Labarai

Siyasar Shekarau da Ganduje da Abba ta zo ƙarshe a Kano – Kwankwaso

Siyasar Shekarau da Ganduje da Abba ta zo ƙarshe a Kano – Kwankwaso

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Mataimakin ɗan takarar jam’iyyar NDC a zaɓen 2027, Sanata Rabiu Kwankwaso, ya bayyana cewa tsofaffin gwamnonin Kano, Ibrahim Shekarau da Abdullahi Ganduje, da kuma Gwamna Abba Kabir Yusuf, sun rasa karfin siyasa a jihar. Kwankwaso ya bayyana haka ne a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Nijeriya (NAN) a Abuja, inda ya ce siyasar da aka gina bisa “cin amana” ba ta daɗewa. Ya ce rikicinsa da Ganduje ya fara ne lokacin da tsohon gwamnan ya fara ƙalubalantar tsarin siyasar da suka gina tare, yana mai cewa hakan ya janyo koma bayan siyasarsa.…
Read More
Bayan kayar da APC, goyon bayan Adeleke ga Tinubu ya raba kan magoya bayansa

Bayan kayar da APC, goyon bayan Adeleke ga Tinubu ya raba kan magoya bayansa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Sa’o’i kaɗan bayan tabbatar da nasarar samun wa’adin mulki na biyu a matsayin Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke ya sake jaddada goyon bayansa ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu a ƙoƙarinsa na neman wa’adin mulki na biyu a zaɓen shugaban ƙasa na 2027. Adeleke, wanda ya kayar da ɗan takarar jam’iyyar APC, Bola Oyebamiji, a zaɓen gwamnan Osun da aka gudanar ranar 15 ga Agusta, 2026, ya bayyana hakan ne jim kaɗan bayan Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta ƙasa (INEC) ta ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaɓen. Yayin da yake gode wa…
Read More
Nijeriya na shirin zama cibiyar noma a Yammacin Afirka — AFAN

Nijeriya na shirin zama cibiyar noma a Yammacin Afirka — AFAN

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Shugaban ƙungiyar Manoma ta Nijeriya (AFAN), Dakta Farouk Rabiu Mudi, ya sake jaddada cikakken goyon bayan ƙungiyar ga Ajandar Sabonta Fata ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu, musamman ƙoƙarin Gwamnatin Tarayya na sauya fasalin harkar noma da tabbatar da wadatar abinci a ƙasar. Mudi ya bayyana hakan ne a wani taron manema labarai, inda ya ce AFAN, a matsayinta na babbar ƙungiyar da ke haɗa manoma, ƙungiyoyin kayan amfanin gona, ƙungiyoyin haɗin gwiwar manoma da sauran hukumomi masu alaƙa da noma, ta ƙuduri aniyar yin aiki tare da gwamnatin yanzu domin magance matsalar ƙarancin abinci tare da…
Read More
Ilimi ba ya cika sai da tarbiyya — Shugaban Makarantar Guidway

Ilimi ba ya cika sai da tarbiyya — Shugaban Makarantar Guidway

Daga WAKILINMU Shugaban Matarantar Guidway Islamic Science Academy, da ke Layin Awe Road, Kinkinau a Jihar Kaduna, Malam Muhammad Surajo Inace, ya yi kira ga iyaye da su ƙara mayar da hankali kan tarbiyya da karatun ’ya’yansu. Malam Surajo ya ce, duk wanda Allah Ya azurta shi da ’ya’ya, ya samu babbar ni’ima da alheri, don haka ya kamata iyaye su kasance masu kulawa da tarbiyya da kuma ilimin ’ya’yansu. Ya ja hankalin iyaye da kada su ɗora wa malamai alhakin tarbiyyar ’ya’yansu su kaɗai, domin iyaye ma suna da muhimmiyar rawa wajen tabbatar da ɗa ya tashi cikin tarbiyya…
Read More
Makarantar Nuru Raudatur Nabiyyu ta gudanar da saukar Alƙur’ani ta farko ga ɗalibai 40

Makarantar Nuru Raudatur Nabiyyu ta gudanar da saukar Alƙur’ani ta farko ga ɗalibai 40

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu kan Yaɗa Labarai, Malam Abdul’azeez Abdul’azeez, ya yaba da ƙoƙarin masu gudanar da Madarasatur Nuru Raudatur Nabiyyu Litahfizul ƙur’ani Wal-Darasatul Islamiyya, da ke Fagge, Kano, bisa irin gudubmawar da suke bayarwa wajen samar da ilimin addini da na Alƙur’ani ga yara da matasa. Malam Abdul’azeez ya bayyana hakan ne a yayin bikin saukar Alƙur’ani ta farko da kuma taron karrama wasu fitattun mutane da suka taka rawa wajen tallafa wa ilimi da ci gaban makarantar, wanda aka gudanar ranar Asabar. Ya ce irin waɗannan makarantu…
Read More
MPM ta taya Yarima, Matawalle, da Lawal murna kan naɗa su cikin tawagar kamfen na Tinubu

