Babban Labari

Takardun kuɗi: CBN ya ce ba zai yi biyayya ga Kotun Ƙoli ba

Takardun kuɗi: CBN ya ce ba zai yi biyayya ga Kotun Ƙoli ba

*Ya ce duk mai tsohon kuɗi ya kai CBN Daga AISHA ASAS Babban Bankin Nijeriya (CBN), ya ce tsofaffin takardun kuɗi na N200, N500 da kuma N1000 sun daina amfani a hukumance tun daga ran 10 ga Fabrairu, 2023. Bayanin haka ya fito ne daga bakin shugaban CBN a Bauchi, Haladu Idris Andaza, yayin zantawarsa da manema labarai ranar Litinin a garin Bauchi. Ya ce, “A tsakanin awowi 24 da suka gabata, mun samu tambayoyi da yawa daga wajen mutane game da batun tsoffin kuɗi." A cewarsa, "domin kawar wa jama'a shakku, muna sanar da cewa a shirye CBN yake…
Read More
Buhari ya kafa majalisar bankwana da mulki

Buhari ya kafa majalisar bankwana da mulki

Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya kafa majalisar da za ta lura da yadda zai miƙa mulki ga sabuwar zaɓaɓɓiyar gwamnatin farar hula a watan Mayu na 2023 bayan kammala zaɓen da za a gudanar a watan nan na Fabrairu, 2023, cikin nasara. Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Boss Mustapha, ne ya bayar da sanarwar a jiya, Alhamis, 9 ga Fabrairu, 2023, mai ɗauke da sa hannun Daraktan Yaɗa Labarai, Mista Willie Bassey. Sanarwar ta ce, shi kansa Sakataren Gwamnatin ne zai jagoranci majalisar tare da Shugaban Ma’aikata na Gwamnatin Tarayya da Solisita Janar kuma…
Read More
Majalisar Ƙasa ta amince da sake fasalin Naira

Majalisar Ƙasa ta amince da sake fasalin Naira

*Ta buƙaci CBN ya ba da himma wajen samar da wadatattun sabbin takardun Naira Daga BASHIR ISAH Majalisar Ƙasa ta amince da sake fasalin takardun Naira na 200, 500 da kuma 1000 da Babban Bankin Nijeriya (CBN), ya yi. Majalisar ta nuna amincewarta ne yayin zaman da ta yi ranar Juma'a a Fadar Shugaban Ƙasa ƙarƙashin jagorancin Shugaba Muhammadu Buhari. Ta kuma shawarci CBN da ya ba da himma wajen aiwatar da sabbin tsare-rsarensa domin rage wa 'yan ƙasa wahalar ƙarancin kuɗi da suke fuskanta. Da yake zantawa da manema labarai jim kaɗan bayan taron, Babban Lauyan Ƙasa kuma Ministan…
Read More
Kotu ta dakatar da CBN aiwatar da dokar taƙaita cire kuɗi

Kotu ta dakatar da CBN aiwatar da dokar taƙaita cire kuɗi

…Ta yi barazanar tsare shugabannin bankuna Daga BASHIR ISAH Babban Kotu mai zamanta a Anuja, ƙarƙashin Mai Shari'a Eneojo Eneche, ta dakatar da Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, Babban Bankin Nijeriya (CBN) da kuma wasu bankuna 27 daga aiwatar da wa'adin daina amfani da tsoffi Naira na 10 ga Fabrairu ko bayar da wani umarni saɓanin wa'adin. Kazalika, kotun ta ba da umarnin shugabannin kotunan da lamarin ya shafa su ba da dalilin da ya sa ba za a tsare su tare da hukunta su ba saboda ɓarnar da suka yi wa fannin kuɗin ƙasa ta hanyar ɓoye sabbin Naira, wato…
Read More
Sabbin Naira: Gwamnonin APC 3 sun maka Gwamnatin Tarayya a kotu kan ƙarancin kuɗi

Sabbin Naira: Gwamnonin APC 3 sun maka Gwamnatin Tarayya a kotu kan ƙarancin kuɗi

Daga BASHIR ISAH Gwamnanonin Kaduna da Kogi da kuma Zamfara sun maka Gwamnatin Tarayya a Kotun Ƙoli kan batun canjin kuɗi. Sun kai ƙara kotun ne inda suke neman kotu ta hana Gwamnatin aiwatar da cikakkun matakan da ta ɗauka dangane da sabbin kuɗaɗen. Ƙarar da suka shigar ta hannun lauyansu, AbdulHakeem Uthman Mustapha (SAN), gwannonin sun buƙaci Kotun Ƙoli da ta ba ikon dakatar dakatar da Gwamnatin Tarayya ko CBN da sauran bankuna dakatar da su daga hana kawo ƙarshen tsoffin takardun Naira na 200 da 500 da 1000. Waɗanda suka shigar da ƙara sun haɗa da Manyan Lauyoyi…
Read More
Canjin takardun kuɗi: Na san za ku sha wahala – Buhari

