Labarai

Yanzu-yanzu: APC ta musanta janye jaddawalin kwamitin yaƙin neman zaɓen Tinubu na 2027

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Jam'iyyar APC ta yi watsi da rahotannin da ke cewa ta janye jaddawalin sunayen 'yan kwamitin yaƙin neman zaɓen Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaɓen 2027. Sakataren yaɗa labaran jam'iyyar, Felix Morka, ya bayyana rahotannin da ke yaɗa hakan a matsayin jita-jita, inda ya ce dukkan wani hukuncin da aka yanke kan kwamitin, za a ji shi ne daga bakin jam'iyyar a hukumance. Da yake magana da 'yan jaridar a safiyar yau Talata a Abuja, Morka ya ce APC ba ta janye jaddawalin ba kuma ra rahotannin da ake yaɗawa akan haka ba gaskiya…
Read More

Dawo da tallafin fetur zai maida hannun agogo baya ga nasarorin da Nijeriya ta samu a tattali – Idris

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Al'umma, Mohammed Idris Malagi, ya ƙalubalanci kira akan a dawo da tallafin fetur da aka cire a baya, yana mai gargaɗin koma wa tsarin na da ka iya haifar da cikas ga bunƙasar da aka samu a ɓangaren wadatar kuɗi, karya ƙwarin-gwiwar masu zuba jari da rushe nasarorin da aka samu sakamakon gyare-gyaren fannin tattali a ƙarƙashin gwamnatin Tinubu. Shugaba Bola Tinubu dai ya cire tallafin fetur ne yayin da ya kama aiki a matsayin shugaban Nijeriya a watan Mayun 2023, matakin da ya zama ɗaya daga…
Read More

Gobara ta ƙone ɗaruruwan shaguna a shahararriyar kasuwar Oranyan ta Ibadan

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ɗaruruwan shaguna ne suka ƙone ƙurmus a wata gobara da tsakar dare a ranar Litinin a sananniyar kasuwar Oranyan da ke Ƙaramar Hukumar Ibadan ta Arewa maso Gabas a Jihar Oyo. Rahotanni sun bayyana cewa, gobarar, wadda ta fara ci tun tsakiyar dare, ta shafi shaguna da dama na sassa daban-daban na kasuwar. Sannan, ta shafi ƙananan 'yan kasuwa da suka haɗa da 'yan harkar gwala-gwalai, kafintancin zamani, 'yan gwanjo da wasu kayayyaki. Shaidu sun ce, wutar da fara ci ne tun da tsakar dare, saidai ba su san ainihin lokacin ba. Wasu rahotanni…
Read More
Sojoji sun kama ƙasurgumin ɗan bindiga a Katsina

Sojoji sun kama ƙasurgumin ɗan bindiga a Katsina

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Sojojin 17 Bridge sun sami nasarar kama ƙasurgumin ɗan bindiga Sunusi Mai Gilas a yayin da sojojin suka kai samame a ƙaramar hukumar Kurfi. Mai gilas na ɗaya daga kwamandan 'yan bindigan a dajin Danmusa wanda dama rundunar sojoji ke neman sa bisa zargin aikata ta'addanci da manyan laifuka a yankin na Ɗanmusa. Wannan kame ya nuna nasarar da rundunar sojoji ke samu a ƙoƙarin da suke na tarwatsa sansanonin 'yan bindiga da hana su kai wa da komowa a tsakankanin al'umma. Yanzu jami'an tsaro sun fi mayar da hankali wajen gano wurare da dazuka…
Read More
Milo ya tallafa wa masu sana’ar shayi 2,000 a Kano da Jos

Milo ya tallafa wa masu sana’ar shayi 2,000 a Kano da Jos

Daga RABI'U SANUSI a Kano Kamfanin Nestlé Milo ya tallafa wa masu sana’ar sayar da shayi 2,000 a Kano da Jos ƙarƙashin shirinsa na tallafa wa kwastomomin da suka jima suna hulɗa da shi domin ƙarfafa gwiwar masu ƙananan sana’o’i. Kamfanin ya ce rabon tallafin zai kuma ƙarfafa rawar da Milo ta shafe tsawon shekaru tana takawa a matsayin mahadin shan shayi a Arewacin Najeriya. Shirin ya bai wa masu shayi kayan tallafin da suka haɗa da risho mai amfani da iskar gas, tukunyar gas, malafar kare rana, fitila mai amfani da hasken rana, kofuna da kuma sinadarin Milo. Masu…
Read More
Ƙungiyar wakilan ‘yan jaridu ta ƙaddamar da sabon ofishin ta bayan yi masa kwaskwarima a Kano