MPM ta taya Yarima, Matawalle, da Lawal murna kan naɗa su cikin tawagar kamfen na Tinubu

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Ƙungiyar siyasa ta Matawalle, mai take Matawalle Political Movement MPM a Zamfara ta taya fitattun 'ya'yan jihar Zamfara guda biyar murna kan shigar da su cikin Majalisar kamfen ɗin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na 2027. A cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labarai na ƙungiya, Yusuf Idris Gusau, ya sanya wa hannu a yau Asabar a Gusau, ƙungiya ta ce naɗin ya ƙara sanya Zamfara a kan matsayi mai kyau a siyasar ƙasa. Kungiyar ta bayyana naɗin a matsayin wani muhimmin abin girmamawa ga gudummawar da jihar ta bayar ga APC. A cewar sanarwar, Shugaba…
Read More

Wike zai wallafa ayyukan da ya gada daga gwamnatocin baya

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ministan Abuja Nyesom Wike, ya sanar da shirinsa na wallafa bayanan ayyukan da ya gada daga gwamnatocin da aka yi a baya da kuma na ayyukan da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta bai wa gwamnatinsa. Wike ya bayyana haka ne a ranar Asabar bayan kai ziyarar sanya ido a wasu titina biyu a Abuja, inda ya bayyana gamsuwarsa a kai da kuma ƙwarin aikin da 'yan kwangilar suke yi. Ya ce, takardun bayanan za su ƙunshi ayyukan da gwamnatinsu ta gada daga na tsofaffin shugabannin ƙasa da suka haɗa da, Olusegun Obasanjo, Umaru Musa…
Read More

Abin da ya sa ba zan zama daraktan yaƙin neman zaɓen APC ba – Wike

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ministan Abuja Nyesom Wike, ya bayyana dalilin da ya sa ba zai karɓi muƙamin Darakta-Janar na kwamitin yaƙin neman zaɓen jam'iyyar APC ba domin zaɓen 2027 duk da goyon bayansa ga Shugaba Tinubu. Wike ya bayyana haka ne a ranar Asabar bayan wata ziyarar sanya ido da ya kai a wuraren wasu ayyukan titi guda biyu a Abuja, inda ya bayyana gamsuwa da salo da ƙwarin aikin 'yan kwangilar. Ya ce, matakin nasa na da alaƙa da darussa da ya samu daga zaɓukan baya, inda ya ce da dama daga cikin waɗanda suka riƙe…
Read More

Matafiya sun shiga mawuyacin hali yayin da manyan motoci da aikin titi suka haifar da cinkoso a hanyar Kaduna zuwa Abuja

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja A safiyar ranar Asabar ne matafiya akan hanyar Abuja zuwa Kaduna suka haɗu da tsaiko a sakamakon wani cinkoson ababen hawa a yankin Kateri, lamarin da ya jefa su cikin halin rashin tabbas game da makomar zirga-zirgarsu. Wakilin Blueprint.ng da ke wajen ya ruwaito cewa, cinkoson ya shafi masu zirga-zirga na ɓangarorin titin guda biyu, inda aka ga wani dogon layi na jerin gwanon motoci a yankunan babbar hanyar. Ya bayyana cewa, halin ya fi zama matsi ga masu zuwa Jere da Abuja inda haɗakar aikin gina titi da yawaitar manyan motoci suka haifar…
Read More
Dakta Elayo ta raba tallafin buhunan shinkafa 600 ga mabuƙata a Keana

Dakta Elayo ta raba tallafin buhunan shinkafa 600 ga mabuƙata a Keana

Daga JOHN D. WADA a Lafiya Gimbiya Dr. Margaret Elayo kwamishiniyar ma’aikatar muhalli da albarkatun ƙasa kuma kwamishiniya mai riƙon kwarya na ma’aikatar harkokin mata da ayyukan jin ƙai a jihar Nasarawa ta raba buhunan shinkafa 600 a faɗin mazaɓu 10 na ƙaramar hukumar Keana a jihar Nasarawa. Wannan tallafi ya kuma haɗa da rabon kuɗi domin ƙara wa tallafin abinci karfi. Wannan ya nuna jajircewar Dakta Elayo a matsayinta na mai fafutukar jin ƙai dake ƙoƙarin magance buƙatun al’ummar da ba su da ƙarfi. Yanzu da ake fuskantar wani zaɓe Dr. Elayo tace jam’iyyar All Progressives Congress APC mai…
Read More