Wasanni

Gwamna Sule ya zira ƙwallo a raga a wasan bikin cikar Nasarawa shekara 25 da kafuwa

Gwamna Sule ya zira ƙwallo a raga a wasan bikin cikar Nasarawa shekara 25 da kafuwa

Daga BASHIR ISAH A matsayin wani ɓangare na cikar Jihar Nasarawa shekara 25 da kafuwa, gwamnatin jihar ƙarƙashin jagorancin Injiniya Abdullahi Sule, ta shirya wasan ƙwallon ƙafa na sada zumunta inda aka fafata tsakanin ɓangaren Gwamna Sule da ya ƙunshi tsoffin masu buga wa jihar wasa, da kuma ɓangaren tsoffin 'yan wasan ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta ƙsa, wato Super Eagles. Sanarwar da ta fito ta hannun jami'in yaɗa labarai na ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Nasarawa United, Eche Amos, ta nuna an buga wannan wasa ne a ranar Alhamis da ta gabata a babban filin wasannin motsa jiki da ke Lafia…
Read More
Gerd Muller ya kwanta dama

Gerd Muller ya kwanta dama

Tsohon zakaran ƙwallon ƙafar ƙasar Jus, Gerd Muller, ya rasu. Muller ya bar duniya yana da sheka 75. Bayanai sun nuna a halin rayuwarsa, Muller ya kasance ɗan wasan da ya fi kowa zira ƙwallaye a Bayern Munich inda ya ci ƙwallaye guda 563 a wasanni 605 na Bundesliga, Tun a 2015 aka gano marigayin na ɗauke da cutar Alzheimer, lokacin da yake kocin ƙungiya ta biyu ta Bayern. A wani sako da ta wallafa a shafinta ma Tiwita, ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Bayern Munich ta ce, "Yau duniyar FC Bayern ta tsaya cak. Gwarzon ɗan wasan Jamus da dukkan…
Read More
PSG ta yi babban kamu

PSG ta yi babban kamu

A halin da ake ciki, ya tabbata cewa fitaccen ɗan wasan ƙwallon ƙafa, Lionel Messi, ya zama ɗan ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta PSG. Ƙungiyar PSG ta sanar cewar Lionel Messi ya sanya hannu a kwangilar shekaru biyu bayan barin sa ƙungiyar Barcelona inda ya shafe shekara 21 yana buga mata wasa. Sanarwar PSG ta nuna kwangilar ta kuma ƙunshi buƙatar ƙarin shekara guda bayan kammala shekaru biyun da aka cim ma yarjejeniya idan hali ya yi. Haka nan, cewa Messi zai sanya riga mai ɗauke da lamba 30, lambar da ya yi amfani da ita lokacin da ya fara yi…
Read More
Messi ya yi hawaye saboda alhinin ficewa daga Barcelona

Messi ya yi hawaye saboda alhinin ficewa daga Barcelona

Shahararren ɗan wasan ƙwallon ƙafar nan, Lionel Messi, ya yi hawayi a baina jama'a saboda alhinin barin ƙungiyar ƙwallon ƙafar da ya shafe shekaru yana buga mata wasa, wato Barcelona. Messi ya zubar da hawaye ne a lokacin da yake ƙoƙarin yi wa taron manema labarai bayani dangane da ficewarsa daga kulob ɗin Barcelona a Camp Nou. A ranar Alhamis da ta gabata Barcelona ta tabbatar wa duniya cewa zakaran ƙwallon ƙafar, ɗan shekara 34 da haihuwa, ba zai sabunta kwantiraginsa da ƙungiyar ba saboda matsalar kuɗi da kuma shirin sake wa ƙungiyar fasali. Messi ya shaida wa manema labarai…
Read More
An shirya wasan sada zumunta na Badminton a Damaturu

An shirya wasan sada zumunta na Badminton a Damaturu

Daga MUHAMMAD AL-AMEEN a Damaturu Sakamakon ci gaba da samun zaman lafiya a Arewa-maso-gabas tare da ma jihar Yobe baki ɗaya, 'yan ƙungiyar wasan Badminton Damaturu sun shirya wasan sada zumunta a Damaturu, babban birnin jihar Yobe. Da yake jawabi wajen buɗe wasan a ranar Asabar, shugaban kwamitin shirya wasan, Alhaji Bashir Baba Geidam, ya bayyana cewa sun shirya wasan ne domin sada zumunta a birnin Damaturu. Haka kuma, ya ce wannan wasa an saba gudanar da shi ta haɗin gwiwa tsakanin manyan ɓangarorin badminton da ke jihar Yobe, waɗanda suka ƙunshi na Gashuwa, Postiskum da Damaturu a jihar. Bugu…
Read More
Brisbane ta samu gurbin ɗaukar nauyin Wasannin Olympic na 2032

Brisbane ta samu gurbin ɗaukar nauyin Wasannin Olympic na 2032

Daga UMAR M. GOMBE Kwamitin Shirya Wasannin Olympic na Ƙasa da Ƙasa ya bayyana birnin Brisbane na ƙasar Australia a matsayin birnin da zai ɗauki nauyin gudanar da Wasannin Olympic na 2032. Da wannan sasarar da Brisbane ya samu, ya sanya Australia ta zama ƙasa ta biyu a duniya bayan ƙasar Amurka da suka samu damar ɗaukar nauyin gudanar da Wasannin Olympic fiye da sau biyu a birane daban-daban. Da farko, Australia ta soma ɗaukar nauyin Olympic ne a Melbourne a 1956, sannan Sydney a 2000, sai kuma na ukun kenan ake sa ran gudanarwa a Brisbane ya zuwa 2032.…
Read More
Kaftin ɗin Super Eagles ya ƙara aure

Kaftin ɗin Super Eagles ya ƙara aure

Daga IBRAHIM HAMISU, a Kano Fitaccen ɗan wasan ƙwallon ƙafa kuma Kaftin na ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta ƙasa Super Eagles, Ahmed Musa, ya ƙara aure. Musa mai shekaru 29, wannan shi ne aurensa na uku, tun bayan da ya rabu da matarsa ta farko Jamila a 2017 wanda nan take ya maye gurbinta da Juliet kuma suke tare har yanzu. A halin da ake ciki dai yanzu sabuwar amaryar tasa mai suna Maryam ita ce matarsa ta biyu. Jarumi a masana’antar Kannywood, Ali Nuhu, shi ne ya wallafa bayani da hotunan auren a shafinsa na Instagram inda ya taya Ahmad…
Read More
Kyawun alƙawari: Buhari ya yi wa Tawagar Super Eagles a gasar Tunisiya 1994 kyautar gidaje

Kyawun alƙawari: Buhari ya yi wa Tawagar Super Eagles a gasar Tunisiya 1994 kyautar gidaje

Daga UMAR M. GOMBE Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya amince a ba da kyautar gida mai ciki uku-uku ga kowane ɗan wasan Super Eagle na tawagar da ta ciyo wa Nijeriya Kofin Afirka a gasar da aka gudanar a ƙasar Tunisiya a 1994. Wannan kyauta na mazaunin cika alƙawarin da Gwamnatin Tarayya ta yi wa 'yan wasan ne a wancan lokaci sakamakon nasarar lashe gasar da suka samu. Mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Malam Garba Shehu ne ya bayyana haka cikin wata sanarwar da ya fitar a ranar Alhamis. Sanarwar ta nuna gwamnati ta cika wannan alƙawari ne bayan da…
Read More