Adabi

Rashin kiyaye ƙa’idojin rubutu illa ce ga marubuci – Mubarak Jiƙamshi

Rashin kiyaye ƙa’idojin rubutu illa ce ga marubuci – Mubarak Jiƙamshi

"Manazarcin Hausa na samun tagomashi mai tsoka a harkar fashin baƙi ko tambihi" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Mubarak Idris Jikamshi, matashin marubuci ne daga Jihar Katsina, duk da kasancewar bai fitar da wasu littattafai masu yawa ba, amma yana da gajerun labarai da dama da ya yi, wasu ma har ya shiga gasannin marubuta da su, a mataki daban-daban. Wani abu da ya bambanta Mubarak da sauran marubuta shi ne kishin da yake da shi a nazarin ilimin harshen Hausa da kula da kiyaye ƙa'idojin rubutu, don yanzu haka yana matakin fara digirinsa na biyu ne a harshen Hausa. Bayan…
Read More
Marigayi Mada Garin Aliyu Babba Ɗan Malam Muhammadu Sambo

Marigayi Mada Garin Aliyu Babba Ɗan Malam Muhammadu Sambo

Daga IBRAHIM MUHAMMAD Asalin su Fulani ne da suka fito daga yankin Ningi ta Jihar Bauchi da zummar za su kai caffa a wajen Mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodiyo Tagammadahullahu birahamatihi a Sakkwato domin shiga dumu-dumu a cikin jihadin jaddada addinin Musulunci wanda Mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodiyo ya jagoranta. Sun zauna a wurare da dama kamar Ƙiru da Gwarzo (da ke Jihar Kano ta yau) da Matazu da Fawwa ( dake Jihar Katsina a halin yanzu) da kuma Wonaka da ke Jihar Zamfara ta yanzu, kafin daga bisani Malam Muhammadu Sambo ya jagorance su ya zuwa inda suke a halin yanzu.…
Read More
Idan ka ga marubuci yana rubutu ba ya samun kuɗi shi ya so – Sadik Lafazi

Idan ka ga marubuci yana rubutu ba ya samun kuɗi shi ya so – Sadik Lafazi

"Wasu ƙungiyoyin ba sa son ɗaukar sabon marubuci" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Baƙon marubucin mu na wannan mako shi ne Malam Sadik Abubakar Abdullahi, shugaban ƙungiyar Lafazi Writers Association, ɗaya daga cikin fitattun ƙungiyoyin marubuta na onlayin da suke taka rawar gani wajen fitar da littattafai masu ƙunshe da basira da darussa masu yawa, da kuma kiyaye ƙa'idojin rubutun Hausa. Ya kasance daga cikin maza marubuta da suka zama tamkar madubi ko ababen koyi ga matasan marubuta masu tasowa. A zantawarsa da wakilin Blueprint Manhaja Abba Abubakar Yakubu ya bayyana masa yadda yadda shi da wasu marubuta suka kafa ƙungiyar…
Read More
Rayuwar Sarki Haile Selassie na Habasha

Rayuwar Sarki Haile Selassie na Habasha

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Haile Selassie an haifeshi a ranar 23 ga watan Yuli na shekara ta 1892 a kusa da Harar cikin ƙasar Habasha, inda aka raɗa masa suna da Tafari Makonnen. Mahaifinsa amintacce ne kuma na kusa da Sarki Menelik na II. An kira shi zuwa kotu a Addis Ababa lokacin da babansa ya mutu a 1906. A 1916 ya zama mabiyin aqidar Ras Tafari, da ake zaton ya gaji sarauniya Zauditu da ke zaman 'ya ga Menelik na II. A shekara ta 1928 tare da magoya bayansa sun sanya sarauniyar ta ba shi sarauta. A shekara ta…
Read More
Duk waƙar da ta rubutu, babu wanda ba ya iya rera ta – Malumman Matazu

Duk waƙar da ta rubutu, babu wanda ba ya iya rera ta – Malumman Matazu

"Jigon waƙa na cikin ababen da ke ban wahala" (Ci gaba daga makon jiya) Daga AISHA ASAS A satin da ya gabata, shafin Adabi ya samu baƙuncin ƙwararre a ɓangaren rubutacciyar waƙa, Abdulhamid Muh'd Sani Matazu, inda muka faro tattaunawar kan abinda ya shafi ma'anar rubutacciyar waƙa da abinda ya bambanta ta da waƙar baka. Kafin mu kai ga tasirin da shawarwarin da suke bayarwa a waƙe suke yi. A wannan makon za mu ɗora ne daga inda muka tsaya: MANHAJA: Me yafi baka wahala a yayin rubuta waƙa? MALUMMAN MATAZU: Jigo ko dalilin waƙa na cikin abin da ke…
Read More
Makaɗin Hausa: Marigayi Salihu Jankiɗi (1852-1973)

Makaɗin Hausa: Marigayi Salihu Jankiɗi (1852-1973)

