01
Oct
Daga BASHIR ISAH A matsayin wani ɓangare na cikar Jihar Nasarawa shekara 25 da kafuwa, gwamnatin jihar ƙarƙashin jagorancin Injiniya Abdullahi Sule, ta shirya wasan ƙwallon ƙafa na sada zumunta inda aka fafata tsakanin ɓangaren Gwamna Sule da ya ƙunshi tsoffin masu buga wa jihar wasa, da kuma ɓangaren tsoffin 'yan wasan ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta ƙsa, wato Super Eagles. Sanarwar da ta fito ta hannun jami'in yaɗa labarai na ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Nasarawa United, Eche Amos, ta nuna an buga wannan wasa ne a ranar Alhamis da ta gabata a babban filin wasannin motsa jiki da ke Lafia…