Ƙungiyar wakilan ‘yan jaridu ta ƙaddamar da sabon ofishin ta bayan yi masa kwaskwarima a Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Ƙungiyar wakilan gidajen jaridu ta Jihar Kano, wato Correspondents’ Chapel, ta ƙaddamar da sabon ofishinta da aka yi wa cikakken gyara, a wani mataki na inganta yanayin aikin ’yan jarida da ƙara ƙarfafa haɗin kan mambobinta. An gudanar da bikin ƙaddamar da ofishin ne a Sakatariyar Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Najeriya (NUJ) da ke Kano, ranar Lahadi, inda tsohon Kwamishinan Yaɗa Labarai na Jihar Kano kuma tsohon Shugaban NUJ na ƙasa, Muhammad Garba, ya jagoranci taron. Manyan baƙin da suka halarci taron sun yaba wa Shugaban Correspondents’ Chapel na Kano, Murtala Adewale, da kwamitin gudanarwarsa,…
Read More
Yari ginshiƙi ne wajen samun nasarar Tinubu – Sani Shinkafi

Yari ginshiƙi ne wajen samun nasarar Tinubu – Sani Shinkafi

Daga SANUSI MUHAMMAD Gusau Fitaccen jigon APC kuma jagoran siyasa, Dr. Sani Abdullahi Shinkafi, ya ce Sanata Abdulaziz Yari yana da darajar tsarin da ake buƙata don sake zaɓen Shugaba Bola Ahmed Tinubu a 2027. Shinkafi ya yi gargaɗin cewa nasara a Arewa maso Yamma ta dogara ne da ɗaukar mataki mai tsauri kan 'yan ta'adda da kuma inganta samar da walwala ga 'yan ƙasa. Shinkafi ya yi wannan furucin ne a ranar Litinin yayin wani taron masu ruwa da tsaki da membobin ƙungiyar siyasarsa, "Wamban Shinkafi Democratic Front", wanda aka gudanar a gidansa da ke Gusau, Jihar Zamfara. Shinkafi…
Read More
Gwamna Raɗɗa ya ƙaddamar da kayan tallafi ga al’ummar da hare haren ‘yan bindiga ya shafa

Gwamna Raɗɗa ya ƙaddamar da kayan tallafi ga al’ummar da hare haren ‘yan bindiga ya shafa

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Raɗɗa ya ƙaddamar da rabon tallafin abinci, kuɗaɗe da sauran kayan agaji ga al’ummar ƙaramar hukumar Musawa da hare-haren 'yan bindiga ya shafa. Tallafin ya samu ne da haɗin gwiwar da ɗan majalissar tarayya mai wakiltar yankin Hon. Abdullahi Aliyu (Dujiman Katsina), sun haɗa kai domin tallafa wa al’ummar yankin tare da rage musu raɗaɗin halin da suke ciki. An raba buhunan shinkafa 1,500 da buhunan taki 200, yayin da Hon. Abdullahi Aliyu Ahmad (Dujiman Katsina), Ɗan Majalissar Tarayya mai wakiltar yankin, ya bayar da gudunmawar Naira miliyan 30…
Read More
Al’ummar Dayi a Katsina sun yi taron inganta siyasa a garinsu

Al’ummar Dayi a Katsina sun yi taron inganta siyasa a garinsu

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Ƙungiyar cigaban Dayi mazauna Katsina sun yi taron masu ruwa da tsaki don bada gudunmuwa ta ingata rayuwar al'ummarsu ta Dayi da ke karamar hukumar Malumfashi. A jawabin sa , shugaban ƙungiyar, mataimakin shugaban mai hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi na ƙasa mai ritaya Hamza Umar Dayi ya shaidawa mahalarta taron cewa an haɗu don a ingata siyasa ta mutanen garin Dayi. Alhaji Hamza Umar Dayi ya tuno cewa babu wani lokacin da aka samu ɗan siyasa da ya taba wakiltar ƙaramar hukumar Malumfashi a majalisar jiha. Yace yanzu jam'iyyar APC ta tsaida ɗan…
Read More

NiMet ta yi hasashen mamakon ruwan sama a Abuja, Nasarawa, Benuwai da wasu jihohi shida

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Yayin da ake tsaka da lokacin damina, Hukumar Kula da Yanayi ta Ƙasa (NiMet), ta yi hasashen samun hadari da tsawa a yankunan Nijeriya a ranar Litinin, 24 ga Agusta, 2026 tare da matsakaicin ruwan sama a sassa da dama na ƙasar. Blueprint ta ruwaito cewa, hasashen ya ƙunshi shiyyoyin arewaci, arewa ta tsakiya da kudanci ƙasar, inda za a yi tsawa da matsakaicin ruwan sama a jihohi da dama a yinin. A jihohin arewa, NiMet ta ce ana sa ran hadari a safiya, yayin da tsawa za ta biyo baya tare da matsakaicin…
Read More