Siyasa

Na rungumi ƙaddarar faɗuwa zaɓe, ba zan je kotu ba, inji Kabiru Gaya

Na rungumi ƙaddarar faɗuwa zaɓe, ba zan je kotu ba, inji Kabiru Gaya

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Sanatan Kano ta Kudu, Kabiru Ibrahim Gaya ya bayyana cewa ya rungumi ƙaddarar faɗuwa zaɓen Majalisar Dattawa na shiyyar Kano ta Kudu da aka gudanar, wanda Sulaiman Abdulrahman Kawu Sumaila na Jam’iyyar NNPP ya yi nasara. Sanata Kabiru Gaya ya bayyana hakan ne cikin wani saƙon murya da aka raba wa manema labarai a Kano ranar Litinin. Kabiru Gaya ya kuma taya Kawu Sumaila murnar lashe zaɓen, tare da ba shi tabbacin ba zai ƙalubalanci sakamakon zaven a kotu ba. ”Sau huɗu na ci zaɓen Sanatan Kano ta Kudu, shekaru 16 kenan. Kuma a cikin…
Read More
Duk zaɓukan ’yan majalisar dokokin ƙasa na Sakkwato ba su kammalu ba – INEC

Duk zaɓukan ’yan majalisar dokokin ƙasa na Sakkwato ba su kammalu ba – INEC

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa duk zaɓukan ’yan Majalisun Tarayya da aka gudanar a jihar Sakkwato ba su kammala ba. An samu labarin cewa akwai tashe-tashen hankula da kuma rashin kaɗa ƙuri'a da wasu kura-kurai a zaɓukan. Akwai kujerun Sanata guda uku da na majalisar wakilai 11 a jihar. An tattaro cewa Gwamna Aminu Waziri Tambuwal ne ke jagorantar Sanata Ibrahim Danbaba Dambuwa na jam’iyyar APC a Sanatan Sakkwato ta Kudu kafin a bayyana ta da rashin kammaluwa. A sakamakon zaɓen, Tambuwal ya samu ƙuri'u 87,850 yayin da Dambuwa ya…
Read More
Zan zama shugaban kowa – Tinubu ya gode wa ‘yan Nijeriya bayan ya doke Atiku da Peter Obi

Zan zama shugaban kowa – Tinubu ya gode wa ‘yan Nijeriya bayan ya doke Atiku da Peter Obi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya gode wa ‘yan Nijeriya da suka ba shi jan ragamarsu, ya kuma ba su tabbacin cewa shi ne zai jagoranci kowa da kowa. Tsohon gwamnan na Legas ya yi wannan alƙawarin ne a lokacin da yake gabatar da jawabinsa na karrama shi biyo bayan ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaɓen Shugaban Ƙasa da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu. Tinubu, wanda shi ne ɗan takarar Jam’iyyar APC a zaɓen na ranar Asabar ya samu ƙuri’u 8,794,726 inda ya doke abokin hamayyarsa kuma ɗan…
Read More
Tinubu ya lashe zaɓen Shugaban Ƙasa

Tinubu ya lashe zaɓen Shugaban Ƙasa

*Yau za a miƙa masa takardar shaida Daga BASHIR ISAH Ɗan takarar shugabancin ƙasa na Jam'iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya zama sabon zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasar Nijeriya. Tinubu ya yaki wannan matsayi me biyo bayan zaɓaɓɓen da aka gudanar a ƙasar ran Asabar da ta gabata. Yau Laraba ake sa ran Hukumar INEC za ta miƙa wa Tinubu shaidar lashe zaɓaɓen da ya yi. Shugaban INEC, Farfesa Mahmoud Yakubu, shi ne ha ba da sanarwar nasarar da Tinubu ya samu, tare da cewa za a miƙa masa shaidar ne da misalin ƙarfe 3 na ranar a Babban Zauren Taro…
Read More
Ba mu yarda a soke sakamakon zaɓen shugaban ƙasa ba – APC

Ba mu yarda a soke sakamakon zaɓen shugaban ƙasa ba – APC

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kwamitim yaƙin neman zaɓe na ɗan takarar shugabancin Nijeriya na jam'iyya mai mulki APC, ya ce buƙatar da jam'iyyun hamayya suke gabatarwa ta soke zaɓen, ba za ta taɓa yiwuwa ba. Kwamitin ya bayyana haka ne a matsayin martani ga taron manema labarai da manyan jam'iyyun hamayya uku, PDP da LP da kuma APC suka yi inda suka ce sai dai a soke zaɓen na ranar Asabar. Kakakin kwamitin yaƙin neman zaɓen na APC Festus Keyamo, ya ce shugaban hukumar zaɓen ta INEC zai saɓa doka idan har ya soke zaɓen da tuni ya riga ya…
Read More
Tinubu ya shigar da ƙara don hana LP, PDP dakatar da tattara sakamakon zaɓe

