Kasashen Waje

Sojojin kiyaye zaman lafiya na ƙasar Sin kusan dubu 50 sun shiga ayyukan kare zaman lafiya na MƊD

Sojojin kiyaye zaman lafiya na ƙasar Sin kusan dubu 50 sun shiga ayyukan kare zaman lafiya na MƊD

Daga CMG HAUSA Ranar 29 ga watan Mayu, ranar ma’aikatan kiyaye zaman lafiya na ƙasa da ƙasa ce karo na 20. Alƙaluman ma’aikatar tsaron ƙasar Sin sun nuna cewa, a cikin shekaru fiye da 30 da suka wuce, sojojin ƙasar Sin kusan dubu 50 sun shiga ayyuka guda 25 na MƊD na kiyaye zaman lafiya baki daya. Ƙasar Sin ta ɗauki hakikanin matakai wajen kiyaye zaman lafiyar duniya, ta zama ƙasa ta farko wadda ta fi tura sojojin wanzar zaman lafiya, cikin ƙasashe 5 da ke da kujerun dindindin cikin kwamitin sulhu na MƊD. Cikin shekaru fiye da 30 da…
Read More
Tsarin ƙasar Sin na bincike da sa ido kan harkokin kuɗi ya bada tabbaci kan bunƙasar ƙasa mai inganci

Tsarin ƙasar Sin na bincike da sa ido kan harkokin kuɗi ya bada tabbaci kan bunƙasar ƙasa mai inganci

Daga CMG HAUSA A cikin shekaru 10 da suka wuce, tsarin bincike da sa ido kan harkokin kuɗi ya taka muhimmiyar rawa cikin tsare-tsaren sa ido na ƙasar Sin, wanda ya ba da tabbaci kan bunƙasar ƙasar Sin mai inganci. An samu sakamako mai kyau a fannin binciken harkokin tattalin arzikin ƙasar cikin shekaru 10 da suka wuce. Aikin binciken harkokin kuɗi ya kara azama kan kyautata tsare-tsare fiye da dubu 70, tare da mika wa hukumomin aiwatar da doka da hukumomin sa ido da ladabtarwa bayanai fiye da dubu 60 dangane da wasu batutuwa. A cikin tsarin ƙasar Sin…
Read More
Jakadan Sin dake Nijeriya ya gana da Janar Gowon

Jakadan Sin dake Nijeriya ya gana da Janar Gowon

Daga CMG HAUSA Jakadan ƙasar Sin a tarayyar Najeriya Cui Jianchun, ya gana da tsohon shugaban gwamnatin sojan ƙasar Yakubu Gowon, wanda ya taba ba da gagarumar gudummowa ga ci gaban huldar diplomasiyyar tsakanin ƙasashen biyu. Jakada Cui ya bayyana cewa, a halin yanzu, hulɗar dake tsakanin Sin da Najeriya tana gudana yadda ya kamata ƙarƙashin ƙoƙarin da gwamnatoci da al’ummomin sassan biyu suke yi, kana ƙasashen biyu suna goyon bayan juna a fannin siyasa, kuma suna taimakawa juna wajen ci gaban tattalin arziki da cinikayya. Ya ce a nan gaba, ƙasar Sin tana son hada hannu da Najeriya domin…
Read More
Rundunar sojin Sin ta kira taro kan yanayin tsaroa gaɓar tekun Guinea

Rundunar sojin Sin ta kira taro kan yanayin tsaroa gaɓar tekun Guinea

Daga CMG HAUSA Shugaban sashen watsa labarai na ma’aikatar tsaron ƙasar Sin kuma kakakin ma’aikatar Wu Qian, ya ce rundunar sojin ƙasar Sin ta kira taron ƙara wa juna sani ta kafar bidiyo, kan yanayin tsaron gaɓar tekun Guinea, domin tabbatar da shawarar tsaron duniya da tunanin kafa kyakkyawar makoma a kan teku, da shugaban ƙasar Sin Xi Jinping ya gabatar. Tare kuma da ƙara ƙarfafa haɗin gwiwar dake tsakanin rundunar sojin Sin da na ƙasashen dake gaɓar tekun Guinea, kan tabbatar da tsaro a kan teku. Taken taron shi ne, “tabbatar da tsaro a gabar tekun Guinea, ta hanyar…
Read More
Sabuwar manufar Amurka kan Sin ba ta canja tunaninta na yakin cacar baka da fin ƙarfi ba

Sabuwar manufar Amurka kan Sin ba ta canja tunaninta na yakin cacar baka da fin ƙarfi ba

Daga CMG HAUSA Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken, ya gabatar da wani jawabi game da manufar ƙasarsa kan ƙasar Sin a jami’ar George Washington a ranar 26 ga wata, inda ya bayyana cewa, Amurka tana aiwatar da manufar “zuba jari da hada kai da yin takara” kan ƙasar Sin, amma kafin hakan, ya taba bayyana cewa, manufar ita ce: “takara da haɗin gwiwa da nuna ƙiyayya”. Duk da cewa, akwai bambanci kaɗan tsakaninsu, ainihin yanayin da Amurka ke ciki shi ne, ta gamu da cikas yayin da take matsawa ƙasar Sin lamba. Amurka ba ta sauya tunaninta na yakin…
Read More
Sin ba ta da buƙatar adana abinci daga kasuwar ƙasa da ƙasa

