Babban Labari

Dalilina na ƙin karɓar takardar shaidar cin zaɓe a NNPP – Sanata Shekarau

Dalilina na ƙin karɓar takardar shaidar cin zaɓe a NNPP – Sanata Shekarau

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Sanata Ibrahim Shekarau, ya bayyana dalilinsa na ƙaurace wa taron miƙa wa  zaɓaɓɓun sanatoci takardar shaidar lashe zaɓen da aka gudanar a Abuja, Babban Birnin Tarayyar Nijeriya, a makon nan. Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana Malam Shekarau a matsayin wanda ya lashe zaɓen Sanatan Kano ta Tsakiya da aka yi ranar 25 ga Fabrairu, 2023 a ƙarƙashin jtsohuwar jam’iyyarsa ta NNPP maimakon jam’iyyarsa ta yanzu, PDP. Sai dai ɗan majalisar mai ci bai halarci taron miqa takardar shaidar lashe zaɓe ga zaɓaɓɓun sanatocin ba a ranar Talatar da ta gabata.…
Read More
Zaɓen 2023: Ana yi wa Tinubu kutingwila a Ingila

Zaɓen 2023: Ana yi wa Tinubu kutingwila a Ingila

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A wani yanayi mai nuna alamun kutingwila ga lashe zaɓen 2023 da zavavven Shugaban Ƙasa mai jiran gado a Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya yi, wasu ’yan Nijeriya da dama mazauna Birnin Landon, Babban Birnin Ƙasar Ingila, sun gudanar da wata gagarumar zanga-zanga a gaban ofishin jakadancin Nijeriya a ƙasar dake birnin Landan ɗin na ƙasar Birtaniya. Wannan ya faru ne jim kaɗan bayan Chatham House ya soki lamarin yadda aka tattara sakamakon zaɓen, wanda ya bai wa Tinubun nasara, inda gidan na dimukraɗiyya ya ce, ba a bi qa’idojin zaɓen da Hukumar Zaɓe Mai Zaman…
Read More
Ɗan Chana ya fallasa abubuwan ta’ajibi a shari’ar kisan Ummita

Ɗan Chana ya fallasa abubuwan ta’ajibi a shari’ar kisan Ummita

*Ba na roƙon kada a kashe ni, inji shi Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ɗan ƙasar Chana ɗin nan mai suna Frank Geng Quangrong mai shekaru 47 da ake tuhuma da laifin kashe masoyiyarsa, jiya Alhamis ya sake faɗa wa kotu a Kano cewa bai taɓa niyyar kashe budurwarsa ‘yar Nijeriya mai suna Ummukulsum Sani 'yar shekara 22, da aka fi sani da Ummita ba. Wanda ake tuhumar, mazaunin Railway Quarters a Kano, ana tuhumar sa da laifin kisan kai. Da lauyan gwamnati, Musa Lawal ke tambayar dalilin sa na zuwa gidan su Ummita ba tare da gayyata ba,…
Read More
Yadda aka tirsasa ni tafka maguɗin zaɓe don APC ta samu nasara – Farfesa Yakasai

Yadda aka tirsasa ni tafka maguɗin zaɓe don APC ta samu nasara – Farfesa Yakasai

Daga WAKILINMU Farfesa Ibrahim Adamu Yakasai na Jami’ar Bayero da ke Kano, ya bayyana yadda aka tilasta masa tafka maguɗi a sakamakon zaɓe a matsayinsa na Baturen Zaɓe a yankin Tudun Wadah, Kano, yayin zaɓen da ya gudana. Cikin wasiƙar da ya aika wa Hukumar Zaɓe ta Ƙasa, INEC, Ibrahim Yakasai ya aibata sakamakon zaɓen da ya bayyana bayan kammala zaɓen Shugaban Ƙasa da na 'yan majalisun tarayya. A cewarsa, tilasta masa aka yi kan ya tafka maguɗin zaɓe bayan da aka jefa rayuwarsa cikin haɗari a zahiri. Ya ce galibin sakamakon zaɓen da jami’an zaɓe suka bayyana ba na…
Read More
INEC ta ɗage zaɓen gwamnoni da na majalisun jihohi da mako guda

INEC ta ɗage zaɓen gwamnoni da na majalisun jihohi da mako guda

Daga BASHIR ISAH Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta kammala shirinta don ɗage zaɓen gwamnoni da na 'yan majalisun jihohi wanda ta shirya gudanarwa ran 11 ga Maris. Yadda al'amarin yake yanzu, shi ne, INEC ta ɗage zaɓe da mako guda zuwa ranar 18 ga Maris, 2023, kamar yadda wata majiya mai tushe ta shaida wa Jaridar News Point Nigeria. Manhaja ta gano ɗage zaɓen na da nasaba da gazawar INEC wajen saita na'urar BVAS ɗin da aka yi amfani da su a zaɓen ranar 25 ga Fabrairu don sake yin amfani da su wajen gudanar da zaɓen gwamnoni. Majiya…
Read More
ECOWAS za ta karrama Buhari kan bunƙasa dimokuraɗiyya