Canjin takardun kuɗi: Na san za ku sha wahala – Buhari

*Ya ce, salon yaƙi da cin hanci da bunƙasa arziki ne*Mun daidaici wannan lokacin ne da gayya, inji shi Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya bayyana jimaminsa kan yadda ’yan Nijeriya ke shan azaba sakamakon canjin fasalin manyan takardun Naira, yana mai bayyana cewa, shan azabar ya zama wajibi matuƙar Nijeriya ta na son ta kawo ƙarshen matsalar annobar cin hanci da rashawa da ta yi kaka-gida a ƙasar da kuma bunƙasa tattalin arzikin ƙasar. Kalaman na Shugaban Ƙasa sun fito ne daga bakin Ministar Kuɗi da Tsare-tsaren Ƙasa, Hajiya Zainab Ahmed, bayan kammala zaman…
Read More
‘Ku ba ni kwana 7 zan magance ƙarancin kuɗi’ – Buhari

‘Ku ba ni kwana 7 zan magance ƙarancin kuɗi’ – Buhari

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya yi kira ga 'yan Nijeriya da su ba shi kwana bakwai domin kawo ƙarshen matsalar ƙarancin kuɗin da ake fuskanta a ƙasa sakamakon canjin kuɗin da CBN ya yi. A wata sanarwa da ya fitar, mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Femi Adesina, ya ce Buhari ya bayyana haka ne yayin ganawarsu da ƙungiyar gwamnoni ta Progressive Governors Forum ranar Juma'a a Fadar Shugaban Ƙasa. Gwamnonin sun ziyarci Buharin ne domin tattauna mafita dangane da ƙarancin kuɗin da ake fama da shi a ƙasa baki ɗaya wanda a cewarsu lamarin na barazana…
Read More
Babu mahalukin da nake tsoro, cewar El-Rufai ga manyan Fadar Shugaban Ƙasa

Babu mahalukin da nake tsoro, cewar El-Rufai ga manyan Fadar Shugaban Ƙasa

Daga WAKILINMU Gwamna Nasir El-Rufai na Jihar Kaduna, ya kalubalancin ’yan Fadar Shugaban Ƙasa da yake zargi da zagon-ƙasa ga takarar Bola Tinubu a zaɓen Shugaban Ƙasa mai zuwa. Tun a ranar Laraba El-Rufai ya fara tayar da ƙura da zargin cewa akwai jami’an Fadar Shugaban Ƙasa da ke neman yi wa takarar Tinubu ƙafar ungulu. A wata hirarsa da BBC Hausa, an ji shi yana cewa, “Na rantse babu mahaluƙin da nake tsoro a duk faɗin ƙasar nan. “Don ana ganin girman mutum ba tsoronsa ake ji ba; amma idan muna girmama mutum sannan yana nuna shi ba babba…
Read More
CBN ya tswaita wa’adin daina karɓar tsoffin takardun Naira da kwana 10

CBN ya tswaita wa’adin daina karɓar tsoffin takardun Naira da kwana 10

Daga BASHIR ISAH Babban Bankin Najeriya (CBN) ya tsawaita wa'adin daina karbar tsoffin takardun Naira ya zuwa 10 ga Fabrairu, 2023. Gwamnan CBN, Godwin Emefiele ne ya ba da sanarwar ƙarin wa'adin a sanarwar da ya fitar ranar Lahadi. Ya ce, sai da CBN ya nemi amincewar Shugaba Muhammadu Buhari kafin ɗaukar matakin tswaita wa'adin da kwana 10. “La'akari da halin da ake ciki, mun nemi yardar Shugaban Ƙasa kan waɗannan abubuwa: Sahalewar tswaita wa'adin da kwana 10 daga 31 ga Janairu zuwa 10 ga Fabrairu don ba ba da damar ci gaba da karɓar tsoffin takardun Naira daga hannun…
Read More
An yi wa Buhari bore a Katsina

An yi wa Buhari bore a Katsina

*Matasa sun yi ƙone-ƙone kan babbar hanyar da Shugaban Ƙasa ya buɗe Daga UMAR GARBA a Katsina Wasu matasa da ake kyautata zaton ’yan bangar siyasa ne, sun yi zanga-zanga tare da ƙona tayoyi akan hanyar Yahaya Madaki dake birnin Katsina, Babban Birnin Jihar Katsina a jiya Alhamis. Lamarin ya faru ne jim kaɗan bayan Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya buɗe wasu tagwayen hanyoyin gadar ƙasa a yayin ziyarar aiki da ya kai jihar tasa ta haihuwa. Matasan, waɗanda suka hau kan hanyar, sun yi ta ihu tare da faɗin “ba ma yi! Ba ma yin jam'iyyar APC!” kamar yadda…
Read More