Wasanni

Aubameyang ya buƙaci ninkin albashin Ibrahimovic a AC Milan

Aubameyang ya buƙaci ninkin albashin Ibrahimovic a AC Milan

Ɗan wasan gaba na Arsenal, Pierre-Emerick Aubameyang, yana neman sau biyu abin da Zlatan Ibrahimovic yake samu a AC Milan don komawa qungiyar ta qasar Italiya. AC Milan ita ce kulob na baya-bayan nan da ake alaƙanta ta da ɗan wasan mai shekaru 32, wanda a yanzu ba a san makomar shi ba a Emirates. Tun a ranar 6 ga watan Disamba, Aubameyang bai taka leda a Gunners ba, lokacin da Arsenal ta sha kashi da ci 2-1 a Goodison Park. An cire ɗan wasan na Gabon ne daga muƙamin kyaftin ɗin ƙungiyar bayan mako guda bayan wani sabon ladabtarwa…
Read More
Joshua ya musanta karɓar cin hanci don fasa karawa da Usyk

Joshua ya musanta karɓar cin hanci don fasa karawa da Usyk

Fitaccen ɗan damben ‘boxing’ ajin masu nauyi, Anthony Joshua ɗan Ingila, ya yi watsi da rahotannin cewa ya amince da yarjejeniyar karɓar kuɗi fam miliyan 15 kwatankwacin Yuro miliyan 18 don janyewa daga shirin sake karawa da Oleksandr Usyk na ƙasar Ukraine. A watan Satumban shekarar bara ne dai Usyk ya kwace dukkanin kambun Joshua na WBA da IBF da kuma WBO, bayan lallasa Joshua ɗin da yayi a fafatawar da suka yi. Rashin nasarar da Joshua ya yi a karon battarsa da Oleksandr Usyk, ita ce karo na biyu da fitaccen dan damben boxing ɗin ya fuskanta tun bayan…
Read More
Everton ta kori Rafael Benitez kwanaki 200 bayan ba shi aikin horarwa

Everton ta kori Rafael Benitez kwanaki 200 bayan ba shi aikin horarwa

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Everton ta kori Manajanta Rafael Benitez kwanaki 200 cif bayan ba shi aikin horarwa daidai lokacin da ƙungiyar ke ci gaba da fuskantar tarin rashin nasara a wasanninta na Firimiya. Benitez wanda ya yi aiki tsawon lokaci da Liverpool da ke matsayin babbar abokiyar dabin Everton ya karɓi ragamar ƙungiyar ne a watan Yunin 2021. Sanarwar da ƙungiyar ta wallafa a shafinta ta tabbatar da raba gari da kocin nata bayan shan kaye a wasanni 9 cikin wasanni 13 da ƙungiyar ta doka a baya-bayan nan ƙarƙashin gasar firimiyar Ingila. Rashin nasara ta baya-bayan nan da…
Read More
Shugaba Buhari ya aika da saƙo ga kocin Super Eagles

Shugaba Buhari ya aika da saƙo ga kocin Super Eagles

Daga WAKILINMU Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya buƙaci kocin Super Eagles, Austin Eguavoen da ya ci gaba da kuma zarce yadda ya kai ga nasara a gasar cin kofin Afrika (AFCON) da ake yi a Kamaru. A cikin wata sanarwa da ya fitar a daren Larabar da ta gabata ta hannun mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai Femi Adesina, Buhari ya bayyana cewa ƙasar na fatan samun nasara guda bakwai a gasar. Shugaba Buhari ya yaba wa ƙungiyar bisa ƙoƙarinta na lashe dukkan wasanninta na rukuni wanda ya sa ta tsallake zuwa zagaye na biyu a…
Read More
Messi na iya girgiza magoya bayan Barcelona a dalilin iyalansa

Messi na iya girgiza magoya bayan Barcelona a dalilin iyalansa

Ɗan wasa Lionel Messi zai iya dawowa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barcelona sakamakon iyalansa basajin daɗin zama a babban birnin France Paris. Iyalan ɗan wasan gaban ƙasar Argentina da Paris saint-german Lionel Messi sun bayyana masa ƙarara cewar ba su jin daɗin zama a babban birnin ƙasar Faransa wato Paris. Iyalan na Lionel Messi sun fi jin daɗin zama a birnin Barca da ke ƙasar Sifaniya kafin subar ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barcelona. A bayyane yake cewar Lionel Messi zai iya komai domin iyalansa kuma wannan dama ce da Barcelona za ta yi yunƙurin dawo da shi filin wasa na…
Read More
AFCON: Buhari ya taya ‘yan wasan Super Eagles murna

