Labarai

’Yan sandan Abuja sun ƙaryata rahoton sayar da ƙodar matasa a Nyanya

’Yan sandan Abuja sun ƙaryata rahoton sayar da ƙodar matasa a Nyanya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Rundunar ’Yan Sandan Babban Birnin Tarayya (FCT) ta ƙaryata wani rahoto da ke yawo a kafafen sada zumunta, wanda ke iƙirarin cewa matasan da ke zaune a yankin Nyanya sun sayar da ƙodarsu domin samun kuɗi, yayin da wani wakili a Mararaba ke sayen sassan jikin mutane. Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar ’yan sandan FCT, SP Josephine Adeh, ta bayyana a Abuja ranar Laraba cewa rundunar ba ta samu ko tabbatar da wani rahoto makamancin haka ba. Ta ce babu wata sanarwa ko saƙo da ya fito daga rundunar da ke tabbatar da…
Read More
Gwamnatin Kano ta ƙara mafi ƙarancin fansho daga N5,000 zuwa N20,000

Gwamnatin Kano ta ƙara mafi ƙarancin fansho daga N5,000 zuwa N20,000

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnatin Jihar Kano ta ƙara mafi ƙarancin kuɗin fanshon da ake biyan ma’aikatan da suka yi ritaya daga N5,000 zuwa N20,000 a wata. Shugaban ƙungiyar ’Yan Fansho ta Nijeriya (NUP), reshen Jihar Kano, Shuaib Musa-Jibrin, ne ya bayyana hakan a wata hira da Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN) a Kano. Musa-Jibrin ya ce ƙarin kuɗin fanshon ya biyo bayan tattaunawa tsakanin gwamnatin jihar da wakilan ’yan fansho. Ya kuma bayyana cewa gwamnatin Kano ta samu ci gaba wajen biyan basussukan alawus-alawus da sauran hakkokin ’yan fansho. A cewarsa, daga cikin bashin da aka gada…
Read More
Ndume ya buƙaci Tinubu ya kori ‘marasa ƙwarewa’ daga gwamnatinsa

Ndume ya buƙaci Tinubu ya kori ‘marasa ƙwarewa’ daga gwamnatinsa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Sanata mai wakiltar Borno ta Kudu, Ali Ndume, ya bukaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya cire jami’an da ba su da kwarewa daga cikin gwamnatinsa, yana mai cewa kasancewarsu na jawo wa gwamnatin abin kunya. Ndume, wanda tsohon shugaban marasa rinjaye ne a Majalisar Dattawa kuma jigo a jam’iyyar APC, ya bayyana hakan ne a wata hira da gidan talabijin na Arise Tɓ. Ya ce abin da ya kira “kakistrocrats”, wato mutanen da ba su da kwarewa ko cancantar gudanar da mulki, na taka muhimmiyar rawa wajen haifar da rikice-rikice da badakalar da…
Read More
Babban Sakataren NLC, Emmanuel Ugboaja, ya rasu jiya

Babban Sakataren NLC, Emmanuel Ugboaja, ya rasu jiya

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Babban Sakataren ƙungiyar ƙwadago ta Nijeriya (NLC), Kwamred Emmanuel Ugboaja, ya rasu yana da shekaru 60 bayan fama da doguwar jinya. An bayyana rasuwar Ugboaja ne a jiya Alhamis, yayin da Majalisar Zartarwa ta ƙasa ta NLC ke gudanar da taro a Enugu. Rahotanni sun ce, Shugaban NLC, Kwamred Joe Ajaero, ne ya sanar da mambobin majalisar labarin rasuwar bayan iyalan marigayin sun aika da wasiƙar sanarwar rasuwar. Kwamred Ugboaja, wanda ƙwararren lauya ne kuma gogaggen ɗan ƙungiyar ƙwadago, ya zama Babban Sakataren NLC na biyar a watan Agustan 2019, inda ya gaji Peter Ozo-Eson. Ya…
Read More
Asabar za a gabatar da littafin ‘Tambarin Zamani’ na matashiya Salma Mailambu

Asabar za a gabatar da littafin ‘Tambarin Zamani’ na matashiya Salma Mailambu

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano  Ya zuwa yanzu dai shirye-shirye sun yi nisa na babban taron gabatar da littafin waƙoƙi mai suna ‘Tambarin Zamani’, wanda matashiyar mawaƙiya, Salma Saeed Mailambu, ta rubuta. Za a gudanar da taron ne a gobe Asabar 29 ga Agusta a ɗakin taro na gidan Mambayya dake Unguwar Gwammaja a cikin birnin Kano. Ana sa ran zai samu halartar manyan baƙi daga sassa daban-daban na ƙasar nan, musamman malamai da ɗalibai da masu nazarin waƙoƙi da al'adun gargajiyar Hausa. Littafin Tambarin Zamani dai wasu waƙoƙi ne daga cikin fitattun waƙoƙin Salma Saeed Mailambu guda 20 aka…
Read More
Bauchi: Harin ramuwar gayya ya yi sanadin mutuwar mutum ɗaya a Gamawa

