Labarai

Shugaban NASETFUND a Nasarawa ya samu digiri na uku kan jagoranci da harkokin ilimi

Shugaban NASETFUND a Nasarawa ya samu digiri na uku kan jagoranci da harkokin ilimi

Daga JOHN D. WADA a Lafiya Shugaban asusun kula da Ilimi na gwamnatin jihar Nasarawa da ake kira NASETFund a turance Abubakar Adamu Idris ya samu digiri na uku a fannin jagoranci da ilimin harkokin ilimi daga jami’ar Atlantic International University. Wannan ya zo ne bayan ya samu nasarar kare rubutunsa na digiri ɗin ƙarƙashin kulawar manyan malamai da aka san su a faɗin duniya. A cikin wani bidiyo da aka fitar kwanan nan shugaban NASETFund din Abubakar Adamu Idris ya bayyana nasarar a matsayin sakamakon hakuri ta cikin ƙalubalen rayuwa da na karatu da kuma tsarin karatun digiri na…
Read More
Ƙungiyar haɗin kan Agatu don Wadada za ta ƙaddamar da ƙungiyar yaƙin neman zaɓe a Nasarawa

Ƙungiyar haɗin kan Agatu don Wadada za ta ƙaddamar da ƙungiyar yaƙin neman zaɓe a Nasarawa

Daga JOHN D. WADA a Lafiya Ƙungiyar haɗin kan al'ummar ƙabilar Agatu ta jihar Nasarawa don Wadada wato Agatu United For Wadada a turance ta kammala shirye-shiryen ƙaddamar da wata ƙungiyar yaƙin neman zaɓen ta domin goyon bayan ɗan takarar gwamna na jam’iyyar All Progressives Congress APC a babban zaɓen 2027 wato sanata Ahmed Aliyu Wadada. Kodinetan ƙungiyar a jihar kwamaret Godspower Ede ne ya bayyana haka a cikin wata hira ta musamman da ya yi da wakilin mu a Lafiya ranar Litinin na makon da ake ciki. Ede yace taron ƙaddamarwar da aka tsara za a yi a ƙarshen…
Read More
Kallamu ya buƙaci haɗin kan APC gabanin zaɓen cike gurbi a Gombe

Kallamu ya buƙaci haɗin kan APC gabanin zaɓen cike gurbi a Gombe

Daga ABUBAKAR A BOLARI a Gombe Ɗan takarar jam’iyyar APC a zaɓen cike gurbin kujerar Majalisar Wakilai mai wakiltar Gombe/Kwami/Funakaye, Injiniya Dakta Usman Maijama’a Kallamu, ya yi kira ga sauran ’yan takarar da suka fafata da shi, shugabannin jam’iyya da magoya baya da su haɗa kai domin tabbatar da nasarar APC a zaɓen da za a gudanar ranar 19 ga Satumba, 2026. Kallamu ya yi wannan kira ne bayan ya samu tikitin jam’iyyar a zaɓen fidda gwani da aka gudanar a Malam Sidi, hedkwatar ƙaramar hukumar Kwami ta Jihar Gombe. A zaɓen fidda gwannin, Kallamu ya samu ƙuri’u 27, inda…
Read More
‘Yan bindiga sun kashe mutane biyar a Katsina

‘Yan bindiga sun kashe mutane biyar a Katsina

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina 'Yan bindiga sun kashe mutane biyar a ƙaramar hukumar Dutsinma ta Jihar Katsina. A hira da wata kafar sadarwa na JBC ta yi da mazaunin garin Dutsinma, 'yan bindigan sun shiga garin Karofi inda suka kashe wani matashi mai suna zaharaddeen,suka jikkata wasu tare da kwashe Dabbobi. Haka kuma sun shiga ƙauyen Dage Lawal nan ma suka kashe mutane uku ciki har da wani tsohon Kansila da ɗan sa. Mazaunin garin da ya nemi a sakaya sunnan sa, ya bayana cewa mutanen garurruwan sun nemi ɗauki daga jami'an tsaro na karamar hukumar amma saboda rashin…
Read More

2027: Tinubu ya janye jaddawalin kwamitin yaƙin neman zaɓensa

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Shugaba Bola Tinubu ya umarci a janye tare da sake tsara jaddawalin 'yan kwamitin yaƙin neman zaɓensa a ƙarƙashin Jam'iyyar APC domin babban zaɓen 2027. Umarnin ya biyo bayan cece-kuce akan jaddawalin da aka fitar da fari a ranar Asabar. A cewar jaridar TheWill, Tinubu ya ɗauki matakin ne bayan ƙorafi daga wasu jiga-jigan 'ya'yan APC da suka ce jaddawalin bai ƙunshi wasu muhimman masu ruwa da tsaki na jam'iyyar ba kuma bai yi daidai da tsarin shugabanci da rarrabawa da kuma tsarin jam'iyyar ba. Majiyoyi sun bayyana cewa, Tinubu ya umarci Fadar Shugaban…
Read More

