zimbabwe ya ƙaddamar da aikin gyara wurin haƙar sinadarin Lithium da kamfanin Sin zai aiwatar

Shugaban Zimbabwe ya ƙaddamar da aikin gyara wurin haƙar sinadarin Lithium da kamfanin Sin zai aiwatar

Daga CMG HAUSA Shugaban ƙasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa ya halarci bikin ƙaddamar da aikin gyara wurin hakar sinadarin Lithium na Bikita, wanda shi ne irinsa mafi girma a ƙasar. Kamfanin Sinomine Resource Group na ƙasar Sin ne ya sayi wurin na Bikita a watan Janairun bana, inda yake shirin zuba jarin dalar Amurka miliyan 200 don gyaran sa, da nufin inganta aikin samar da sinadarin Lithium da ƙara samar da aikin yi a yankin. Shugaba Mnangagwa ya bayyana a gun bikin cewa, gwamnatin ƙasar Zimbabwe na ba da muhimmanci ga kamfanonin Sin da suka zuba jari a ƙasar. Ya ce…
Read More
Ya kamata a sanya binciken kare haƙƙin ɗan Adam a Amurka cikin ajanda

Ya kamata a sanya binciken kare haƙƙin ɗan Adam a Amurka cikin ajanda

Daga CMG HAUSA Yayin gudanar da taron ƙolin kwamitin kare haƙƙin dan Adam na MƊD karo na 50 wanda aka gudanar kwanakin kaɗan da suka gabata a Geneva, ƙasar Cuba ta fidda sanarwa a madadin ƙasashe kusan 70, inda ta nuna adawa da yin shisshigi a harkokin cikin gidan ƙasar Sin ta hanyar fakewa da batun haƙƙin dan adam. Bugu da ƙari, sama da karin ƙasashe 20 ne suka yi jawaban nuna goyon baya ga ƙasar Sin. Kusan ƙasashe 100 ne suka yi jawabai game da ƙasar Sin ta hanyoyi daban-daban, inda hakan ke nuna cewa, al’ummar ƙasa da ƙasa,…
Read More
Sin za ta taimakawa Tanzania bunƙasa ilimin sana’o’in hannu

Sin za ta taimakawa Tanzania bunƙasa ilimin sana’o’in hannu

Daga CMG HAUSA Ƙasashen Sin da Tanzania, sun ƙaddamar da wani shirin hadin gwiwa dake da nufin bunƙasa ilimin sana’o’in hannu, ta hanyar samar da sabon mizani a ɓangaren, a ƙasar ta gabashin Afrika. Shirin kawance kan ilimin sana’o’in hannu tsakanin Sin da Afrika ne ya ɗauki nauyin sabon shirin na nazari da inganta mizanin ƙwarewar aiki da aka ƙaddamar a ranar Laraba, inda zai gudana ƙarƙashin kulawar majalisar kula da ilimin fasahohi da sana’o’in hannu ta ƙasar Tanzania (NACVET). A cewar Jiang Yilin, sakatare janar na shirin kawancen Sin da Afrika, jimilar kwalejojin koyar da sana’o’in hannu 43 na…
Read More
A bana ne Sin ta samu sakamako mai kyau wajen sa ƙaimi ga yin haɗin gwiwa a tsakanin ƙasashen BRICS

A bana ne Sin ta samu sakamako mai kyau wajen sa ƙaimi ga yin haɗin gwiwa a tsakanin ƙasashen BRICS

Daga CMG HAUSA Kakakin ma’aikatar harkokin wajen ƙasar Sin Wang Wenbin ya bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar a yau cewa, shekarar bana shekara ce da Sin ta samu sakamako mai kyau wajen sa kaimi ga yin haɗin gwiwa a tsakanin ƙasashen BRICS. Bisa goyon bayan ɓangarori daban daban, ƙasar Sin ta gudanar da taruka da bukukuwa fiye da 70 cikin nasara a matsayin ƙasar dake shugabancin BRICS a wannan karo, matakin da ya taimaka wajen yin haɗin gwiwa a tsakanin ƙasashen BRICS a fannoni daban daban. Wang Wenbin ya bayyana cewa, an samu sakamako mai kyau…
Read More
Sabon layin dogo da ya zagaye hamada mafi girma a ƙasar Sin ya fara aiki

