Wasanni

Bellingham ya ci wa Real Madrid ƙwallo ta 19

Bellingham ya ci wa Real Madrid ƙwallo ta 19

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Jude Bellingham ya ci ƙwallonsa na 19 a wasan da Real Madrid ta lallasa Deportivo Alsves da ci 5 da nema a filin wasa na Santiago Bernabeu. Ɗan wasan Ingila ɗin ne ya fara cin ƙwallo a wasan, wanda shine na farko tun da Real Madrid ta lashe kofin gasar La Liga ta Sifaniya. Ƙwallon da Bellingham ya ci dai ta sa yanzu ya bai wa ɗan wasan gaba na Girona Artem Dovbyk tazarar maki guda a tseren da suke na lashe takalmin zinari, na wanda ya fi saka kowallo a raga. Vinicius Jr ne ya…
Read More
Juventus ta lashe kofin Italiya bayan shekara uku

Juventus ta lashe kofin Italiya bayan shekara uku

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Juventus ta lashe kofin Italiya karo na 15, bayan da ta doke Atalanta da ci 1-0 a birnin Rome, a wasan da suka fafata ranar Laraba. Ƙwallon ɗaya tilo da Dusan Vlahovic ya zura a mintina na huɗu da fara wasa ya tabbatar da nasarar Juventus, wanda ta lashe Kofin bayan shafe shekaru uku babu labari. Tawagar Massimiliano Allegri da suka kawo matakin ƙarshe da nasara a wasanni uku kacal, sun nuna turjiya, tare da daƙile yunqurin Atalanta na lashe gasar. Ɗan wasan gaban na Serbia ya sake cin wata amma aka soke ta saboda satar…
Read More
Ƙungiyoyin Firimiya na neman a soke amfani da na’urar VAR

Ƙungiyoyin Firimiya na neman a soke amfani da na’urar VAR

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyoyin gasar Firimiyar Ingila za su kaɗa ƙuri'ar amincewa ko akasin haka kan cigaba da amfani da na'urar VAR mai taimaka wa alƙalin wasa a wata mai zuwa. Kulob ɗin Wolves ya miƙa ƙudiri a hukumance zuwa ga hukumar firimiya, abin da zai sa a kaɗa ƙuri'ar lokacin da mambobin gasar za su gana ranar 6 ga watan Yuni. Ƙungiyar ta ce an ƙaddamar da VAR ɗin ne da "kyakkyawar manufa" amma kuma ta koma jawo abubuwan da ba a nufata ba da ke lalata alaƙar 'yan kallo da wasan ƙwallon ƙafar". An fara amfani da…
Read More
Dortmund ta fitar da PSG daga gasar Zakarun Turai

Dortmund ta fitar da PSG daga gasar Zakarun Turai

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Borussia Dortmund ta kai wasan ƙarshe a gasar Zakarun Turai, bayan da ta yi nasarar cin Paris St Germain 1-0 ranar Talata a Faransa. Ƙungiyoyin sun je hutu babu ci ko ɗaya, bayan da suka koma zagaye na biyu ne Dortmund ta ci ƙwallo ta hannun Mats Hummels. A ranar Talata a makon jiya a wasan farko a daf da ƙarshe a Jamus, Dortmunda ta yi nasara 1-0, kuma Niclas Fullkrug ne ya ci mata ƙwallon tun kan hutu. Kenan Dortmund ta kai wasan ƙarshe a gasar zakarun Turai ta bana da cin ƙwallo 2-0 gida…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Kano Pillars ta dakatar da kocinta Abdu Mai-Kaba

Da Ɗumi-ɗumi: Kano Pillars ta dakatar da kocinta Abdu Mai-Kaba

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Shugaban ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars, Alh. Babangida Little, ya bayyana dakatar da mai horar da 'yan wasan ƙungiyar, Abdu Maikaba, a ranar Talata. Babangida Little ya bayyana dakatarwar da kuma kafa wani kwamiti wanda zai binciki kocin kuma idan aka same shi da laifi, to, zai fuskanci ladaftarwa. Kawo yanzu ba a bayyana ainihin dalilin dakatarwar da aka yi masa ba, sai dai wasu na zargin furucin da Abdu Mai-kaba ya yi a lokacin wani taro da ƙungiyar magoya bayan Kano Pillars suka yi a cibiyar 'yan Jaridu ta jiha ne ya haifar…
Read More
Hada-hadar kasuwar ’yan wasan ƙwallo