Tinubu ya shigar da ƙara don hana LP, PDP dakatar da tattara sakamakon zaɓe

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) da ɗan takararta na Shugaban Ƙasa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, sun shigar da ƙara domin hana Jam’iyyar Labour Party (LP) da PDP yin wani abu na hana tattarawa da bayyana sakamakon zaɓen Shugaban Ƙasa na ranar 25 ga watan Fabrairu. A ƙarar da aka shigar gaban Babbar Kotun Tarayya dake Kano mai lamba FHC/KN/CS/43/2023, an haxa da Action Alliance da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta (INEC) a matsayin waɗanda ake ƙara, yayin da mataimakin shugaban Jam’iyyar APC, Kashim Shettima a matsayin mai gabatar da ƙara. Masu gabatar da ƙara…
Read More
Ba za a soke sakamakon zaɓe ba, inji Shugaban INEC

Ba za a soke sakamakon zaɓe ba, inji Shugaban INEC

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta shawarci jam’iyyun siyasa da ke ƙorafi da su nemi haƙƙinsu a kotu idan ba su gamsu da yadda zaɓen ke gudana ba, inda ta ƙara da cewa kiraye-kirayen da wasu jam'iyyu ke yi kan shugaban INEC, Mahmood Yakubu ya yi murabus bai dace ba. Idan dai ba a manta ba a ranar Litinin ne wakilan jam’iyyar PDP, Dino Melaye da Emeka Ihedioha suka fice daga babban taron INEC na ƙasa da ke Abuja bisa zargin tafka maguɗi a zaɓe. Wakilan wasu jam'iyyu, ciki har da na SDP,…
Read More
INEC ta sanar da Shekarau a wanda ya lashe zaɓen sanatan Kano ta tsakiya

INEC ta sanar da Shekarau a wanda ya lashe zaɓen sanatan Kano ta tsakiya

Daga IBRAHIM HAMISU, a Kano Hukumar Zaɓe ta Ƙasa, INEC, ta sanar da sunan Malam Ibrahim Shekarau a matsayin wanda ya lashe zaɓen Sanatan Kano ta tsakiya a ƙarƙashin Jam’iyyar NNPP. Baturen zaɓen Farfesa Tijjani Hassan Darma ne ya bayyana Sanata Shekarau a matsayin wanda ya lashe zaɓen da ƙuri’a 456,787 akan babban abokin karawarsa na Jamiyyar APC Abdulkarim Abdussalam Zaura wanda ya sami ƙuri’a 168, 677, da Hajiya Laila Buhari ta jam'iyyar PDP da kuri'a 55,237, Jim kaɗan bayan kammala faɗin sakamakon wakilin jam'iyyar NNPP ya ƙalubalanci hukumar zaɓe akan kin canja sunan Shekarau wanda tuni ya koma jam'iyyar…
Read More
El-rufa’i ya rasa kujerun sanatoci uku a Kaduna

El-rufa’i ya rasa kujerun sanatoci uku a Kaduna

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-rufa'i ya rasa kujerun sanatoci na dukkan shiyyoyi uku da ke faɗin jihar. El-rufa'i wanda na gaba-gaba ne a Jam'iyyar APC kuma mai faɗa a ji a cikinta, ya rasa kujerar Sanatan Kaduna ta Tsakiya wanda Muhammad Sani Dattijo na APC ke takara da abokin karawarsa na Jam'iyyar PDP, wato Lawal Adamu wanda aka fi sani da Mr LA. Dattijo dai ana ganin ɗan lele ne a gwamnatin Jihar Kaduna, domin ya riƙe manyan muƙamai a gwamnatin El-rufa'i, ciki har da Shugaban Ma'aikatan Gidan Gwamnatin jihar, da kuma Kwamishinan…
Read More
Jami’in tattaran sakamakon Jihar Ribas ya yi zargin barazana da rayuwarsa

Jami’in tattaran sakamakon Jihar Ribas ya yi zargin barazana da rayuwarsa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jami’in tattara sakamakon zaɓen Shugaban Ƙasa a Jihar Ribas, Farfesa Teddy Charles Adias, ya dakatar da aikin tattara sakamakon zaɓe saboda abin da ya bayyana a matsayin barazana ga rayuwarsa. Kafin dakatarwar, an tattara sakamakon ƙananan hukumomi 21 cikin 23 na jihar. Sakamako ne kawai daga ƙananan hukumomin Obio Akpor da Degema, wanda aka ce za a tattara a safiyar yau. Adias, wanda shi ne Mataimakin Shugaban Jami’ar Tarayya, Otuoke, Jihar Bayelsa, ya sanya ranar Talata don tattara sakamako a ƙananan hukumomin. Sai dai a safiyar ranar Talata, ya ce waɗanda ke yi wa…
Read More