Kasashen Waje

Ya kamata Sin da Amurka su samar da kyakkawan yanayin yin haɗin gwiwa tsakaninsu ta fuskar tattalin arziki da ciniki

Ya kamata Sin da Amurka su samar da kyakkawan yanayin yin haɗin gwiwa tsakaninsu ta fuskar tattalin arziki da ciniki

Daga CMG HAUSA Kakakin ma’aikatar kasuwancin ƙasar Sin Gao Feng, ya bayyana a yau Alhamis cewa, har kullum ƙasar Sin na adawa da sanya takunkumi don ƙashin kai, da ɗaukar matakai kan wasu ƙasashe bisa dokokin ƙasar Amurka, kuma kamata ya yi Sin da Amurka su ɗauki matakai bisa buri iri ɗaya, a ƙoƙarin samar da kyakkyawan yanayi, da sharuɗɗan na yin haɗin gwiwa a tsakaninsu ta fuskar tattalin arziki da cinikayya. Dangane da ra’ayin wasu jami’an Amurka, kan sanya takunkumi ga kayayyakin da kamfanonin ƙasar Sin suke sayarwa Amurka, Gao Feng ya nuna cewa, ƙasar Sin ba za ta…
Read More
Yadda aka maida fari ya zama baƙi

Yadda aka maida fari ya zama baƙi

Daga LUBABATU LEI Bullar cutar ƙyandar biri a kwanan nan a wasu kasashen Turai da Amurka ta yi matukar jawo hankalin jama‘a. Sai dai wasu kafofin yaɗa labarai na ƙasashen yamma sun sha yin amfani da hotunan 'yan Afirka da suka harbu da cutar a lokacin da suke ba da rahoton ɓullar cutar, duk da cewa hukumar lafiya ta duniya WHO ta sha jaddada cewa, akasarin waɗanda suka harbu da cutar a ƙasashen Turai da Amurka ba su taba zuwa Afirka ba. A game da wannan, ƙungiyar ‘yan jaridar waje a Afirka (FPPA) ta fitar da sanarwa, inda ta bayyana…
Read More
Yadda haɗin gwiwar Sin da Afirka ke ƙara cigaban ƙasashen Afirka

Yadda haɗin gwiwar Sin da Afirka ke ƙara cigaban ƙasashen Afirka

Daga IBRAHIM YAYA Layin dogo yana daya daga cikin muhimman ababen more rayuwa da ƙasashen nahiyar Afirka suka amfana da shi, ƙarƙashin haɗin gwiwar Sin da ƙasashen na Afirka, baya ga hanyoyin mota, da gadoji na zamani, da makarantu da cibiyoyin lafiya da makamantansu. Tun bayan ƙaddamar da layin dogo na zamani na SDR a ranar 31 ga watan Mayun shekarar 2017 tsakanin Mombasa zuwa Nairobo, da ƙasar Sin ta gina, shekaru biyar da suka gabata, yanzu haka ƙasar Kenya ta shiga wani sabon tsari na rayuwa, inda ya sauya harkokin sufuri, da kasuwanci da nishaɗi a ƙasar Kenya. Bayanai na…
Read More
Sin ta buƙaci haɗin gwiwar ɓangarori daban-daban don hana yaduwar makaman nukiliya

Sin ta buƙaci haɗin gwiwar ɓangarori daban-daban don hana yaduwar makaman nukiliya

Daga CMG HAUSA Zaunannen wakilin ƙasar Sin a MƊD Zhang Jun ya ce, hana yaduwar makaman nukiliya wani babban ƙalubale ne na kasa da ƙasa. Domin daidaita wannan batu, akwai buƙatar a tabbatar da haƙiƙanin haɗin gwiwar ɓangarori daban-daban, kuma jagorancin MƊD na da matuƙar muhimmanci game da wannan batu. Zhang Jun ya bayyana hakan ne a yayin buɗe taron tuntubar juna game da yin cikakken nazari domin aiwatar da ƙudurin kwamitin sulhun MƊD mai lamba 1540, da farko wannan ƙuduri ya dora alhakin wajabtawa dukkan ƙasashe mambobin kwamitin sulhun MƊD, da su yi kokarin dauka tare kuma da aiwatar…
Read More
‘Yancin mallakar makamai barazara ce ga yara a Amurka

‘Yancin mallakar makamai barazara ce ga yara a Amurka

Daga AMINA XU Abokai, yau na zana wani Cartoon dangane da harbe-harben bindiga da suka yi ta faruwa a ƙasar Amurka, kuma da hakan ina nuna alhini ga yaran da suka rasu sakamakon harbe harben bindiga da suku rutsa da su a Amurka, musamman ma yara 19 da suka rasa rayukansu kwanan baya a jihar Texas na ƙasar. ‘Yancin mallakar makamai na samar da sauki ga masu aikata laifuka a ƙasar, matsalar da ta addabi yaran ƙasar sosai. Bai kamata irin wannan matsala ta bullo a cikin wata ƙasa dake iƙirarin kare hakkin Bil Adama da martaba dimokuraɗiyya ba. Dole…
Read More
Masanan ƙasar Sin na cigaba da gabatar da abubuwa na ban mamaki ga duniya

