Labarai

Yadda gagarumin mauludin Manzon Allah na Zawiyyar Ahlul Faidhati Mai Diwani ya ƙayatar a Kaduna

Yadda gagarumin mauludin Manzon Allah na Zawiyyar Ahlul Faidhati Mai Diwani ya ƙayatar a Kaduna

Daga ZAHARADDEEN ILIYASU a Kaduna Zawiyyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group ta gudanar da gagarumin taron Maulidin Manzon Allah (SAW) na watan Rabi’ul-Awwal na shekarar 1448/2026 a Kaduna, inda aka shafe tsawon dare ana gudanar da ibadu da shirye-shirye daban-daban domin ƙarfafa soyayya ga Manzon Allah (SAW) da kuma koyarwarsa. Taron ya ƙunshi karatun Alƙur’ani, zikiri, rera yabo da salati ga Manzon Allah (SAW), gaisuwar sada zumunci, rabon kyaututtuka da takardun shaidar kammala haddace wasu littattafai, tare da gudanar da addu’o’i na musamman a ƙarshen taron. A yayin taron, babban Shehin Zawiyyar, Shehu Isma’ila Umar Almaddah, ya gabatar da dogon…
Read More
Shugaban ƙaramar hukumar Dala ya yaba wa Malami mai nama kan samar wa matasa ayyukan yi

Shugaban ƙaramar hukumar Dala ya yaba wa Malami mai nama kan samar wa matasa ayyukan yi

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Shugaban ƙaramar Hukumar Dala, Hon. Surajo Imam, ya yaba da ƙoƙarin fitaccen ɗan kasuwar gasashen naman rago, Alhaji Malami Mai Nama, wajen samar wa matasa ayyukan yi da kuma bunƙasa harkar kasuwanci a Jihar Kano. Surajo Imam ya bayyana hakan ne a wajen buɗe wani sabon katafaren wajen sayar da gasashen naman rago na Alhaji Malami Mai Nama, da ke kan Titin Ibrahim Taiwo a Kano, ranar Laraba. Ya ce kasuwanci na ci gaba da bunƙasa a Jihar Kano, yana mai cewa Alhaji Malami ya fara sana’ar ne da tallan nama a kwano, kafin daga…
Read More
2027: Yadda Bello Dalhatu ya fito da sabon tsarin ceton al’ummar Kano

2027: Yadda Bello Dalhatu ya fito da sabon tsarin ceton al’ummar Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Dan takarar gwamnan Jihar Kano a ƙarƙashin jam’iyyar PDP a zaɓen 2027, Amb. Muhammad Bello Dalhatu, ya bayyana ƙudirinsa na sake fasalta tafiyar jihar, tare da mai da hankali kan bunƙasa tattalin arziki, samar da ababen more rayuwa da inganta rayuwar al’umma. Amb. Dalhatu ya ce lokaci ya yi da za a kawo sauyi a Kano, yana mai cewa jihar na buƙatar shugabanci mai hangen nesa, ƙwarewa da kishin jama’a domin amfani da dimbin damar da Allah Ya hore mata. Ya ce yana da burin samar da tsarin shugabanci da zai tunkari matsalolin da suka…
Read More
Matatar Dangote ta ƙara farashin fetur duk da faɗuwar farashin ɗanyen mai

Matatar Dangote ta ƙara farashin fetur duk da faɗuwar farashin ɗanyen mai

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Duk da raguwar farashin ɗanyen mai a kasuwannin duniya, Matatar Man Fetur ta Dangote ta ƙara farashin fetur, lamarin da ake sa ran zai sa farashin man ya koma kusan Naira 1,250 kan kowace lita. Matatar Man Fetur da Sinadarai ta Dangote (FZE) ta ƙara farashin sayar da man fetur daga Naira 1,185 zuwa Naira 1,200 kan kowace lita. Sabon farashin ya fara aiki ne daga ranar 26 ga Agusta, 2026. Rahotanni sun ce matatar ta sanar da abokan cinikinta da wannan sauyi ne ta wata sanarwa da sashen Ayyukan Kasuwanci na Rukunin Kamfanin ya fitar…
Read More

Garkuwar Borgu: Har yanzu ba mu samu tattaunawa da ‘yan bindiga ba – Gwamnatin Neja

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Gwamnatin Jihar Neja ba ta samu wani kira daga 'yan ta'addan da suka sace masallata ba a wani masallaci da ke Ƙaramar Hukumar Borgu a ranar Juma'a, inji Kwamishinan Yaɗa Labaran Jihar Neja, Obed Nuhu. Nuhu ya bayyana haka ne a ranar Alhamis yayin wata hira da gidan talabijin na Channels, inda ya ce harin ya faru ne a wurare guda uku da ke yankin, wanda ake zargin ƙungiyoyin Lakurawa da Boko Haram da alhakin ƙaddamarwa. Rahotanni sun bayyana cewa, kwamishinan ya ce har yanzu gwamnatin ba ta samu damar tattaunawa ba da masu…
Read More