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An haifi Salihu Jankidi ne a garin Rawayya ta ƙasar Bungudu ne a yanzu cikin Ƙaramar Hukumar Gusau, wajejen shekara ta 1852. Sunan mahaifinsa Alhassan ɗan Giye ɗan Tigari mai abin kiɗi. Salihu shi ne sunansa na yanka, amma ƙanen mahaifiyarsa Kardau ya yi masa laƙabi na Jankiɗi saboda jan da Allah ya ba shi, wanda ya bi shi har bayan rasuwarsa. Alhassan Giye Ɗan Tigari: Mahaifin Jankidi Alhassan Makadi ne na kalangu kuma mai yawan yawace-yawace don kiɗa. Yakan bar garinsu Rawayya ya shiga uwa duniya don sana’arsa ta kiɗa. Shi kuma makaɗi ne na…
Read More
Rubutacciyar waƙa ta masu ilimi ce, waƙar baka kuwa ta kowa ce – Malumman Matazu

Rubutacciyar waƙa ta masu ilimi ce, waƙar baka kuwa ta kowa ce – Malumman Matazu

"Duk wanda yake yin rubutacciyar waƙa zai iya waƙar baka" Daga AISHA ASAS  A wannan satin dai ba bako shafin adabi ya kawo wa masu karatu ba, kasancewar mun saba kawo shi a bangarori da dama na adabi. Don haka za mu wuce kai tsaye ga tattaunawar.  Idan kun shirya Aisha Asas ce tare da Malumman Matazu: MANHAJA: Duk da ba ka kasance bako a jaridar Manhaja ba, za mu so mu ji takaitaccen tarihinka? MALUMMAN MATAZU: Bismillahirrahmanirrahim. Da farko dai cikakken sunana shi ne: Abdulhamid Muh'd Sani Matazu (Malumman Matazu). An haife ni a Gidan marigayi liman Malam Bala…
Read More
Wane ne Dr. Aliyu Ishaq Namangi?

Wane ne Dr. Aliyu Ishaq Namangi?

Daga MOHAMMED BALA GARBA Aliyu Namangi Malami ne, kuma mawaƙi mai wa'azi, wanda ya fito daga wani ƙauye mai suna Mangi a kusa da ƙaramar hukumar Zariya ta jihar Kaduna, a Arewacin Nijeriya. Wakoƙinsa sun yi matuƙar tasiri wajen ilmantarwa da karantarwa game da sukar mulkin kama-karya. Sufi ne mabiyin tafarkin Sufaye.  Masana da manazarta da dama sun kawo tarihin Aliyu Namangi a aikace-aikacensu da suka gudanar, ire-iren waɗannan ayyuka na manazarta kan Aliyu Namangi sun haɗa da Skinner (1969) da Ɗangambo (1973) da Hassan (1973) da Birniwa (1989) da Yakawada (1987) da Sankalawa (2005) da Muhammad (2010) da Muhammad…
Read More
Mutane na girmama ni saboda lashe gasar Hikayata – Aisha Fulani

Mutane na girmama ni saboda lashe gasar Hikayata – Aisha Fulani

"Zumuncin marubuta abin a yaba ne sosai" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Aisha Abdullahi Yabo ba bakuwa ba ce a cikin marubuta, musamman marubutan onlayin, inda take daya daga cikin masu ba da gagarumar gudunmawa ga cigaban adabin Hausa. Ita ce ta zo gwarzuwa ta biyu a Gasar Hikayata ta BBC Hausa ta 2023. 'Ya ce ga fitaccen malamin addinin Musuluncin nan na Jihar Zamfara, Sheikh Abdullahi Abubakar Yabo. Don haka babu mamaki jin cewa, Aisha da aka fi sani da Fulani, hafizar Alkur'ani Mai Girma ce, kuma masaniya a sauran fannonin ilimin addini, kuma har yanzu tana cigaba da neman…
Read More
Alhassan Ɗantata: Mutum mafi arziki a Afirika ta yamma a shekarar 1950

Alhassan Ɗantata: Mutum mafi arziki a Afirika ta yamma a shekarar 1950

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Alhassan Dantata, fitaccen attajiri a fadin nahiyar Afirika ta yamma, wanda tushen arzikinsa ya samo asali daga sayar da Goro da Gyada. Haihuwa da nasaba; Alhassan Dantata ya fito ne daga cikin zuri’ar Agalawa, iyayensa fatake ne masu yawon kasuwanci daga wannan gari zuwa wancan. An haife shi a shekarar 1877, a wani qaramin qauye da ake kira Danshayi a garin Bebeji, wanda ke da tazarar aqalla kilomita goma sha-biyar daga garin Kano. Alhasan daya ne daga cikin ’ya’yan Abdullahi wanda matarsa Fatima da ake kira Amarya ta haifa. Shi Abdullahi da ne ga wani mutum…
Read More