Hada-hadar kasuwar ’yan wasan ƙwallo

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ɗan wasan tsakiya na Manchester United da Portugal Bruno Fernandes, mai shekara 29, ya ce makormarsa a Old Trafford ta dogara ne akan ko ƙungiyar ta na son ya cigaba da buga mata wasa har bayan bazara. Newcastle United ba za bada kai ba wajan sayar da dan wasan tsakiya na Brazil Bruno Guimaraes mai shekara 26 kan kuɗi ƙasa da fam miliyan 100 ko rabuwa da ɗan wasa mai kai hari na Sweden Alexander Isak, ɗan shekara 24. Newcastle na son ɗaukar mai tsaron bayan Fulham da Ingila Tosin Adarabioyo mai shekara 26. Adarabioyo, wanda…
Read More
Barcelona ta koma ta biyu a teburin La liga

Barcelona ta koma ta biyu a teburin La liga

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Yayin da ya rage saura wasanni biyar a ƙarƙare La Ligar Sifaniya ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barcelona ta koma matsayi na biyu a teburin gasar da maki 73 bayan da ta tsallake Girona, wacce ke matsayi na uku da 71. Wannan gagarumar nasara da Barcan ta samu na zuwa ne bayan da ta caskala Valencia da ci 4 da 2 a daren ranar Litinin. Kafin tafiya hutun rabin lokaci ƙungiyar Valencia ce ke kan gaba da ƙwallaye 2 da 1. Sai dai bayan dawowa daga hutun rabin lokaci ɗan wasan gaba na Barcelona Robert Lewandowski ya…
Read More
Man United ta fi nuna ƙwarewarta a Firimiya – Ten Hag

Man United ta fi nuna ƙwarewarta a Firimiya – Ten Hag

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Erik ten Hag ya bayyama cewa Manchester United ɗaya ce daga cikin ƙungiyoyin da ta fi nuna bajinta a gasar Firimiya ta bana. Kocin ya faɗi hakan duk da ƙungiyar Old Trafford na fama da kalubalen cin wasa ko dai a gida ko a waje a kakar nan. Ranar Asabar United ta tashi 1-1 da Burnley a firimiya, wadda take ta biyun ƙarshe, inda mai tsaron raga, Andre Onana ya yi kuskuren da aka farke a bugun fenariti ta hannun Zeki Amdouni. Hakan na nufin Ten Hag ya samu nasarar wasa daya a cikin minti 90…
Read More
Gwamnatin Jigawa ta ware N250m don gyara filin wasannin motsa jiki na Dutse – Eka

Gwamnatin Jigawa ta ware N250m don gyara filin wasannin motsa jiki na Dutse – Eka

Daga UMAR AKILU MAJERI a Dutse Gwamnatin Jihar Jigawa ta ware Naira miliyan 250 domin gyaran filin wasnnin motsa jiki na Dutse, hedikwatar jihar Jigawa . Gyaran fulin ya ƙunshi samar da ƙarin gine-gine irin na zamani da wurin dama da fitilu da dasa ciyawa irin ta zamani domin filin ya yi daidai da filin wasa na zamani da ake yayi a duniya. Shugaban ƙungiyar wasan ƙwallon kafa na Jihar Jigawa, Alh Sabo Abdullahi Eka, shi ne ya tabbatar da hakan a lokacin da yake ganawa da manema labarai a filin wasa na Dutse.  Eka  ya ce tuni gwamnatin Jihar…
Read More
Xavi ya yi amai ya lashe kan batun barin Barcelona

Xavi ya yi amai ya lashe kan batun barin Barcelona

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kocin Barcelona, Xavi Hernandez ya sauya shawararsa na barin Barcelona a ƙarshen kakar wasa ta bana kuma zai ci gaba da zama koci bayan tattaunawa da shugaban kulob ɗin, Joan Laporta, da shugabannin ƙungiyar a ranar Laraba. An ruwaito Xavi ya gana da shugaban ƙungiyar, Joan Laporta da daraktan wasanni, Deco, a daren Laraba. Bayan taron ya sauya ra'ayi kuma ya amince da sharuɗɗan ci gaba da jagorantar ƙungiyar ta LaLiga. Ƙwararre a harkar wasan ƙwallon aafa Fabrizio Romano ya bayyana hakan a shafinsa na X. Romano ya rubuta: Xavi ya yanke shawarar canja ra'ayinsa ya…
Read More