AFCON: Buhari ya taya ‘yan wasan Super Eagles murna

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, ya bayyana jin daɗinsa tare yaba wa 'yan wasan Super Eagles dangane da nasarorin da suka samu a duka wasanni ukun da suka buga a gasar cin kofin Afirka (AFCON) da ke gudana a ƙasar Kamaru. Buhari ya nuna jin daɗinsa ne a saƙon da ya wallafa a shafinsa na facebook a ranar Laraba. Buhari ya buƙaci 'yan wasan da su ci gaba da tabbata a kan wannan hanya ta nasara da suka ɗauka har zuwa ƙarshen gasar tare kuma da zama jakadu nagari ga Nijeriya a cikin filin wasa da kuma wajen…
Read More
Ɗan wasan Madrid, Isco, na shirin ƙulla yarjejeniya da Barcelona

Ɗan wasan Madrid, Isco, na shirin ƙulla yarjejeniya da Barcelona

A karon farko cikin kusan shekaru 15, ana shirin samun sauyin sheƙar ɗan wasa kai tsaye tsakanin manyan abokan hamayya a gasar La Liga, wato Real Madrid da Barcelona FC. Rabon da a ga irin wannan sauyin sheƙa dai tun shekara ta 2007, lokacin da Javier Saviola ya koma Real Madrid daga Barcelona. A halin yanzu kuma ɗan wasan tsakiyar Real Madrid, Isco Alcaron, ke shirin sauyin shekar zuwa Camp Nou. Tuni dai aka tsegunta cewar har ma Isco ya gana da kocin Barcelona Xavi Hernandez. Ɗan wasan mai shekaru 29 a yanzu shi ne na 5 a matakin muhimmanci…
Read More
Yadda Nijeriya ta lallasa Masar a gasar AFCON

Yadda Nijeriya ta lallasa Masar a gasar AFCON

Daga WAKILINMU Kelechi Iheanacho na Super Eagles ya cirewa Nijeriya kitse a wuta a karawarta da Masar ranar talata bayan ƙwallonsa da ta bai wa ƙasar ta yammacin Afrika nasara a wasanta na farko ƙarƙashin gasar cin kofin Afrika. Shahararren ɗan wasan gaba na Liverpool Salah bai taɓuka abin kirki ba, sakamakon yadda zaratan ’yan wasan Nijeriya suka riƙe shi tsawon mintuna 90 da aka yi a wasan. Babban wasa na biyu da kowa ke jiran gani a gasar cin kofin Afrika na shekarar 2021 tsakanin Nijeriya da Misra, ya zo ƙarshen inda Nijeriya ta yiwa Misra da shahararren ɗan…
Read More
Korona: Kashi 60 za a bari su shiga kallon gasar Kofin Afrika

Korona: Kashi 60 za a bari su shiga kallon gasar Kofin Afrika

Daga WAKILINMU A tsakanin watannin Yuni da Yulin bara ya kamata a yi gasar, amma annobar Korona ta sa aka ɗage zuwa bana. Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta nahiyar Afirka CAF ta ce kashi 60 zuwa 80 na ’yan kallo za a bari su shiga filayen wasanni da za a kara gasar cin kofin nahiyar na AFCON. Matakin a cewar hukumar na da nasaba da annobar COVID-19. Cikin wata sanarwa da ta fitar, CAF ta ce bayan wata tattaunawa da ta yi da hukumomin cikin gida na Kamaru, sun cimma matsaya akan cewa kowanne filin wasa za a bar ‘yan kallo…
Read More
Hana Ighalo wakiltar Nijeriya: Eguavoen ya mayar da martani ga Al-Shabab

Hana Ighalo wakiltar Nijeriya: Eguavoen ya mayar da martani ga Al-Shabab

Daga WAKILINMU Kocin riƙon ƙwarya na Super Eagles, Augustine Eguavoen, ya ce, yana da ƙwarin gwiwar cewa Odion Ighalo zai haɗa kai da sauran ‘yan wasan da za su buga gasar kofin Afrika ta 2021. Ƙungiyar Al Shabab ta Ighalo ta ƙi sakinsa a domin fafata gasar. Wannan ya sa tsohon ɗan wasan Manchester United da Watford ya shiga tsakanin kulob da ƙasar. An ruwaito Ighalo yana Nijeriya kuma yana da wa’adin tabbatar da kasancewarsa. “Da fatan Odion ya zo,” inji Eguavoen a wani taron manema labarai a ranar Talatar da ta gabata. Ana kyautata zaton cewa gogaggen ɗan wasan…
Read More