Tinubu ya sabunta wa’adin jagororin NAN da NTA

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Shugaba Bola Tinubu ya sabunta wa'adin Malam Ali Muhammed Ali, wato Darakta Manaja na Kamfanin Dillancin Labarai (NAN), na tsawon wasu shekaru uku. Kakakin Shugaban ƙasa Bayo Onanuga ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya fitar a Abuja, ranar Lahadi. Ya ce, shugaban ƙasar ya kuma sabunta na jagorancin Darakta Janar na Gidan Talabijin na Ƙasa (NTA), Malam Abdulhamid Dembos. A cewar Onanuga, shugaban ya naɗa Dembos na NTA da Ali na NAN a ranar 20 ga watan Oktoba, 2023, inda ya ƙara da cewa, zangon nasu na biyu zai fara…
Read More
Shugaban ‘yan wasan gargajiya na Kebbi ya rasu

Shugaban ‘yan wasan gargajiya na Kebbi ya rasu

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Da safiyar ranar Lahadin nan gwamnatin jihar Kebbi ta sanar da rasuwar Alhaji Garba Muhammed Kola da aka fi sani da Kanga. Alhaji Garba Muhammed Kola ya rasu a garin Birnin Kebbi bayan ya yi fama da rashin lafiya.Kafin rasuwar da shi ne shugaban sashen tsare-tsaren wasannin al'adun gargajiya a ma'aikatar yaɗa labarai ta jihar Kebbi. Ya rasu ya bar mata uku da yaya da dama.An kuma yi jana'izar sa a garin Birnin Kebbi kamar yadda shari'ar musulunci ta tanada. Kwamishinan yaɗa labarai Alhaji Ahmed Yakubu Birnin Kebbi da babban Sakatare Alhaji Alkasim Salihu Gunabi…
Read More

Shahararren jarumin Nollywood, Taiwo Hassan Ogogo ya rasu

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Sanannen jarumin Masana'antar Nollywood, Taiwo Hassan, wanda aka fi sani da Ogogo ya rasu. 'Yarsa Kira Taiwo ce ta tabbatar da rasuwarsa a wani faifan bidiyo da aka yi kai-tsaye yayin tattaunawa a shafinta na Instagram. A ranar Litinin, 17 ga Agusta ne 'ya'yan Ogogo biyu, wato Kira Taiwo da Lima Taiwo suka fitar da wani faifan bidiyo, inda suke roƙon jama'a shawarwarin lafiya da agaji ga mahaifin nasu da ya kasance yana fama da cutar daji ta mataki na huɗu. A cewar Kira, likitoci sun ce ba za su yi masa aikin kashe…
Read More

Malaman addini sun goyi bayan sake zaɓen Tinubu a 2027

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Yayin da aka sake kaɗa gangar siyasa a Nijeriya, wata tawagar Malaman Addinin Islama a Jihar Jigawa, ta bayyana goyon bayanta ga sake zaɓar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaɓen 2027 da ke tafe. A wani taro da aka gudanar a Dutse, Babban Birnin Jihar Jigawa, an manyan malamai daga jihohin Arewa goma 19 da adadinsu ya kai kusan 500, inda suka bayyana amincewarsu ga takarar Shugaba Tinubu. Haka kuma, sun amince kan lallai shi za su yi wa yaƙin neman zaɓe kuma za su zaɓe a yayin zaɓukan, waɗanda za a gudanar a…
Read More

Tsohon Gwamnan Adamawa, Bindow ya koma APC bayan ganawa da Tinubu

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Tsohon Gwamnan Jihar Adamawa, Sanata Muhammad Umar Jibrilla Bindow, ya koma Jam'iyyar APC a hukumance gabanin shirye-shiryen babban zaɓen 2027. Hakan na zuwa ne bayan shawarwari da abokan hulɗar siyasa da kuma tattaunawa da Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima. Bindow ya sake rajistar zama mamban jam'iyyar ne a mazaɓarsa da ke Mubi, wato cibiyar kasuwanci ta jihar Adamawa a ranar Lahadi, a gaban Shugaban APC na mazaɓar, Alhaji Ahmadu Guruja. A yayin haka ne aka samu halartar tsofaffin magoya bayansa, abokai, 'yan dangi, abokan harkokin siyasa da masu fatan…
Read More