Labarai

2027: SERAP ta buƙaci INEC ta bayyana adadin kuɗaɗen da doka ta ƙayyade wa jam’iyyu su kashe yayin yaƙin neman zaɓe

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja. Cibiyar kula da 'yancin zamantakewa da tabbatar da gaskiya da adalci a Nijeriya (SERAP), ta yi kira ga Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Joash Amupitan, da ya yi amfani da ikon da dokar ƙasa ta bayar wajen bayyana ainihin adadin gudunmawar da ta halasta a bayar a harkokin siyasa ƙarƙashin Sashe na 91 na Dokar Zaɓe ta 2026. Haka kuma, SERAP ta roƙi hukumar da ta wallafa ainihin adadin da aka ƙayyade da kuma sanar da su ga jam'iyyun siyasa, 'yan takara, masu taimakawa da kuma al'ummar ƙasa domin tabbatar da biyayya…
Read More
Matasan malaman Zamfara sun yi addu’o’i ga Tinubu da Yari a matsayin shugaban kamfen na 2027

Matasan malaman Zamfara sun yi addu’o’i ga Tinubu da Yari a matsayin shugaban kamfen na 2027

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Reshen Jihar Zamfara na ƙungiyar malamai matasa don wa'azi da faɗakarwa, (Zamfara United of Youth Scholars for Preaching and Guidance) yau Lahadi sun gudanar da zaman addu'o'i na musamman don samun nasarar Shugaba Bola Ahmed Tinubu da nasarar Sanata Abdulaziz Abubakar Yari a matsayin darakta janar na majalisar yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa a shekarar 2027. An gudanar da zaman addu'o'in, a zauren taro na Maryam Multi-Purpose Hall da ke Gusau, babban birnin jihar. Taron ya samu halartar malamai da ɗalibai daga faɗin jihar. Da yake jawabi a wurin taron, shugaban ƙungiyar, Malam Naziru Ibrahim…
Read More

Yaƙin neman zaɓen APC: Ƙungiyar Arewa ta jinjina wa Tinubu kan saka Yerima Shettima

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ƙungiyar Arewa Community APC a jihohin kudanci 17, ta taya Alhaji Kwamared Yerima Shettima kan samun muƙamin Darakta na Hulɗar Ƙwadago na II a kwamitin yaƙin neman zaɓen Jam'iyyar APC a zaɓukan 2027. Da yake magana a Gusau, Jihar Zamfara a ranar Lahadi Frins Alhaji Aliyu Bambado na II, wanda shi ne Galadiman Legas na I kuma mai bayar da shawara ga ƙungiyar Community APC a Legas da jihohin kudu 17, ya bayyana naɗin Shettima a matsayin ajiye ƙwarya a gurbinta duba da yadda yake da ƙwarewa da jajircewa a harkar shugabanci. Ya bayyana…
Read More

‘Ofishin Made in Nigeria halastacce ne’, inji Nwabueze yayin musanta zargin haramcinsa, ya fitar da shaidar bada aiki

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Kodineta na Ƙasa kuma Babban Daraktan 'Ofishin National Brands Development and Made in Nigeria Special Project' da ake taƙaddama a kai, George Nwabueze, ya musanta zargin cewa yana gudanar da "hukumar bogi" a Nijeriya. Nwabueze ya bayyana haka ne ga manema labarai a ranar Asabar, inda ya ce ya jagoranci wani ofishi da ke gudana a ƙarƙashin sanya idon Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya (OSGF). Ya ce, ofishin yana aiki tun sawon shekaru 16 baya. A ranar Juma'a ne Hukumar Yaƙi da Rashawa (ICPC) ta ce Shugaba Bola Tinubu ya umarci a kama Nwabueze bisa…
Read More

Ƙungiyar kansilolin APC ta taya Yari da Ganduje murnar samun shugabanci a kwamitin yaƙin neman zaɓen Tinubu na 2027

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ƙungiyar Kansilolin Jam'iyyar APC ta Ƙasa (NPSCF) ta fitar da saƙonta na taya murnar ga Sanata Abdulaziz Yari Abubakar kuma Gwamnan Jihar Zamfara bisa naɗa shi a matsayin darakta-janar na kwamitin yaƙin neman zaɓen Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaɓen 2027 ƙarƙashin jam'iyyar APC. A wata sanarwa da ke ɗauke da sanya hannun Shugabanta na ƙasa, Hon. Muslihu Yusuf Ali da ya fita a Abuja, ranar Asabar, NPSCF ta kuma taya wanda ta naɗa a matsayin Uban Ƙungiya, tsohon shugaban APC na ƙasa kuma tsohon gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje murna bisa…
Read More
Magidanci ya zuba wa matarsa fetur ya banka mata wuta saboda riga

