Wasanni

Hada-hadar kasuwar ’yan wasan ƙwallon ƙafa

Hada-hadar kasuwar ’yan wasan ƙwallon ƙafa

Arsenal ta ɗauki zaɓin sayen mai tsaron gidanta Daɓid Raya da tauka aro daga Brentford kan kuɗi fan miliyan 27. Raya mai shekara 28 ya buga wasannin gasar firimiya 16 ba tare da an zura masa ƙwallo a raga ba. An zura masa ƙwallo 16 ne kacal a gasar firimiya sannan a ƙarshe ya lashe kyautar maitsaron ragar da ya fi kowanne ƙoƙari a kakar da ta gabata. Arsenal tana da mai tsaron ragarta Aaron Ramsadale, wanda ya buga mata wasanni 38 na kakar da aka yi ta 2022/23, ya buga wasanni 14 ba tare da an zura masa ƙwallo…
Read More
CAF ta bayyana ranakun gasar AFCON na 2025

CAF ta bayyana ranakun gasar AFCON na 2025

Hukumar Ƙwallon Ƙafar Afrika, CAF, ta ce za a fara gasar kofin nahiyar ta shekarar 2025, wadda za a yi a ƙasar Moroko daga ranar 21 ga watan Disamba zuwa 18 ga watan Janairu.  Shugaban hukumar, Patrick Motsepe ne ya bayyana haka a makon da ya gabata, a yayin taron majalisar zartarwa hukumar, wanda aka yi ta kafar bidiyo, inda ya ce yana da ƙwarin gwiwar gasar za ta kasance mafi armashi. Tun da farko an tsara za a yi wannan gasa daga watan Yuni zuwa Yulin shekarar 2025 ne, amma sai aka canja shawara don gudun kada ta ci…
Read More
Yadda aka ƙarƙare gasar firimiyar Nijeriya na 2023/24

Yadda aka ƙarƙare gasar firimiyar Nijeriya na 2023/24

A ƙarshe dai ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Enugu Rangers ta ɗauki kofin babbar gasar firimiyar Nijeriya a karo na takwas bayan doke Gombe United har gida da ci 2-1. Rangers ta samu jimillar maki 70 a gasar ta Nigeria Professional Footbal League (NPFL) kakar 2023-24, wanda hakan ke nufin ta samu tikitin zuwa gasar zakarun Afirka. An gudanar da bikin ba ta kofin ne a filin wasa na Jos International Stadium - inda Gome United ke buga wasa - bayan wasan mako na 38. Rangers ce ta fara cin ƙwallo minti uku da take wasa ta hannun Ogunleye, sannan Obaje…
Read More
Hada-hadar kasuwar ‘yan wasan ƙwallon ƙafa

Hada-hadar kasuwar ‘yan wasan ƙwallon ƙafa

Manchester United na fatan sake sabon kwantiragi da Erik ten Hag, kafin a fara rangaɗin shirin sabuwar kakar wasa zuwa Amurka, a watan gobe. Tsohon ɗan wasan Manchester United, Ɓan Nistelrooy, mai shekara 47, sun yi tattaunawa mai armashi kan batun komawarsa ƙungiyar a cikin shirin horar da 'yan wasa da Ten Hag ke yi. Ɗan wasan gaba na Sifaniya Joselu, 34, na daf da barin ƙungiyar Real Madrid, bayan da ya samu tayi mai gwabi daga kulub ɗin Al Gharafa, na ƙasar Ƙatar. Chelsea ta fara tattaunawa da Barcelona, kan ɗan wasan gaba na Sifaniya, Marc Guiu, mai shekara…
Read More
Ƙasashen da suka kai matakin ‘yan 16 a gasar kofin Euro 2024

Ƙasashen da suka kai matakin ‘yan 16 a gasar kofin Euro 2024

Tawagogin ƙasashe 6 sun samu gurbin kaiwa matakin 'yan 16 a gasar kofin Turai wato Euro, da ke gudana a ƙasar Jamus. Tawagogin ƙasashen Jamus da Sifaniya da Portugal da Italiya da Birtaniya da kuma Switzerland ne suka samu nasarar tsallakawa zagayen. Italiya dai ta samu gurbin ne bayan da aka tashi kunnen doki 1-1, tsakaninta da Croatia a karawar da suka yi a cikin daren ranar Litinin. A yanzu dai Italiya da ke kare kambin wannan gasa, za ta barje gumi ne da Switzerland don neman gurbi a matakin daf da na kusa da na ƙarshe a gasar. Ita…
Read More
FIFA ta gudanar da bikin tunawa da shigowar Super Eagles Gasar Kofin Duniya

