Wasanni

Doke Real Madrid sau biyu a jere ba abu ne mai yiwuwa ba, inji Guardiola gabanin karawar UCL

Doke Real Madrid sau biyu a jere ba abu ne mai yiwuwa ba, inji Guardiola gabanin karawar UCL

Daga MAHDI M. MUH'D Kocin Manchester City, Pep Guardiola ya bayyana cewa ƙungiyarsa na fuskantar babban ƙalubale idan suka kara da Real Madrid a gasar La Liga. Idan dai ba a manta ba, Man City ta fitar da 'yan wasan Carlo Ancelotti a kakar wasan da ta gabata a cikin salo mai ban sha'awa (ci 5-1) a hanyarsu ta ɗaukar kofin zakarun Turai na UEFA a karon farko a tarihinsu. Pep Guardiola ya tattaro haziƙan ’yan wasansa wajen ganin sun lallasa Real Madrid da ci 4-0 a wasan daf da na kusa da ƙarshe a filin wasa na Etihad bayan…
Read More
PSG ta kai wasan ƙarshe a gasar kofin Faransa

PSG ta kai wasan ƙarshe a gasar kofin Faransa

Daga MAHDI M. MUH'D Ƙungiyar ƙwallon koafa ta PSG ta samu kaiwa wasan ƙarshe na kofin Faransa wato French Cup bayan ƙwallon ɗaya tilo da Kylian Mbappe ya zura a ragar Rennes daren ranar Laraba a wasan daf da na ƙarshe da suka doka tsakaninsu. A minti na 40 daf da tafiya hutun rabin lokaci ne Mbappe ya zura ƙwallon bayan tun farko mai tsaron ragar Rennes Steve Mandanda ya varar da fenaritin da tauraron na Faransa ya buga a minti na 33. Mbappe wanda ke matsayin mafi zurawa PSG ƙwallo na taka leda ne a kakarsa ta ƙarshe a…
Read More
Super Eagles ta taki sabon matsayi a jadawalin FIFA

Super Eagles ta taki sabon matsayi a jadawalin FIFA

Daga MAHDI M. MUH'D A yanzu haka tawagar Super Eagles ta Nijeriya ta taki matsayi na 33 inda ta sha gaban abokiyar hamayyarta ta yammacin Afirka a sabon jadawalin FIFA bayan da ta doke ta da ci 2-1 a wasan sada zumunta da suka yi a watan jiya. Duk da cewa sau biyu tawagar Super Eagles ta Nijeriya tana faɗuwa ƙasa a sabuwar kimar hukumar ta FIFA, amma har yanzu zakarun Afirkan na gaban Ghana da ke yammacin Afirka. Super Eagles dai ta kasance ta 28 a duniya a jadawalin watan Fabrairu amma ta koma mataki na 30 a kimar…
Read More
Diawara ya soke kwataraginsa da Faransa bayan haramta wa ’yan wasa yin azumi

Diawara ya soke kwataraginsa da Faransa bayan haramta wa ’yan wasa yin azumi

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Ƙwallon Ƙafar Ƙasar Faransa ta gayyaci Dehmaine Tabibou Assoumani na ƙungiyar Nantes a matsayin wanda zai maye gurbin ɗan wasan tsakiyar tawagar ’yan ƙasa da shekara 19 ta ƙasar. Ɗan wasan tsakiyar Mahamadou Diawara ya yanke shawarar barin tawagar ne bayan da hukumar ƙawallon ƙafa ta ƙasar ta kafa wasu sabbin dokoki waɗanda suka haramtawa 'yan wasa Musulmi yin azumin watan Ramadan a lokacin da suke atisaye. Diawara bai ji dadin sabbin dokokin ba, waɗanda aka fara aiwatar da su tun daga matakin tawagar ’yan qasa da shekaru 16 har zuwa babbar tawagar ƙasar. Wannan…
Read More
Zan bayyana makomata bayan gasar kofin Turai – Mbappe

Zan bayyana makomata bayan gasar kofin Turai – Mbappe

Sga MAHDI M. MUHAMMAD Ɗan wasan gaba na PSG Kylian Mbappe ya ce zai bayyana matsayarsa na gaba bayan gasar kofin nahiyar Turai ta 2024. Ɗan wasan na Faransa ya yi magana a karon farko game da raɗe-raɗin da ake yi na yarjejeniyarsa da Real Madrid a bazara. A yayin da yake magana a gidan jaridar Faransa, ya ce “Ban sanar da komai ba saboda babu abin da zan sanar. "Zan bayyana makomata kafin gasar kofin Turai." Dangane da gasar Olympics ta Paris, Mbappe ya ce: “A koyaushe ina da wannan buri, abu ne na musamman kuma a koyaushe ina…
Read More
Amusan ta lashe tambarin zinare a gasar tseren Afrika