Sin ba ta da buƙatar adana abinci daga kasuwar ƙasa da ƙasa

Daga CMG HAUSA Game da kalaman da wasu ƙasashen yamma suka yi wai ƙasar Sin tana adana abinci daga kasuwar ƙasa da ƙasa, kakakin ma’aikatar harkokin wajen ƙasar Wang Wenbin ya bayyana a yayin taron ganawa da manema labarai cewa, ƙasar Sin tana da sharaɗi da ƙarfi da kuma imani wajen samar da isasshen abinci ga al’ummun ƙasarta, kuma babu buƙatar ta adana hatsi daga kasuwar ƙasa da ƙasa. Wang Wenbin ya ƙara da cewa, tun bayan ɓarkewar annobar cutar COVID-19, ƙasar Sin ta samar wa wasu ƙasashe tallafin abinci cikin gaggawa bisa shawarar MƊD da sauran ƙungiyoyin kasa da…
Read More
Sin Na fatan qarin qasashe za su shiga BRICS

Sin Na fatan qarin qasashe za su shiga BRICS

Daga CMG HAUSA Yau Juma’a kakakin ma’aikatar harkokin wajen ƙasar Sin Wang Wenbin ya yi tsokaci yayin taron ganawa da manema labaran da aka shirya cewa, a matsayinta na ƙasar dake shugabancin BRICS a bana, ƙasar Sin tana goyon bayan ƙasashen ƙungiyar, da su ƙara haɓaka mambobinsu, tare kuma da ƙarfafa haɗin gwiwar dake tsakaninsu da sauran ƙasashen duniya, tana kuma fatan ƙarin ƙasashe waɗanda ke da muradu iri ɗaya za su shiga kungiyar ta BRICS. A farkon bana, wasu ƙasashe kamar Argentina sun nuna fatansu na shiga BRICS, Wang Wenbin ya bayyana cewa, ƙungiyar BRICS, muhimmin tsarin gudanar da…
Read More
Ƙasar Sin ta ce Blinken ya yaɗa bayanan ƙarya a cikin jawabinsa

Ƙasar Sin ta ce Blinken ya yaɗa bayanan ƙarya a cikin jawabinsa

Daga CMG HAUSA Ma'aikatar harkokin wajen ƙasar Sin ta fada Juma'ar nan cewa, jawabin da sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya yi kan manufofin ƙasar Sin, ya yada labaran karya a cikinsa, ya kuma azuzuta wai "barazanar ƙasar Sin", da tsoma baki a harkokin cikin gidan ƙasar Sin da kuma bata sunan manufofin cikin gida da waje na ƙasar Sin. Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin, ya shaidawa taron manema labarai cewa, ƙasar Sin ta nuna rashin amincewarta da ma adawa da kakkausar murya kan wannan jawabi. Wang ya ƙara da cewa, sakatare Blinken…
Read More
Ƙasashen Yamma na “fakewa da guzuma domin harbin karsana”

Ƙasashen Yamma na “fakewa da guzuma domin harbin karsana”

Daga SAMINU HASSAN Sau da yawa wasu ƙasashen yammacin duniya, suna danganta ci gaban da suka samu da biyayyar su ga tsarin dimokaraɗiyya, da salon mulki mai alaƙa da hakan. Ga misali, ƙasashen Amurka da Birtaniya, da ƙasashen tarayyar Turai, na yayata cewa dimokaraɗiyya ce ta haifarwa al’ummunsu da daidaito wajen samun damammakin kyautata rayuwa da 'yanci, kuma hakan ne ya ba su damar bunƙasa tattalin arzikin su yadda ya kamata. Don haka ne suke tsananin fatan yayata salon jagorancin su zuwa sauran sassan duniya. To sai dai kuma, masu sharhi kan al’amuran siyasar duniya da dama, na ganin cewa,…
Read More
Li Keqiang ya jaddada buƙatar aiwatar da manufofin daidaita tattalin arzikin ƙasar Sin

Li Keqiang ya jaddada buƙatar aiwatar da manufofin daidaita tattalin arzikin ƙasar Sin

Daga CMG HAUSA Firaministan ƙasar Sin Li Keqiang, ya jaddada buƙatar aiwatar da manufofin ƙasa, na daidaita ci gaban tattalin arziki, da tallafawa sassan kasuwanni, da bunƙasa samar da ayyukan yi, da inganta rayuwar alumma. Li, wanda kuma mamba ne a ofishin siyasa na kwamitin ƙolin JKS, ya yi wannan tsokaci ne a jiya Laraba, yayin taron majalissar gudanarwar ƙasar Sin da ya gudana ta kafar bidiyo. Yana mai jan hankali da a ƙara azama wajen ingiza harkokin tattalin arziki bakin gwargwado. Firaministan ya ƙara da cewa, ana aiwatar da matakai daban daban domin shawo kan wahalhalu, da ƙalubaloli da…
Read More