Babban Labari

2023: Gwamnoni 17 sabbin yankan rake – 9 ’yan tazarce – 2 ’yan jiran tsammani

2023: Gwamnoni 17 sabbin yankan rake – 9 ’yan tazarce – 2 ’yan jiran tsammani

Daga SANI AHMAD a Abuja A ranar Asabar, wacce ta zo daidai da 18 ga Maris, 2023, ne aka gudanar da zaɓen gwamnoni da na ’yan majalisun dokokin Nijeriya bayan kusan kammala wa’adin mulkinsa na yanzu. An gudanar da zaɓukan gwamnonin a jihohi 28, yayin da sauran takwas kuma aka gudanar da na majalisun dokokin jihohin tare da na jihohin 28. Ma’ana; an yi zaɓen ’yan majalisar dokokin jihohin Nijeriya 36 bakiɗaya, amma a jihohi 28 ne kawai aka yi na gwamnoni. Wannan ya biyo bayan wasu hukunce-hukuncen Kotun Ƙoli ne da ya shafi zangon mulkin wasu jihohi ne, waɗanda…
Read More
Tukur Mamu ya ƙi amsa tuhuma

Tukur Mamu ya ƙi amsa tuhuma

Daga SANI AHMAD GIWA Tsohon mai shiga tsakani wajen tattaunawa da 'yan ta'adda, Tukur Mamu, ya ƙi amsa tuhumar laifuka 10 da Gwamnatin Tarayya ke zarginsa da aikatawa. A ranar Laraba ofishin Babban Lauyan Nijeriya ya gurfanar da Mamu a gaban Mai Shari'a Inyang Ekwo na Babban Kotun Tarayya da ke Abuja kan zargin taimaka wa 'yan ta'adda. Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya ya bayar da rahoton cewa, Mai Shari’a Nkeonye Maha na wata kotun tarayya a ranar 13 ga watan Satumba, 2022, ta bai wa hukumar tsaro ta farin kaya, SSS, izinin tsare tsohon ɗan mai sasanci tsakanin 'yan ta'addan…
Read More
Gwamnati ta gurfanar da Tukur Mamu

Gwamnati ta gurfanar da Tukur Mamu

Daga WAKILINMU Gwamnatin Tarayya ta gurfanar da tsohon mai shiga tsakani wajen tattaunawa da 'yan ta'adda, Tukur Mamu, kan zargin laifuka 10 da suka haɗa da taimaka wa 'yan ta'adda da sauransu. A ranar Laraba Ofishin Babban Lauyan Ƙasa (AGF) ya gurfanar da Mamu a madadin Gwamnatin Tarayya a gaban Mai Shari'a Inyang Ekwo na Babbar Kotun Tarayya a Abuja. Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya rawaito cewar, a ranar 13 ga Satumban 2022 wata kotu ƙarƙarshin jagorancin Alƙali Nkeonye Maha, ta bai wa hukumar tsaro ta DSS damar tsare Mamu na kwana 60 domin ba ta damar kammala…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Kano ta zama ta Abba Yusuf

Da Ɗumi-ɗumi: Kano ta zama ta Abba Yusuf

Daga BASHIR ISAH Hukumar Zaɓe INEC, ta tabbatar da ɗan takarar gwamna na Jam'iyyar NNPP a Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar. Abba ya taki wannan matsayi ne bayan da ya samu ƙuri'u 1,019,602 wanda hakan ya ba shi damar doke babban abokin hamayyarsa na APC kuma Mataimakin Gwamnan jihar mai ci, Nasiru Yusuf Gawuna, wanda ya tsira da ƙuri'u 890,705 a zaɓen. INEC ta ce Muhammad Sani Abacha na Jam'iyyar PDP, shi ne ya zo na uku da ƙuri'u 15,957. Da safiyar wannan Litinin INEC ta ayyana Abba sabon zaɓaɓɓen Gwamnan Kano…
Read More
Bayan shafe sa’o’i uku a kan layi, Gwamna El-Rufai ya kaɗa ƙuri’arsa