Magidanci ya zuba wa matarsa fetur ya banka mata wuta saboda riga

Rundunar ’yan sanda a Jihar Kogi ta kama wani mutum mai shekaru 33, Jacob Irewa, bisa zargin banka wa matarsa wuta a lokacin da suka samu saɓani a gidansu. Lamarin ya faru ne ranar Juma’a, 14 ga Agusta, a Oworo Estate da ke Felele, Lokoja, babban birnin jihar Kogi, kamar yadda Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kogi, ASP Afusat Saliu, ta bayyana. A cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Lahadi a Lokoja, Saliu ta ce matar, mai suna Berida Irawo, ta samu raunuka kuma ana duba lafiyarta a Asibitin Honey Gold da ke Felele. Ta ce, jami’an Sashen B…
Read More
Amarya ta saka wa angonta guba a abinci kwana 40 da aurensu

Amarya ta saka wa angonta guba a abinci kwana 40 da aurensu

An kama wata sabuwar amarya mai shekaru 19, Aisha Musa, bisa zargin sanya wa mijinta guba a cikin abincinsa a ƙauyen Gwamna, ƙaramar Hukumar Bauchi ta Jihar Bauchi. An ce lamarin ya faru ne kwanaki 40 kacal da auren ma’auratan. Rahotanni sun ce bayan mijin ya ci abincin ya fara fama da rashin lafiya. An garzaya da shi Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBU) da ke Bauchi, inda yake karɓar magani. Rundunar ’Yan Sandan Jihar Bauchi ta tabbatar da kama matar da ake zargi da hannu a lamarin. Kakakin rundunar, SP Nafiu Habib, ya ce lamarin ya faru…
Read More
Gajerun wasannin kwaikwayo sun fara jan hankalin Hollywood

Gajerun wasannin kwaikwayo sun fara jan hankalin Hollywood

Daga AISHA ASAS  Masana'antar fina-finan Hollywood na fara ƙara karkata zuwa wani sabon salo na shirye-shiryen bidiyo gajeru da ake kallo kai tsaye ta wayar salula, yayin da masu shirya fina-finai ke neman sabbin hanyoyin samun masu kallo a zamanin TikTok. Rahoton Reuters ya bayyana cewa wannan salo, wanda ake kira 'microdramas', ya ƙunshi jerin shirye-shirye masu gajeren lokaci, inda kowane sashe zai iya ɗaukar tsakanin daƙiƙa 45 zuwa mintuna biyu. Asalin wannan salo ya samo asali ne daga Chana, amma yanzu ya samu babbar tagomashi a Amurka. Waɗannan shirye-shiryen suna amfani da labarai masu saurin tafiya, rikice-rikicen soyayya da…
Read More
Jarumar ‘Heroes’ Hayden Panettiere ta rasu tana da shekaru 36

Jarumar ‘Heroes’ Hayden Panettiere ta rasu tana da shekaru 36

Daga AISHA ASAS  Jarumar Hollywood Hayden Panettiere, wadda aka fi sani da rawar da ta taka a shirin Heroes da Nashville, ta rasu tana da shekaru 36. Rahotanni daga kafafen yaɗa labarai na Amurka sun tabbatar da mutuwar jarumar a ranar 16 ga Agusta 2026, kwanaki kaɗan kafin ta cika shekaru 37. Wakilinta ne ya tabbatar da mutuwar, yayin da labarin ya jawo alhini a tsakanin 'yan uwanta da masu sha'awar fina-finanta. Panettiere ta fara fitowa a fina-finai tun tana ƙarama, inda daga baya ta samu gagarumar shahara bayan ta taka rawar Claire Bennet, wata yarinya mai ƙarfin warkar da…
Read More
Funke Akindele ta fitar da jerin jaruman sabon fim ɗinta

Funke Akindele ta fitar da jerin jaruman sabon fim ɗinta

Daga AISHA ASAS  Fitacciyar jarumar Nollywood kuma mai shirya fina-finai, Funke Akindele, ta bayyana jerin fitattun jaruman da za su fito a sabon fim ɗinta mai suna 'The Four: No One Fights Alone'. Fim ɗin, wanda za a fara nuna shi a gidajen sinima a faɗin duniya ranar 11 ga Disamba 2026, ya haɗa manyan sunaye daga Nollywood, ciki har da Funke Akindele, Bisola Aiyeola, Chioma Akpotha, Waje, Richard Mofe-Damijo, Timini Egbuson, Lateef Adedimeji, Ali Nuhu, Uzor Arukwe, Ronke Oshodi-Oke da Wunmi Toriola. Haka kuma fim ɗin zai kunshi fitattun mawaƙa da masu nishaɗi, ciki har da Waje da Shoday,…
Read More