ECOWAS za ta karrama Buhari kan bunƙasa dimokuraɗiyya

Daga BASHIR ISAH Ƙungiyar Bunƙasa Tattalin Arzikin Ƙasashen Afirka ta Yamma (ECOWAS), ta ce ta kammala shirinta don karrama Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari da lambar yabo saboda nasarorin da ya samu a fannin tsaro da dimokuraɗiyya. Wannan na zuwa ne yayin da Buhari yake shirin kammala wa'adin mulkinsa na biyu. Shugaban ECOWAS kuma Shugaban Ƙasar Guinea Bissau, Umaro Sissoco Embalo, shi ne ya bayyana haka a wajen taron ƙawancen da suka yi yayin da suka haɗu a wajen Babban Taron Majalisar Ɗinkin Duniya da aka gudanar a Doha, babban birnin Qatar. Shugaba Embalo ya ce Buhari ya taka rawar gani…
Read More
INEC ta garzaya kotu kan sake fasalin na’urar BVAS

INEC ta garzaya kotu kan sake fasalin na’urar BVAS

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Rahotanni sun bayyana cewa Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), ta ce za ta garzaya Kotun Ɗaukaka Ƙara domin ba ta damar sake fasalin tsarin tantance masu kaɗa ƙuri’a (BVAS) a gwamnoni da na 'yan majalisun jihohi da za a yi ranar 11 ga Maris, 2023. Wani babban jami’in hukumar da bai so a ambaci sunansa ya shaida wa Aminiya irin ci gaban da aka samu a ƙarshen mako a Abuja. Majiyar ta yi nuni da cewa wannan umarni na da matuƙar muhimmanci biyo bayan umarnin da aka ba shi na hana…
Read More
BIDIYO: Atiku da wasu jiga-jigan PDP sun jagoranci zanga-zanga zuwa ofishin INEC

BIDIYO: Atiku da wasu jiga-jigan PDP sun jagoranci zanga-zanga zuwa ofishin INEC

Daga BASHIR ISAH Ɗan takarar Shugaban Ƙasa ƙarƙashin Jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar, tare da abokin takarsa, Ifeanyi Okowa sun jagoranci zanga-zangar lumana zuwa babban ofishin Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) a Abuja. Daga cikin waɗanda aka hango su a dandazon masu zanga-zangar, har da shugaban PDP na ƙasa, Iyorchia Ayu, Abiye Sekibo, Dino Melaye da kuma Uche Secondus. Zanga-zangar ɓangare ne na ci gaba da nuna rashin yarda da sakamakon zaɓen Shugaban Ƙasa da na 'yan majalisun tarayya da ya guda asabar ta makon jiya, inda mambobin jam'iyyar suke zargin ba a yi adalci ba. Zanga-zangar wadda aka faro ta…
Read More
Sulhu: Atiku ya fatattaki su Ganduje, ya ce da masu daraja zai zauna

Sulhu: Atiku ya fatattaki su Ganduje, ya ce da masu daraja zai zauna

Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Wazirin Adamawa kuma ɗan takarar Jam’iyyar PDP a zaven 2023, Alhaji Atiku Abubakar, ya fatattaki tawagar neman sulhun da zaɓaɓɓen Shugaban Nijeriya mai jiran gado, Asiwaju Ahmed Bola Tinubu, ya aike masa, wacce ta ƙunshi Gwamnan Jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje, Gwamnan na Kebbi Atiku Bagudu, na Jihar Jigawa Badaru Abubakar da na Jihar Nasarawa Abdullahi Sule tare da tsohon Shugaban Hukumar EFCC Nuhu Ribadu. Majiya mai tushe daga jikin tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasar ta shaida wa News Point Nigeria cewa, nan take Atikun ya ja kunnensu da kada ya sake ganin ƙeyarsu a…
Read More
Shugabannin duniya sun yi na’am da zaɓen Tinubu

Shugabannin duniya sun yi na’am da zaɓen Tinubu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Sabon zaɓaɓɓen shugaban Tarayyar Nijeriya mai jiran gado, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, yana cigaba da samun tagomashi a duniya ta hanyar karɓar saƙon taya murna daga shugabannin ƙasashen duniya, inda kawo yanzu kusan dukkan manyan ƙasashen duniya masu faɗa-a-aji sun aiko masa da saƙonnin taya murna tare da ba shi tabbacin za su yi aiki tare da shi. Idan za a iya tunawa, a ranar Laraba, 1 ga Maris, 2023, Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta a Nijeriya ƙarƙashin jagorancin Shugaban Hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, ta sanar da Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaɓen Shugaban Ƙasa…
Read More