Amusan ta lashe tambarin zinare a gasar tseren Afrika

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Sarauniyar wasannin guje-guje ta Nijeriya, Tobi Amusan, ta cika burin magoya bayanta bayan da ta lashe tambarin zinare a tseren gudu na mita 100 a gasar kofin Afrika da ke ci gaba da gudana a ƙasar Ghana. Amusan, wadda ita ce ke riƙe da kambun tseren mita 100 na duniya, ta kasance wadda aka fi so a gasar, an nuna mata ƙauna bayan ya doke sauran abokan hamayyarta a karo na farko a tsaren. A karo na biyu bayan an harba bindigar farawa, Amusan ba ta tsaya sanya ba, inda ta yi nasara a cikin sauƙi…
Read More
Gasar Zakarun Turai: Arsenal da Barcelona sun kai zagayen kusa da ƙarshe

Gasar Zakarun Turai: Arsenal da Barcelona sun kai zagayen kusa da ƙarshe

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Arsenal ta kai zagayen daf da na kusa da na ƙarshe, bayan da ta yi nasara a kan FC Porto da cin 4-2 a bugun fenariti ranar Talata a Emirates. Tun farko Arsenal ce ta ci 1-0 ta hannun Leandro Trossard saura minti hutu su je hutu, irin wannan sakamakon Porto ta samu a Portugal a wasan farko. Hakan ne ya sa aka yi ƙarin lokaci daga nan aka je bugun daga kai sai mai tsaron raga. Gunners ta ci ƙwallaye a bugun fenariri ta hannun Odegaard da Kai Havertz da Bukayo Saka da kuma Declan…
Read More
An dakatar da ’yan wasan Kamaru 62 saboda zaftare shekaru

An dakatar da ’yan wasan Kamaru 62 saboda zaftare shekaru

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Ƙwallon Ƙafar Kamaru ta dakatar da 'yan wasan ƙasar 62 bisa laifin coge wajen bayyana shekaru, cikinsu har da matashi mafi ƙarancin shekaru a tawagar da ta buga gasar kofin nahiyar Afirka da aka yi a watan Janairu. Hukumar ta FECAFOOT ta fitar da jerin sunayen a hukumance a ƙarshen wannan makon, ciki harda Wilfried Nathan Douala mai shekaru 17 wanda ya ba da mamaki cikin tawagar Rigobert Song a gasar da aka kammala a Ivory Coast. A cewar FECAFOOT, mai tsaron ragar Victoria United ya yi ƙarya game da shekarunsa, don haka an hana…
Read More
La Liga za ta binciki batun cin zarafin Vinicius

La Liga za ta binciki batun cin zarafin Vinicius

Daga MAHDI M. MUHAMMAD La Liga na nazarin wani bidiyo da ake zargin yana nuna wariyar launin fata ga Vinicius Jr a wasan da Real Madrid ta buga da Valencia a ƙarshen makon da ya gabata. Bidiyon da aka wallafa a shafukan sada zumunta na Intanet ya nuna yadda wani yaro mai goyon bayan Valencia ke jagorantar cin zarafin ɗan wasan. Vinicius ya zura ƙwallaye biyu a wasan da suka tashi 2-2 a ranar Asabar kuma ya yi murna ta hanyar ɗaga hannunsa sama. Ɗan wasan mai shekaru 23 ya fuskanci cin zarafi na wariyar launin fata sau da dama…
Read More
Ahmed Musa ya dakatar da kwantiraginsa da Sivasspor ta Turkiyya

Ahmed Musa ya dakatar da kwantiraginsa da Sivasspor ta Turkiyya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Rahotanni sun bayyana cewa kyaftin ɗin Super Eagles, Ahmed Musa ya soke kwantiraginsa da ƙungiyar Sivasspor ta Turkiyya. An kawo ƙarshen kwantiragin tsakanin Musa da Sivasspor ta hanyar yarjejeniya. Ɗan wasan mai shekaru 31 ya ɗauki matakin ne bayan ƙungiyar ta kasa biyan albashin sa na watanni shida da suka gabata. Ɗan wasan gaba ya riga ya fara aiki don komawa wani kulob a lokacin bazara. Musa ya koma Sivasspor daga wata ƙungiyar Turkiyya Fatih Karagumruk a shekarar 2022. Ya buga wasanni tara a ƙungiyar ba tare da samun nasarar zura ƙwallo ko ɗaya a raga…
Read More