Bauchi: Harin ramuwar gayya ya yi sanadin mutuwar mutum ɗaya a Gamawa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Mutum ɗaya ya rasa ransa, yayin da wasu mutane shida suka samu raunuka sakamakon wani rikici tsakanin matasan garuruwan Buskuwa da Mabani da ke ƙaramar Hukumar Gamawa a Jihar Bauchi. Rundunar ’Yan Sandan Jihar Bauchi ta ce ta fara bincike kan lamarin, tare da kama wani mutum da ake zargi da hannu a rikicin. A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, SP Nafiu Habib, ya fitar ranar Alhamis, ya ce ’yan sanda sun samu rahoton lamarin ne ranar Laraba daga wani mazaunin ƙauyen Buskuwa mai shekaru 55. Ya ce rikicin ya samo asali ne…
Read More
Tallafin mai: Atiku na rikitar da ’yan Nijeriya — Fadar Shugaban ƙasa

Tallafin mai: Atiku na rikitar da ’yan Nijeriya — Fadar Shugaban ƙasa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Fadar Shugaban ƙasa ta zargi tsohon Mataimakin Shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, da bayar da bayanai masu karo da juna kan shirinsa na dawo da tallafin man fetur idan aka zaɓe shi a matsayin Shugaban ƙasa a 2027. Aminiya Mai bai wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu shawara kan yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya ce Atiku da mataimakansa sun bayar da bayanai daban-daban kan yadda shirin dawo da tallafin zai kasance cikin mako guda. A cewar Onanuga, mai magana da yawun Atiku, Paul Ibe, ya fara cewa gwamnatin Atiku za ta dawo da tallafin…
Read More
NNPCL ya ƙara farashin fetur zuwa N1,270 duk da rangwamen Dangote na kai kaya kyauta

NNPCL ya ƙara farashin fetur zuwa N1,270 duk da rangwamen Dangote na kai kaya kyauta

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Kamfanin Nigerian National Petroleum Company Limited (NNPCL) ya ƙara farashin litar man fetur (PMS) daga N1,250 zuwa N1,270 a gidajen mai na kamfanin da ke Abuja da kewaye. ƙarin N20 ya zo ne duk da shirin matatar Dangote na raba fetur ba tare da kuɗin jigilar kaya ba zuwa wasu wurare 10 a Nijeriya, ciki har da Abuja, inda ake sayar da litar kan N1,185. Wani binciken kasuwa da aka gudanar a Abuja ya nuna cewa farashin fetur ya bambanta daga gidan mai zuwa wani, inda ake sayar da litar tsakanin N1,230 da N1,299.…
Read More
Katsina: Rashin jituwa ta ɓarke tsakanin Raɗɗa da Masari hadimin Shugaban ƙasa

Katsina: Rashin jituwa ta ɓarke tsakanin Raɗɗa da Masari hadimin Shugaban ƙasa

Daga UMAR GARBA a Katsina Rashin jituwa da ke tsakanin Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umar Radda, da Hadimin Shugaban ƙasa, Ibrahim Masari, ya sa aka gayyaci jami’an tsaron Gwamna Radda zuwa Abuja. Rikicin ya fara ne bayan da wasu matasa suka rushe wani babban allon siyasa da ke ɗauke da hoton Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu. Rahotanni sun bayyana cewa matasa ’yan bangar siyasa sun lalata allon sakamakon an sanya ɗan ƙaramin hoton Gwamna Radda, amma an sanya manya-manyan hotunan Shugaba Tinubu da kuma mai ba shi shawara kan harkokin siyasa, Ibrahim Masari. An yi zargin cewa jami’an tsaron Gwamnan…
Read More
Mauludi: Lokaci ne na jaddada aiki da koyarwar Annabi Muhammad –  Idris

Mauludi: Lokaci ne na jaddada aiki da koyarwar Annabi Muhammad –  Idris

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su yi riƙo da koyarwar Annabi Muhammad (SAW), musamman wajen kyautatawa, zaman lafiya, haƙuri, adalci da haɗin kai. Idris ya bayyana hakan ne a saƙonsa na taya Musulmi murnar zagayowar Maulidin Annabi Muhammad (SAW), inda ya ce bikin wata dama ce ta tunawa da kyawawan halaye da koyarwar Manzon Allah. Ya ce waɗannan halaye suna da muhimmanci musamman a lokacin da Nijeriya ke fuskantar sauye-sauyen tattalin arziki da sauran ƙalubale. Ministan ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya, ƙarƙashin jagorancin…
Read More