FIFA ta gudanar da bikin tunawa da shigowar Super Eagles Gasar Kofin Duniya

Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Duniya, FIFA, ta gudanar da bikin cika shekaru 30 da fara fitowar tawagar Nijeriya a gasar kofin duniya a shekarar 1994, lokacin da tawagar Super Eagles ta razana takwararsu ta ƙasar bulgaria wacce ake hangowa nasara inda suka fara gasar da ƙafar dama. Tawagar ta Super Eagles ta fara bayyana a gasar  kofin duniya a shekarar 1994, inda ta kara da takwararta ta Bulgaria wacce ke cike da 'yan wasa masu ƙwazo. Duk da cewa an bai wa Nijeriya matsayin da ya ɗara na takwarorinta na Turai, duk da haka ana yi musu kallon raini har…
Read More
Tinubu ya sa zamowar Osimhen Gwarzon Afirka a nasarorinsa na shekara guda

Tinubu ya sa zamowar Osimhen Gwarzon Afirka a nasarorinsa na shekara guda

Daga MAHDI M. MUH'D Tinubu ya saka nasarar da Osimhen ya samu na zama gwarzon ɗan wasan ƙwallon ƙafa na Afirka a cikin nasarorin da ya samu yayin da ya cika shekara guda a kan karagar mulki. Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sanya ɗan wasan gaba na Napoli Victor Osimhen ya zama gwarzon ɗan ƙwallon Afrika na bana a matsayin wani ɓangare na nasarorin da ya samu yayin da ya cika shekara guda a kan karagar mulki. Idan za a iya tunawa, Osimhen ya zama gwarzon ɗan ƙwallon Afrika na 2023 bayan ya doke Mohamed Salah da sauran su, inda…
Read More
Toni Kroos: Ɗan wasan Real Madrid da Jamus zai yi ritaya bayan kammala gasar Euro 2024

Toni Kroos: Ɗan wasan Real Madrid da Jamus zai yi ritaya bayan kammala gasar Euro 2024

Daga MAHDI M. MUH'D Ɗan wasan tsakiya na Real Madrid da Jamus, Toni Kroos zai rajaye takalmansa daga buga wasan ƙwallon ƙafa bayan gasar Euro 2024 da za ta gudana a Jamus ɗin. Ɗan wasan mai shekaru 34, ya yi fice a ƙwallon ƙafa, inda ya lashe kofuna da dama tare da Real Madrid tun bayan da ya koma ƙungiyar daga Bayern Munich a watan Yulin shekarar 2014, inda ya lashe kofin La Liga da na zakarun Turai sau 4 kowanne. Kroos na cikin tawagar ƙwallon ƙafar Jamus da ta lashe gasar kofin duniya a shekarar 2014. A watan Yulin…
Read More
Gwamna Soludo ya sauke shugabannin ƙananan hukumomi

Gwamna Soludo ya sauke shugabannin ƙananan hukumomi

Gwamnan Jihar Anambra, Chukwuma Soludo, ya sauke shugabannin ƙananan hukumomi 21 da jihar ke da su. Haka nan, Gwamnan ya buƙaci saukakkun ciyamomin da su miƙa ragamar aiki ga shugabannin sassan gudanarwa na ƙananan hukumomin. Bayanin haka na ƙunshe ne cikin sanarwa mai ɗauke da da hannun Kwamishinan Kula da Harkokin Ƙananan Hukumomi da Sarautun Gargajiya na Jihar, Collins Nwabunwanne, da kwanan wata 17 ga Mayu. Ya zuwa ranar Litinin, 20 ga Mayu ake sa ran waɗanda lamarin ya shafa su miƙa ragamar aiki ga waɗanda suka dace. A cewar wasiƙar: “Biyo bayan ƙarewar wa'adinka a matsayin shugaban kwamitin miƙa…
Read More