Sabon layin dogo da ya zagaye hamada mafi girma a ƙasar Sin ya fara aiki

Daga CMG HAUSA Alhamis din nan ne, aka fara aiki da sashin ƙarshe na layin dogo mai tsawon kilomita 2,712, wanda ya zagaye hamada mafi girma a ƙasar Sin, wato Taklamakan, dake yankin artewa maso yammacin jihar Xinjiang ta Uygur mai cin gashin kanta, bayan da aka shafe shekaru 3 da rabi ana ƙoƙarin ginawa. Sabon sashin layin dogon mai nisan kilomita 825, ya tashi ne daga gabas da birnin Hotan zuwa gundumar Ruoqiang, kusa da gefen kudu da Taklamakan, hamada ta biyu mafi girma a duniya mai cike da yashi, inda kusan kashi 65 na layin dogo yake gudana…
Read More
Saƙon Xi ya ƙarfafa gwiwar matasan Afrika wajen raya hulɗar Sin da Afrika

Saƙon Xi ya ƙarfafa gwiwar matasan Afrika wajen raya hulɗar Sin da Afrika

Daga CMG HAUSA Aikewa da sakon da Xi Jinping, babban sakataren kwamitin tsakiyar jamiyyar kwaminis ta ƙasar Sin ya yi cikin lokaci, ga wasiƙar da mahalarta taron ƙarawa juna sani na ƙungiyar ‘yantar da kudancin Afrika na shekarar 2022, ya yi matuƙar ƙara ƙaimi ga matasan Afrika. Nawanda Yahya, jagoran mahalarta taron daga ƙasar Tanzania, ya bayyana cewa, samun sakon amsa daga shugaba Xi cikin ƙasa da mako guda, wani kwarin gwiwa ne ga bangarorin matasan Afrika, da shugabannin da suka halarci taron na makonni biyu, a makarantar nazarin mulki ta Mwalimu Julius Nyerere, dake gundumar Kibaha a gabar tekun…
Read More
Ya kamata ‘yan siyasar Birtaniya su riƙa yin abu gwargwadon ƙarfinsu

Ya kamata ‘yan siyasar Birtaniya su riƙa yin abu gwargwadon ƙarfinsu

Daga CMG HAUSA Jiya Laraba hukumar gudanarwar ƙungiyar tarayyar Turai wato EU ta kai ƙarar gwamnatin Birtaniya saboda rashin mutunta wasu tanade-tanaden da ke cikin yarjejeniyar Arewacin Ireland. Madam Michelle O’Neil, mataimakiyar shugaban jam’iyyar Sinn Féin ta Arewacin Ireland, jam’iyyar da ke goyon bayan rabuwar Arewacin Ireland daga Birtaniya, ta nuna cewa, abun da gwamnatin Birtaniya ta yi ya ƙara tada ƙura a yanayin siyasar yankin Arewacin Ireland. Kwanaki 2 kafin wannan kuma, madam Nicola Sturgeon, babbar jami’in mahukuntan Scotland ta sanar da cewa, ko gwamnatin Birtaniya ta yarda ko a’a, za ta ƙara azama kan jefa ƙuri’a kan ficewar…
Read More
Yaushe Amurka za ta cika alƙawarin da ta yiwa ƙasar Sin?

Yaushe Amurka za ta cika alƙawarin da ta yiwa ƙasar Sin?

Daga CMG HAUSA Mamban hukumar siyasar kwamitin ƙolin JKS kuma darektan ofishin hukumar kula da harkokin waje ta kwamitin Yang Jiechi ya gana da mai taimakawa shugaban ƙasar Amurka kan tsaron ƙasa Jake Sullivan a Luxembourg a Litinin da ta gabata har na tsawon awoyi huɗu, inda suka yi tattaunawa mai zurfi, tare kuma da amincewa da tabbatar da matsaya guda da shugabannin ƙasashen biyu wato Sin da Amurka suka cimma. Yanzu hulɗar dake tsakanin sassan biyu ta gamu da matsala, sakamakon ƙasa tabbatar da matsayar da shugabannin ƙasashen biyu suka cimma, duk da cewa, ƙasar Sin ta nuna sahihanci…
Read More