Babban Labari

2023: Sauya fasalin Naira da ƙarancin fetur ba za su hana nasarata ba – Tinubu

2023: Sauya fasalin Naira da ƙarancin fetur ba za su hana nasarata ba – Tinubu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa a ƙarƙashin Jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu, ya yi zargin matsalar ƙarancin man fetur da ake fuskanta da sauya fasalin wasu takardun Naira da aka yi, take-taken neman wargaza zaɓen 2023 ne kawai. Tinubu ya bayyana haka ne yayin gangamin yaqin neman zaɓen APC da ya gudana ranar Laraba a Abeokuta, babban birnin Jihar Ogun. “Ba sa son zaɓen ya gudana. So suke su wargaza shi. Za ku bari hakan ta faru?” inji Tinubu. Ɗan takarar ya ce, yana da yaƙinin matsalar ƙarancin fetur ba za ta hana ’yan Nijeriya zuwa kaxa…
Read More
Canjin takardun Naira: Kakakin Majalisa ya yi barazanar cafko masa Emefiele

Canjin takardun Naira: Kakakin Majalisa ya yi barazanar cafko masa Emefiele

•Yadda al’amura suka kwaɓe Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Kakakin Majalisar Wakilai, Rt. Hon. Femi Gbajabiamila, ya ce, zai bayar da umarnin a cafko masa Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele, da manajan daraktocin bankuna bisa kunnen uwar shegu kan sammacin da majalisar ta aika musu kan batun canjin sababbin takardun kuɗi. Kakakin Majalisar ya bayyana hakan a zauren majalisar jiya Alhamis, 26 ga Janairu, 2023, yana mai cewa, maimakon majalisar ta ɗage zamanta zuwa ranar 28 ga Fabrairu, 2023, bayan kammala zaven Shugaban Ƙasa da na Majalisar Dokoki ta Ƙasa, kamar yadda tun da fari aka tsara,…
Read More
Shugabannin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi sun ajiye muƙamansu

Shugabannin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi sun ajiye muƙamansu

Daga JAMIL GULMA a Kebbi  Bayan wani zama na gaggawa da shugabannin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi suka yi a jiya Alhamis, sun yanke shawarar ajiye muƙamansu. Wannan yana ƙunshe a cikin wata takarda mai ɗauke da sa hannun Shehu Muhammed Yauri, sakataren yaɗa labarai na majalisar. Sai dai takardar ba ta bayyana dalilin ajiye muƙaman da suka yi ba. Shugabannin majalisar dokokin da suka sauka daga kan muƙaman nasu dai sun haɗa da Mataimakin Kakakin  Majalisar da Mai Tsawatawa da mataimakinsa zuwa shugabannin masu rinjaye da marasa rinjaye da mataimakansu. Har wa yau dai, ’yan majalisar sun nemi gwamnan jihar,…
Read More
Nijeriya za ta fara cire tallafin fetur daga watan Afrilu

Nijeriya za ta fara cire tallafin fetur daga watan Afrilu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Gwamnatin Nijeriya ƙarƙashin shugaba Muhammadu Buhari na iya fara cire tallafin man fetur sannu a hankali daga watan Afrilun 2023, kimanin watanni uku gabanin shirin farko na dakatar da shugaban na kashe kuɗaɗe. Ministar Kuɗi, Kasafi da Tsare-tsaren Ƙasa, Hajiya Zainab Ahmed ce ta bayyana hakan a ranar Talata yayin wata tattaunawa da ta yi da gidan talabijin na ARISE a gefen taron tattalin arzikin duniya da aka gudanar a birnin Davos na ƙasar Switzerland. Ta bayyana cewa, cire tallafin da alama matsayin duk masu neman shugabancin qasar ne a yaƙin neman zaɓensu na siyasa a…
Read More
Nijeriya ta fi dukkan Afirka shigo da janareto – Bincike

Nijeriya ta fi dukkan Afirka shigo da janareto – Bincike

Daga AMINA YUSUF ALI Wani sakamakon bincike da Hukumar Sabunta Makamashi Ta Duniya  (IRENA) ta gudanar ya bayyana cewa, Nijeriya ita ce jagaba wajen shigo da injin janareto a faɗin ƙasashen Afirka gabaɗaya.  Rahoton mai taken ECN ya bayyana dalilan da suka sanya 'yan Nijeriya suka dogara matuƙar dogara da janareto da kuma illarsa ga tattalin arzikin ƙasar da sana'o'i.  Sana'o'i da gidaje da dama a ƙasar sun dogara ne kacokan a kan injinan janareto don samun wuta saboda ƙarancin wutar lantarki a ƙasar.  Saboda haka, rashin isasshen sinadarin gas, tangarɗar na'urori da rashin wadatar tashoshin wutar su na daga…
Read More
SSS ta mamaye CBN, ta karbe ikon ofishin Emefiele