Masanan ƙasar Sin na cigaba da gabatar da abubuwa na ban mamaki ga duniya

Daga FAEZA MUSTAPHA A karon farko, ƙasar Sin ta ƙaddamar da wata sabuwar tashar samar da lantarki daga hasken rana da ƙarfin igiyar ruwa, wadda ke da ƙarfin samar da lantarkin da ya zarce kilowatt miliyan 100 cikin shekara guda. Haƙiƙa wannan wani ƙarin nasara ce ga ƙasar Sin a ƙoƙarin da take ci gaba da yi na rage fitar da hayaƙi mai gurɓata muhalli. Haka kuma nasara ce ga duniya domin ta gabatar musu wani abun misali da koyi a ɓangaren amfani da makamashi mai tsafta domin raya muhalli da biyan buƙatun al’umma. Abun da ya burge ni cikin…
Read More
Shanghai zai dawo da sufurin zirga-zirgar jama’a daga ranar 1 ga Yuni

Shanghai zai dawo da sufurin zirga-zirgar jama’a daga ranar 1 ga Yuni

Daga CMG HAUSA Ofishin kandagarki da hana yaɗuwar COVID-19 na birnin Shanghai, ya faɗa a ranar Litinin cewa, daga ranar 1 ga wwatan Yuni, birnin zai buɗe hanyoyin shiga unguwannin jama'a, da ayyukan sufurin jama'a da zirga-zirgar ababen hawa, a yayin da birnin ke murmurewa daga ɓarkewar COVID-19 da ta fara a watan Maris. Bugu da ƙari, birnin ya ƙaddamar da matakan tallafawa tattalin arziki a ranar Lahadi, ciki har da rage wasu haraji kan motocin da za a saya. Mai Fassarawa: Ibrahim Yaya
Read More
Tattalin arzikin Sin 2022: Akwai yiwuwar tattalin arzikin Sin ya bunƙasa fiye da yadda ake hasashe

Tattalin arzikin Sin 2022: Akwai yiwuwar tattalin arzikin Sin ya bunƙasa fiye da yadda ake hasashe

Daga AHMAD FAGAM Masu azancin magana na cewa, “Juma’ar da za ta yi kyau, tun daga Laraba ake ganewa.” Da alama za mu iya cewa hasashen da masana suka yi game da yiwuwar samun tagomashin bunƙasar tattalin arzikin kasar Sin ya fara tabbata, domin kuwa, a kwanakin baya bayan nan da suka gabata. Dukkanin larduna da birane 31 na ƙasar Sin sun fitar da ma’aunin ci gaban tattalin arzikinsu na GDP a rubu’in farko na bana, inda alƙaluma suka nuna cewa, sassa daban daban na kasar sun samu ci gaba mai inganci yadda ya kamata, duk da cewa ana fama…
Read More
Sin ta yi alƙawarin raba sakamakon cigaban da ta samu tare da ƙasashen Tsibirin Pacific

Sin ta yi alƙawarin raba sakamakon cigaban da ta samu tare da ƙasashen Tsibirin Pacific

Daga CMG HAUSA Mamban majalisar gudanarwar ƙasar Sin kana ministan harkokin wajen ƙasar Wang Yi ya bayyana a jiya Lahadi cewa, ƙasar Sin za ta ƙara faɗaɗa da zurfafa bude kofa ga ƙasashen waje, kuma tana son raba sakamakon ci gaban da ta samu da ƙasashen tsibirin Pacific. Wang ya bayyana hakan ne a wata ganawa da ya yi da Henry Puna, babban sakataren dandalin tattaunawar tsibiran Pacific, a Suva, babban birnin ƙasar Fiji. Fiji ne zango na huɗu, a rangadin aiki na kwanaki 10 da Wang Yi ke yi, bayan ziyarar da ya kai tsibirin Solomon, da Kiribati da…
Read More
Kar a maimaita kuskuren da aka taɓa yi a baya

Kar a maimaita kuskuren da aka taɓa yi a baya

Daga CMG HAUSA Yau 30 ga watan Mayu, rana ce ta musamman, a shekaru 55 da suka wuce ne, Chukwuemeka Ojukwu, shugaban al’ummar Igbo ta Najeriya ya sanar da ɓallewar yankin kudu maso gabas daga ƙasar Najeriya, don kafa “jamhuriyar Biafra”, lamarin da ya ta da yaƙin basasa a ƙasar. An shafe tsawon shekaru 2 da rabi ana wannan yaƙi, wanda ya haddasa hasarar miliyoyin rayukan mutane. A ƙarshe dai, gwamnatin tarayyar Najeriya ta yi nasarar kare cikakken yankin ƙasar, sai dai kamar yadda shugaban gwamnatin soja na ƙasar na lokacin Yakubu Gowon ya fada, “Ba wanda ya ci nasara…
Read More