Hukumar bogi: ICPC ta zayyano manyan jami’an da suka taimaka wa Adeyemi bayan karɓar na goro

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ICPC, ta bankaɗo yadda aka zargi wasu jami'an gwamnati da taimaka wa Adeniyi Adeyemi, wato Darakta-Janar na hukumar bogi ta Presidential Foreign Intervention Promotion Council (PFIPC) wajen samun wasu amincewa na gwamnati da damar shiga tsarin kuɗaɗe da gudanarwa a hukumance. An bayyana haka ne a wani kundin rahoton binciken badaƙalar PFIPC na wucin-gadi da ICPC ta gudanar. Shugaba Bola Tinubu ne ya umarci a yi binciken bayan ayyana ƙungiyar a matsayin haramtacciya. Bincike ya nuna cewa, ikon da PFIPC ta samun ya kai ga ta yi…
Read More
An buƙaci shugabannin ƙananan hukumomi su ja mataimakansu a jiki

An buƙaci shugabannin ƙananan hukumomi su ja mataimakansu a jiki

Daga ABUBAKAR A BOLARI a Gombe Kwamishinan ƙananan hukumomi da cigaban al’umma na Jihar Gombe, Barista Sani A.A. Haruna, ya buƙaci shugabannin ƙananan hukumomi 11 da na yankunan cigaban ƙananan hukumomi (LCDA) da su riƙa bai wa mataimakansu muhimmiyar rawa wajen tafiyar da harkokin mulki. Haruna ya yi wannan kiran ne a wajen taron ƙara wa juna sani da ma’aikatar ƙananan hukumomi da cigaban al’umma ta shirya domin shugabannin ƙananan hukumomi da LCDA na jihar. Kwamishinan ya ce bai kamata shugabannin su mayar da mataimakansu saniyar ware ba, yana mai cewa sanya su cikin ayyukan gwamnati zai taimaka wajen inganta…
Read More
Miyetti Allah ta karrama Sanata Maidoki

Miyetti Allah ta karrama Sanata Maidoki

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Ƙungiyar Miyetti Allah reshen ƙaramar hukumar Zuru ta karrama Sanata Musa Garba Maidoki Sanata mai wakiltar gundumar Kebbi ta kudu.Shugabannin ƙungiyar miyetti Allah na ƙaramar hukumar ta Zuru sun bayyana cewa ɗan majalisar dattijan ya cancanci wannan karramawar bisa irin gagarumin ƙoƙari da jajircewar da ya ke nunawa wajen tallafa wa harkokin tsaro da zaman lafiya a yankin da ya ke wakilta. An shirya gabatar da wannan karramawa ne jiya yayin bikin taron ƙaddamar da shugabannin yaƙin neman zaɓe na jam’iyyar ADC ne saboda a nuna wa al'ummar jihar Kebbi irin ƙoƙarin da ya ke…
Read More
Zargin sace kayan asibiti: Hukumar NHMB ta kafa kwamitin bincike

Zargin sace kayan asibiti: Hukumar NHMB ta kafa kwamitin bincike

Daga JOHN D. WADA, a Lafiya Hukumar kula da asibitoci ta jihar Nasarawa (NHMB) ta kafa wani kwamiti domin binciken zargin sace kayayyakin asibitin gwamnati na yankin rayawa na Umaisha dake ƙaramar hukumar Toto a jihar. Bincike a kan lamarin ya tabbatar cewa ɗan majalisar dokokin jihar mai wakiltar mazaɓar Ugya/Umaisha Hon. Ibrahim Sa’ad ne ya bai wa asibitin kayan tallafin don a turo su zuwa Umaisha ɗin amma sai aka gano daga bisani cewa kayayyakin sun yi ɓatan dabo a yanzu haka. Dr. Egba Edego babban daraktan hukumar ne ya bayyana haka yayin da yake magana da manema labarai…
Read More

Babban Sakataren NLC, Ugboaja ya rasu

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Emmanuel Ugboaja, wanda shi ne Babban Sakataren Ƙungiyar Ƙwadago ta Ƙasa (NLC), ya rasu bayan shafe shekaru 60 a duniya. An sanar da rasuwarsa ne yayin da ake tsaka da zaman kwamitin zartarwar NLC da aka gudanar a Inugu, ranar Alhamis. Shugaban ƙungiyar Joe Ajaero ne ya sanar da labarin ga mambobi kwamitin bayan karɓar wata wasiƙa daga iyalan marigayin. A watan Agustan 2019 ne Ugboaja, wanda daɗaɗɗen ɗan ƙungiyar ƙwadago kuma lauya ne, ya zama babban sakataren NLC na biyar, inda ya gaji Peter Ozo-Eson a muƙamin. Ya rasu ne bayan shafe tsawon…
Read More