SSS ta mamaye CBN, ta karbe ikon ofishin Emefiele

Daga WAKILINMU A ranar Litinin jami'an hukumar tsaro ta SSS suka mamaye ginin hedkwatar Babban Bankin Nijeriya (CBN) da ke Abuja inda suka karɓe ikon ofishin Gwamnan Bankin, Godwin Emefiele. Jaridar Daily Nigerian ta rawaito cewar ba yau SSS ta fara farautar Emefiele ba kan zargin almundahana. A baya, hukumar SSS ta buƙaci kotu ta ba ta izinin tsare Emefiele amma ya zamana ba ya ƙasa sakamakon hutu da ya tafi wanda zai ƙare ranar Talata, 17 ga Janairu. Sai dai a Disamban da ya gabata Babbar Kotun Abuja ta haramta wa SSS cafke Emefiele, ko tsare shi, ko kuma…
Read More
Rikici ya ɓarke tsakanin Hausawa da Fulani a Ondo

Rikici ya ɓarke tsakanin Hausawa da Fulani a Ondo

*An rasa ran mutum*Gwamnatin jihar ta saka dokar ta-ɓaci Daga MAHDI M. MUHAMMAD Mutum ɗaya ya rasa ransa tare da lalata kadarori da dama sakamakon rikicin da ya ɓarke tsakanin wasu Fulani da Hausawa mazauna yankin Ogbese da ke Ƙaramar Hukumar Akure ta Arewa a jihar Ondo. An tattaro cewa, rikicin da ya faro tun a yammacin ranar Talata 3 ga watan Junairun 2022 inda ya yi ƙamari da safiyar Laraba 4 ga watan Junairun 2022, wanda aka qona shaguna da dama na ’yan Arewa a babbar kasuwar garin. Har yanzu dai ba a san ainihin musabbabin faɗan a hukumance…
Read More
Buhari ya rattaɓa hannu a kasafin 2023

Buhari ya rattaɓa hannu a kasafin 2023

Daga BASHIR ISAH A ranar Talata Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya rattaɓa hannu a kasafin 2023 na Naira tiriliyan 21.83. Rattaɓa hannun ya haɗa da na ƙarin kasafin 2022 da Majalisar Tarayya ta sahale wa Buharin. Wannan dai shi ne karo na takwas kuma na ƙarshe da Buhari zai rattaɓa wa Kasafin Ƙasa hannu tun bayan da mulkin ƙasa ya koma hannunsa kusan shekara takwas da suka gabata. Da yake jawabi, Buhari ya ce an samu ƙarin tiriliyan N1.32 kan tiriliyan N20.51 da aka kasafta tun farko wanda hakan ya sa kasafin ya ƙaru zuwa tiriliyan N21.83. Shugaban ya ce…
Read More
2023: Buhari ya taya ‘yan Nijeriya murnar sabuwar shekara

2023: Buhari ya taya ‘yan Nijeriya murnar sabuwar shekara

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya taya 'yan Nijeriya murnar shiga sabuwar shekara ta 2023. Cikin saƙon nasa Buhari ya gode wa Allah da Ya ƙaddari 'yan ƙasar da ke raye ganin wannan lokaci. Ya yi fatan duka 'yan Nijeriya da suka kwanta dama kafin sabuwar shekarar, mutuwa ta zama hutu a gare su. Ya ce nan da wata biyar Nijeriya za ta samu sabon Shugaban Ƙasa da gwamnoni da sauransu. Don haka ya sha alwashin gudanar da sahihin zaɓe ƙarƙashin Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), don bai wa 'yan ƙasa damar zaɓen shugabannin da suka dace. Ya…
Read More
Majalisa ta amince wa Buhari ƙarin kasafin biliyan N819

Majalisa ta amince wa Buhari ƙarin kasafin biliyan N819

Daga BASHIR ISAH Majalisar Dattawa ta amince da ƙarin kasafin biliyan N819 da Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya gabatar mata don cike giɓin kasafin 2022. wannan na zuwa ne bayan da Majalisar ta ƙara wa'adin aiwatar da kasafin na 2022 zuwa ranar 31 ga Maris, 2023. Da farko dai Majalisar ta amince da tiriliyan N17.12 a matsayin kasafin 2022, daga bisani ta ƙara kasafin zuwa tiriliyan N17.31 bayan da Shugaba Buhari ya buƙaci hakan inda ya ce tasirin yaƙin Ukraine da Rasha ga tattalin arzikin ƙasa ya haifar da buƙatar ƙarin. A ranar Laraba Majlisar ta amince da kasafin bayan…
Read More