Bayan shafe sa’o’i uku a kan layi, Gwamna El-Rufai ya kaɗa ƙuri’arsa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Bayan haƙuri a kan layi na tsawon lokaci, gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya sauke nayinsa na jama'a a mazaɓarsa na PU024 da ke Unguwar Sarki GRA a Ƙaramar Hukumar Kaduna ta Arewa. Da yake magana da manema labarai bayan kaɗa ƙuri’arsa, El-Rufai ya ce, ana neman masu kaɗa ƙuri’a a yankin Kudancin Kaduna da su zaɓi wata jam’iyya ko kuma su koma gidajensu. Ya ce, a halin yanzu jami’an tsaro na gudanar da bincike a jihar. Gwamnan ya ce, an gudanar da zaɓen a wasu rumfunan zaɓe ba tare da wata matsala ba. “Babu komai,…
Read More
Zaɓen gwamnoni: A ina za a iya yin ‘inconclusive’ bana?

Zaɓen gwamnoni: A ina za a iya yin ‘inconclusive’ bana?

*Ba a san maci tuwa ba..! Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Gobe ake gudanar da zaɓen gwamnoni da na majalisar dokoki na jihohi a Tarayyar Nijeriya, waɗanda ake sa ran rantsarwa a ranar 29 ga Mayu, 2023, bayan kammala wa’adin zangon gwamnoni da ’yan majalisar dokoki na jihohi. Zaɓen da ya gabata na 2019 ya zo da wani sabon salon ƙa’idar da ba a saba gani ba a zaɓukan baya, inda ba a sanar da sakamakon zaɓe bisa dalilin wata kalma ta ‘inconclusive’, wacce ta ke nufin ‘rashin kammaluwa’ ko kuma ‘zaɓen da bai kammalu ba’. Shin mene ne…
Read More
Gwamnati ta daƙile kutse ta yanar gizo sau miliyan 12.9 lokacin zaɓen Shugaban Ƙasa – Pantami

Gwamnati ta daƙile kutse ta yanar gizo sau miliyan 12.9 lokacin zaɓen Shugaban Ƙasa – Pantami

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnatin Tarayya ta bakin Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na Zamani, Isa Pantami, ta bayyana cewa an samu jimillar hare-hare 12,988,978 da suka samo asali daga ciki da wajen Nijeriya a lokacin zaɓen Shugaban Ƙasa da ya gudana 25 ga Fabrairu, 2023. A cewar Pantami, a kullum ana samun barazanar da bai gaza 1,550,000 ta yanar gizo da kafofin sadarwa, inda ya ƙara da cewa alƙaluma daga bisani suka haura zuwa 6,997,277 a ranar zaɓen Shugaban Ƙasa. Wata sanarwa a ranar Talata ta bakin mai magana da yawun Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na…
Read More
CBN ya bai wa bankuna odar ci gaba da karɓar tsoffin kuɗi

CBN ya bai wa bankuna odar ci gaba da karɓar tsoffin kuɗi

Daga BASHIR ISAH Babban Bankin Nijeriya (CBN), ya ba da umarnin bankuna su ci gaba da karɓa da kuma ba da tsoffin tarkadun kuɗi na N200 da N500 da N1000 har zuwa 31 ga Disamban 2023. CBN ya amince da hakan ne domin cika umarnin Kotun Ƙoli biyo bayan hukuncin da kotun ta yanke ran 3 Maris inda ta buƙaci da a ci gaba da amfani da tsoffin kuɗin har zuwa ƙarshen wannan shekarar. Muƙaddashin Daraktan Sadarwa na bankin, Isa AbdulMumin, shi ne ya bayyna amincewar CBN na ci gaba da amfani da tsoffin kuɗin a sanarwar da ya fitar…
Read More